💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎
*FAMILY DOCTOR'S*
🩺
💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱
*NAFEESAT RETURN*
🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱*MALLAKAR:*
_NAFISAT ISMA'IL LAWAL_*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
*FEENAH WRITER'S ASSO*📖
'''®Ɗaya tamkar da Dubu'''💪✓*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattapad: UmmuDahirah*👈
*\F.W.A📚/*
*SADAUKARWA*
_Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. *GOMA'S FAMILY*_.
*EPISODE Thirty Five*
Usman be dawo gidan ba sai dare, yana shigowa parlor ya tarar da Hajiya na zaune tana tsimayen shigowar sa, domin kuwa a lokacin wajen ƙarfe 12:00pm ne na dare
Yana shigowa tayi zumbur ɗin zuwa wajen sa, cikin tashin hankali tace, "Ina ka je ne tun ɗazu ina buga wayan ka ban samu ba?"
Kallon ta kawai yake yi amma be ce komi ba, gaba ɗaya ransa a ɓace yake har yanzu, zuciyar sa gaba ɗaya ba ta masa daɗi, shiyasa ma ko kaɗan bazai iya buɗe bakin sa ba, bare yayi magana
Zata sake yin magana, sai suka ji muryan Big Dady yana cewa, "Ka dawo?"
Gaba ɗaya kallon sa suke yi kamar yanda ya kafe su da ido, yana tsaye a bakin ƙofar ɗakin sa
Shiru Usman yayi yana me kawar da kai daga kallon sa
"Dama kai nake jira, daga ke har shi a gidan nan zan yi mummunan saɓa muku, muddin kuka ce za ku ja da maganar auren nan, duk abinda kike faɗa min a kan a janye auren nan, to wlh muddin ina numfashi sai an yi sa, sakaran banza sakaran hofi, kuma wlh idan har baka dena nuna wa Daughter irin tsanar nan ba, Ni da kai ne a gidan nan, zan ga uban da tayi maka ka tsane ta". Yana ƙare maganar ya juya ya shige ɗakin sa
Usman be bari ya ƙara Socond ɗaya ba shima ya wuce ɗakin sa da sassarfa, yana jin Hajiya na kiran sa amma ina sam ya ƙi waigo wa
Itama cikin ɓacin rai ta nufi ɗakin Dadyn, tana shiga ta tarar da shi zaune gefen gado yana shirin kwanciya, ta ƙarisa wajen sa tana cewa, "wai me kake nufi da zaka saɓa mana a kan maganar nan? Ina ce yaron nan ba ya ƙaunar yarinyan? Kowa yasan da cewa jinin su be haɗu ba a gidan nan, kuma kafi kowa sani, amma sabida tada zaune tsaye ake son tauye wa ɗana haƙƙin sa, Ni fa bazan goyi bayan gaskiya ko ƙarya ba, Ni ɗana kawai na sani, abinda yake so shi nake so, tunda ya nuna ba ya son haɗin nan, kun hana sa ya faɗi ra'ayin sa, amma ai fuskar sa ta nuna muku ba ya so, to wlh bazai yiwu ba, a kan ɗana babu abinda bazan yi ba".
"Wato kina so ki nuna min wuyan ki ya isa yanka Asiya? Har Ni kike tsayawa a gaba na a kan wannan maganar kike son gaya min magana ko? To kar ki fasa, ki je kiyi duk abinda za ki yi, amma aure ne babu fashi, tunda kuka nuna ba ku son auren nan, to yanzu ne na ɗau ɗammaran sai ya aure ta, wlh bari kiji ko bayan raina bazan taɓa yafe wa ba muddin Usman be auri Ɗahira ba, idan kin ga ba'a yi ba kuwa, to ɗayan biyu ne, ko Allah ne be yi nufin matar sa ba ce, ko kuma Baba ne ya hana, shi ne kawai zan iya bin umarnin sa a duniyar nan, kuma ki ɓace ki bani wuri kar ki sake tanka wa tun kafin raina ya ɓaci".
Dole Hajiya ba don ta so ba ta juya ta wuce ɗakin ta, amma a ranta ta ɗau alwashin muddin ɗanta ba ya son auren nan, to itama baza ta taɓa son Ɗahira ba, sai ta muzguna wa rayuwan ta.
⚫⚫⚫
A wannan dare a cikin Usman da Ɗahira babu wanda yayi barcin farin ciki, zan iya cewa gaba ɗayan su a zaune suka kwana.
![](https://img.wattpad.com/cover/262673222-288-k158926.jpg)
YOU ARE READING
DOCTOR'S FAMILY
FantasyFamily ne me cike da abun mamaki, gaba ɗayan su sun kasance DOCTORS ne, Rayuwar Ɗahira da Usman waɗanda suka kasance cikin Familyn, sun kasance maƙiyan juna, inda ƙaddara ta zo ta haɗa su aure, suna zama ne tamkar za su kashe juna don ƙiyayya, ya ts...