Page 2

114 4 1
                                    

*MAI ƊAKI...!*
FitattuBiyar

          ©️ *Nana Haleema.*

*Book 1*
*Page 2*

            Yadda take kallon sa idanun ta kyam a cikin nasa tana tab'e baki zaka d'auka d'anta ne ko kuma k'anin ta wanda suke sa'anni ita dashi, kana kallon irin kallon da yake masa zaka tabbatar babu girmamawa a lamarin, duk abinda yake fad'a girgiza kai kawai take yi alamun maganar ba shigar ta yake yi ba kawai dai tana jira ya kai k'arshe ta d'ora da abinda yake bakin ta itama. 

Duk da yana lura da kallon da take masa bai fasa fad'ar abinda yake fad'a ba yace, "Kina ji Atika?; Y'an mata uku ne a gaban mu ga babbar yayar su bazawara kinga guda hud'u kenan dukkan su babu manema, shekaru kullum ja suke gaba suke yi ba baya ba, yau in muna raye bamu da tabbacin zamu kai gobe a raye. Wannan dalilin ya saka na yanke hukunci ko nace muka yanke hukuncin zamu had'a su aure da y'an uwan su domin rufawa juna asiri."

Wacce ya kira da Atika ta gyara zama tace, "Ina jinka." Ya sake cewa, "D'an wajan Yayata Saifu kenan kinga yana da hankali da sa'ana kuma yana da aure da yara ya rik'e su da mutunci na tabbata muka bashi Maimuna zai rik'eta hannu biyu daga ita har yaran ta, shi kuma Kalamu ya nuna yana son Fauziyya me zai hana bazata amince ba tunda ta kammala karatun nata? In muka rage biyun kinga saura biyu ko babu komai za'a daina wayo damu a baki a cikin unguwar nan ana cewa sunk'i aure Muna jiran mai kud'i."

Ta tab'e baki tace, "To banda abin Alhaji sai me dan anyi yawo damu a baki? Ai ni da y'ay'ana bakin mutane babu abinda zai mana, inda baki yana fitowa a jiki da yanzu kaf jikina zagi ne da bakin mutane ne, musamman en uwanka da y'an unguwar nan meye basa cewa a kaina?.

"A'a Atika, in kasan bakin wani baka san na wani ba. Abinda ya kamata ayi shi na fad'a miki, kullum addu'ar mu Allah ya kawo musu mazajen aure kuma....." ta dakatar dashi ta hanyar fad'in, "Dakata Alhaji! Tun bayan da karayar arzuk'i ta same ka akwai wanda ya tab'a bani sabulu a cikin y'an uwan ka yace na kula da yarana?, nice nake fad'i tashin neman abinda zan rufa mana asiri har muka kawo wannan mataki. Yanzu kuma kwatsam sai azo da wani batun auren dole akan y'ay'ana? Auren ma kuma da y'ay'an y'an uwan ka?."

"Atika waye yace miki auren dole ne? Duka yaran nan su suka ce suna son su ba had'a su akayi ba ai baza ki kira shi da auren dole ba."
"Kaga Alhaji, ko auren had'i ne kona soyayya ban amince dashi ba wallahi. Babu wanda ya isa ya yiwa y'ay'ana auren dole ko auren cushe sai wanda ya gansu yace yana so suna so suma. Kafi kowa sanin harka da y'an uwan ka ba so nake ba domin tun farko ba k'auna ta suke ba dan haka kowa ya kama gaban sa shida yaran sa."

Kallon ta kawai yake yi yana jin duk abinda take cewa domin kuwa daman yasan ta gama raina shi gabad'aya bata ganin girman sa kamar ba mijin ta ba in tana yi masa magana, tunda ta fara d'aukar d'awainiyar da shi ya kamata ya d'auka a gidan shikenan dan ta kalle shi ta fad'a masa magana ba wani abun bane, wani lokacin tana mantawa mijin tane sai ta gama fad'ar maganar son ranta take tunawa, In tana yi masa fad'a kamar d'an da ta Haifa haka take yi. Ya sauke numfashi yace, "Yanzu so kike mu saka su a gaba muna kallo kenan?."

"Allah zai kawo musu har inda suke amma ban amince da auren dangin nan ba, daman ana musu kallon marasa tarbiyya in suka auri ahlin ka nan gaba shiga dangin sai ya gagare su ko kuma ace musu kafurai,. Bazan lamunta ba wallahi kowa yaje ya aura a waje har gida Allah zai kawo musu, duk wata mace da mijin ta a duniya sai dai in Allah bai rubuta zatayi auren ba."

Kai yake girgizawa kafin yace, "Ina da iko da y'ay'an nan kamar ke, ina da ikon aurar dasu na nemi shawarar kine dan kin kasancewa uwa a wajan su amma da zan iya yanke hukunci sai dai kiji labari." Tayi shewa tare da tafa hannu tana yi masa wani kallo na raini tace, "Allah Alhaji? A hakan yanzu akwai iko a tare dakai? Har kana da bakin ma fadar haka?. ai tun ranar da na d'aukewa y'ay'ana ci da sha, suttura da kud'in makaranta daga ranar na koma mijin ka koma matar. Me kake mana a gidan nan da zaka kalle ni kace min wai kana da iko dasu? Ai wallahi da kayi gangancin had'a auren nan da kayi gagarumar dana sani wacca Baka tab'a yi ba. Nice nake da iko da y'ay'ana bayan ni babu wani domin nice nasan wahalar su tsahon shekara goma sha, banga wani mai iko dasu bayan ni ba, kuma wallahi baza'a ayi auren nan ba."

MAI ƊAKI...!Where stories live. Discover now