Episode Sixty Eight

288 11 6
                                    

💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎
*DOCTOR'S FAMILY*
🩺
💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎

🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱
*NAFEESAT RETURN*
🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱

*MALLAKAR:*
_NAFISAT ISMA'IL LAWAL_

*بسم الله الرحمن الرحيم*


*FEENAH WRITER'S ASSO*📖
'''®Ɗaya tamkar da Dubu'''💪✓

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*👈

*\F.W.A📚/*

*SADAUKARWA*
_Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. *GOMA'S FAMILY*_

.

*EPISODE Sixty Eight*

A taƙaice please. Kuyi haƙuri sabida abubuwa sun yi min yawa dole zan taƙaita labari na daga nan, ba wai don ya ƙare ba, amma dai na san kowa na son jin ƙarshen labarin shiyasa zan taƙaita.

An kai ruwa rana kafin Ɗahira ta yarda ta koma gidan Usman, a lokacin cikin ta ya shiga wata na biyar ne

Sai da aka sake shagulgula isu-isu ƴan gidan kafin ta tare, inda aka gyara mata ko ina

A ranan dai Usman yayi kwanan farin ciki, yau ga shi ga Ɗahiran shi cikin sukuni, domin ta rigada ta sallama tuni ta yafe mishi komi ya wuce, tunda ta koma kuma biyayya take mishi kamar yanda aka santa, hakan ya ƙara jawo shaƙuwa me ƙarfi da ƙauna a tsakanin su

Inda Usman ɗin ya so su wuce TURKEY yayi hutun amarcin sa da ya ɗauka

Amma Kaka ya hana, ya ce, "dole sai ta haihu".

Ba don ya so ba ya haƙura

Ita kanta Ɗahiran ma ba ta son zuwa sabida idan har suka je rayuwar da tayi a can ne zai dawo mata, amma bata ce mishi komi ba.

Cikin ta na wata shida Aunty Zulaiha ta haifi ɗan ta na miji, an yi suna inda yaron yaci sunan mahaifin mijin ta Aliyu, za su na kiran shi da Aiman.

Fannin Hajja Fatu kuwa don dole tayi ladab yanzu, domin ba kaɗan ba Abba yake gasa mata aya a hannu, duk wani jin daɗi yanzu yayi ƙaura a wajen ta.

Matsalan da Shakira take fuskanta wajen mijin ta Sahabi, zama dai ya ƙi daɗi, domin ashe har yanzu be dena bata ƙwayoyin hana samun ciki ba, ko ɓatan wata bata sake yi ba, sai da dubun shi ta cika ashe Allah ya bata ciki, daga baya da ya gane sai ya je ya siyo magani ya bata, ciki ya zube lafiya lau, duk a tunanin ta Allah ne ya ƙaddara hakan, domin yanda Sahabin ya nuna damuwarsa tsantsa dole ta cire tunanin komi, sai daga baya kawai ta kama shi yana waya da abokin shi, inda yake faɗa mishi komi "shi ne yake bata maganin hana ɗaukan ciki, don shi wlh be ƙaunar haihuwa yanzu sai nan gaba," sanadin da aka yi ta fitina kenan, daga ƙarshe dai aka raba auren dole duk da rai be so ba, amma su Big Dady sun ce, "dole sai ya sake ta, ya je can ya auro wacce ba ta son haihuwar". Ita kanta Shakiran hakan ya fi mata, domin burin ta yanzu kenan ta samu ciki, tunda ga shi duk ƴan uwan ta da yaran su, Fadila ma yanzu tana ɗauke da nata cikin, sai dai be kai wancan matsala ba, haka ma itama Aunty Zainab.

Ɗahira ta haihu lafiya ta samu Baby Boy, inda yaro yaci sunan Abbun ta, sunan Kaka kenan, Al'ameen, za su kira shi da sunan A'sim

An yi shagulgula an gama lafiya.

Sai kuma a lokacin ne aka yi bikin Firdausi ita da sauran ƴan uwan ta jikokin Granny, sun je sun kwana sun raɓashe.

Sai da Ɗahira tayi arba'in kafin suka tafi Turkay, satin su uku a can suka wuce Saudiya suka yi umra, sannan daga can suka wuce Dubai, sun yo wa ƴan uwa siyayya kala-kala inda suka dawo gida. Zaman su sai son barka, domin ƙauna tsantsa suke nuna wa junan su, gefe kuma ga ɗan su dake ta wayau tubarakalla.

DOCTOR'S FAMILYWhere stories live. Discover now