Episode Forty Six

131 10 3
                                    

💎💎💎💎💎💎💎💎💎
*FAMILY DOCTOR'S*
🩺
💎💎💎💎💎💎💎💎💎

🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱
*NAFEESAT RETURN*
🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱

*MALLAKAR:*
_NAFISAT ISMA'IL LAWAL_

*بسم الله الرحمن الرحيم*


*FEENAH WRITER'S ASSO*📖
'''®Ɗaya tamkar da Dubu'''💪✓

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattapad: UmmuDahirah*👈

*\F.W.A📚/*

*SADAUKARWA*
_Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. *GOMA'S FAMILY*_

.

*EPISODE Forty Six*

"Wlh idan baki rufe min baki ba sai nayi ƙasa-ƙasa dake a nan, bar ganin kina kwance a nan sai na ɓalla miki ƙasusuwa, mahaifin ki zai yi magana da ke, idan kika sake kika yi wani motsin da zai sa ya gane wani abu.. uhm wlh I will teach you a lesson".

Cak ta tsayar da kukan nata jin ya kirayi mahaifin ta, da sauri jikin ta na rawa ta kai hannu ta amshi wayan da yake miƙo mata, muryan mahaifin ta taji ya doki kunnen ta, sai ta lumshe idanu tana me tsiyayar da hawaye, cike da sanyin murya take gaishe sa zuciyar ta cinkushe da kewar sa

Nan ya tambaye ta jikin nata?

Ta amsa mishi tana faɗin, "taji sauƙi sosai". Kana ta soma jero masa tambayan "ina su Maman ta da su Umma? Har Fadil sai da ta tambaya"

Abbu yace mata, "babu su Fadil kusa, amma ga Maman ta su gaisa".

Jin muryan Maman ta sai ta fashe da kuka tana me kiran sunan ta

Daga can Aunty Amarya tace, "har yanzu dai kin kasa girma ko? Kukan na mene ne?"

"Nayi kewar ku ne sosai Mama, don Allah ki saka baki ya dawo dani".

Aunty Amarya ta gane wa take nufi, sai tace mata, "ke baki da baki ne? Duka-duka yaushe kuka tafi? Idan kin yi haƙuri nan ba da jima wa ba kamar yau ne za ku dawo, Allah ya muku albarka baki ɗaya".

"Amin Mama". Ta amsa ta tana me share hawayen ta da bayan hannu

Daga nan Aunty Amarya sallama tayi mata

While Usman ya amshi wayan sa, sai da suka yi magana da Abbu kafin ya kashe wayan. Ya dube ta fuska a tamke yace, "tashi mu je".

Ko kallon sa bata yi ba, illa sake haɗe kai da gwiwa da tayi ta saki wani Marayan kuka, domin wayan nan da suka yi ba ƙaramin fama mata zuciya yayi ba, sosai take kuka kamar ana yanka ta, har wani shashsheƙa take yi

Hakan yasa ran Usman yayi mugun ɓaci, ya daka mata tsawan da ya razana ta lokaci ɗaya

A dai-dai lokacin ne Doctor Shamel ya shigo ɗakin, da mamaki yake bin Usman da kallo, sai yace, "what's going on?"

"Ka bamu sallama zamu wuce gida yau".

Murmushi Doctor Shamel yayi, cikin harshen turanci yace, "my friend ban da abun ka ka barta mana ta samu sauƙi, ka ga har yanzu da sauran rashin lafiya a tare da ita".

Usman be kalle sa ba ya saka hannu ya riƙo nata, jan ta ya soma yi dole ta sauko a kan gadon tana ci gaba da kuka

Dr. Shamel yace, "Oh Man, leave her. Don't hurt her. You see her crying. Maybe it's her body."

Shi dai be saurare sa ba tuni yayi waje da ita, be sake ta ba har sanda ya isa da ita motan sa, ya buɗe mazaunin gaba ya tura ta ciki, sannan ya rufe ya saka lock

DOCTOR'S FAMILYWhere stories live. Discover now