Episode Thirty Two

122 8 1
                                    

💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎
*FAMILY DOCTOR'S*
🩺
💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎

🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱
*NAFEESAT RETURN*
🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱

*MALLAKAR:*
_NAFISAT ISMA'IL LAWAL_

*بسم الله الرحمن الرحيم*


*FEENAH WRITER'S ASSO*📖
'''®Ɗaya tamkar da Dubu'''💪✓

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattapad: UmmuDahirah*👈

\𝗙.𝗪.𝗔📚/

*SADAUKARWA*
_Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. *GOMA'S FAMILY*_

*HADHISI*
_An karbo dga Aisha Allah ya ƙara yarda agareta tace " Manzon Allah s.a.w ya aureta tana da shekara shidda,kuma yatare da ita tana da shekara Tara,kuma Allah ya karbi ransa tana er shekara sha takwas. Muslim ya ruwaito_

.

*EPISODE Thirty Two*

Ɗago kanta tayi tana kallon sa, sai tayi saurin ƙirƙirar murmushi tace, "No, I'm not crying, abu ne ya faɗa min a ido shiyasa".

Duk da be yarda ba, sai yace, "Eyya sorry! Amma dai ba tafiya zaki yi ba?"

"I'm going Yaya Sulaiman, har da gidan Shakira zan je, and Mama says" I'll be back soon ".

"To babu damuwa, ki gaida mutanen gidan don Allah".

"Insha Allah, they will".

Hannu yasa cikin aljihu ya fito da kuɗi yana faɗin, "amma shi ne Yusran bata zo ta taka miki ba?"

Bata ce mishi komi ba, tunda bata san me zata ce mishi ba

Sai ya miƙa mata kuɗin har 20k Yana faɗin, "ga shi babu yawa kiyi haƙuri".

Girgiza kanta tayi tace, "a'a wlh bazan amsa ba, ka bar shi Yaya Sulaiman". Tana faɗan hakan ta wuce sa ta bar wurin

Da kallo ya bi ta da shi har ta kai wajen motan ta, kafin yaja numfashi yana mayar da kuɗin cikin aljihun sa, ƙofan ya buɗe ya shiga ciki da sallama

Yusra dake zaune har yanzu a inda take, tana faman karkaɗa ƙafafu tana latsa waya, ɗago wa tayi tana amsa sallaman nasa idanun ta a kansa

Shi kuwa a kan Centre table ɗin ya sauke idanun sa, zuciyar sa sosai take ɗarsa masa tabbas Yusra ce tayi wa Ɗahira wani abun, domin ya san cewa Yusra ba ta shiri da ita, tunda sau nawa take faɗar magana a kanta, kuma sannan ba ta son ko kaɗan yayi maganar ta a waje, idan yayi kuma ta dinga kushe ta kenan

Kallon ta yayi yace, "meyasaka Ɗahira ta tafi tun yanzu?"

Taɓe baki tayi tace, "can ta matse mata nima ban sani ba".

Waro ido yayi kanta yana sake gasgata abinda ke ransa, sai kuma ya juya yana kwaɗa wa me aikin nasu kira. Tana fitowa ya tambaye ta "ina abincin nan da na ga Ɗahira tana ci? Yanzun nan daga fitan ta har kin kawar da Plate ɗin?"

Jiki na rawa matar tace, "wlh ranka ya daɗe! Uwar ɗaki na ce ta sanya Ni na ɗauka na mayar tunda abincin ka ne".

"Kina nufin tana zaune a nan ta saka ki kika ɗauke?"

Jiki a sanyaye ta duƙar da kanta ƙasa saboda uwar hararan da Yusra ta banka mata, ta amsa mishi da "eh. Amma a gafarce Ni yallaɓoi, ba laifi na ba.."

"Je ki abun ki Baaba".

Da sauri ta wuce ta koma kichen

Sai ya mayar da idanun sa kan Yusra dake ci gaba da karkaɗa ƙafafun ta, tamkar ma bata damu da abinda yake tambaya a kai ba, yace da ita, "Yusra wai Ni shin in tambaye ki? Ɗahira ba ƴar uwan ki bace?"

DOCTOR'S FAMILYWhere stories live. Discover now