37-38

84 19 0
                                    

👠👠
*YAWON* *SALLAR* *HAJIYA* *IYA*
( _A hanyar lamba_) 👜👜
       _17/7/2020_

*Written by*:- _Ameera Adam_
    _AmeeraAdam60_
*@wattpad*

*HADAKA WRITER'S ASSOCIATION*
_Home_ _of_ _co-opration_, _peace_ _caring_ _and_ _accepting_ _of_ _correction_ _among_ _us_✍🏼

*BISMILLAHIR* *RAHAMANIR* *RAHEEM*

                37&38

Hjy iya na kwance ta ga shigowar mutum tana shirin kurma ihu batayi aune ba taji anbanko kofar da karfi ga duhu dakin, cikin tsananin tashin hankali da gigicewa ta rafka wani uban salati tana neman agaji.
            " Jama'a ku taimaka ku kawon agaji yau ni hadiza me nake gani agidan duniyar nan, abunda nake jinsa wai-wai shi ne yau ya iso gareni, tsofai-tsofai dani na hadu da shaidanun zamani"

firgigit larai ta bude ido tana yan dube-dube cikin duhu, ta wawuri fitilarta haska dakin ta farayi bata ga komai ba cikin mamaki take tambayar hjy iya, " anya iya nikam ba mutanen boye bane suke san su fara tsorata ki, cikin dare sai ihu kike ko dai gamo kikayi?

        A'a hange nayi ba gamo ba, me kika dauke ni ne yarinya? To iya kina gani dai na haska babu komai adakin larai ta fada tana kara haska jikin bangwayen dakin.

Idan bakiga komai ba to ki sauka ki haska har karkashi gadajen nan, hjy iya ta bata amsa, da himmarta larai ta muskuta zata sauko daga gado tana hasko kasa ta hango inuwar mutum a jikin zanin gadon ta ya tsugunna, da alama wani ne ya lab'e a karkashin gado.

Wani razanannan ihu larai ta saki ta koma gado da baya tayi cen kuryar gado tana zunduma ihu.

_GIDAN ALH HABIBU_

Buguzum-buguzum haka ladidi ta tafi sashen su hjy mami, tana zuwa bakin falon ta canja tafiya tana dan dingisawa, tana shiga falon ta fashe da kukan karya na munafurci, matan gidan ne zaune da yara, lokacin Alh habibu ya shige sashen sa, dan tun lokacin da abun hjy iya ya faru ya ke kadaice kanshi daga cikin mutane.

Ido suka zuba mata har ta karaso cikin falon, tana zuwa tsakiyar falon kuwa ta kara rushewa da kuka sai da tayi mai isarta sannan, Auntyn yara ta fara tabayarta,  " lafiyarki ladidi ko wani abun ne ya faru?" girziga kai ta fara yi, mami itama ta jeho mata tambaya,  " to ladidi ko waya aka miki daga gida akace ba lafiya? Hjy ba daya daga ciki, yanxu hjy kamarni wai yaran nan zasuyiwa irin wannan cin mutumcin na tsamar nama, harda duka.

       duka yan falon zaro idanu sukayi cikin mamaki, Mami tace " duka ladidi ana zaune kalau to me yake damun su hazuma" , sharce hawaye tayi gefe sannan tace, " hjy ba su hazuma bane, sababbuun yan aikin da aka kawo ne" ladidi kina nufun  su inna zaunabu? To dududu mintinsu nawa a gidan ko awa guda basuyi ba shine har zasu nuna halinsu lallai da sake.

Ay ba tsohowar bace wannan yan matan ne akan ina gaya musu ayyukan gidan nan kuma nace musu bakwa san kazanta a gidan shine suka fara zagina dan nace zan gaya muku shine suka ce inje infada, dayar cikin su harda zagin uwata nikuma naji haushi na mareta shine suka rufeni da duka, ladidi na kaiwa karshe ta kara fashewa da kuka.

Sororo su hjy mami sukayi suna jin abunda ladidi taxo musu dashi.

Bayan fitar ladidi daga dakinsu, ta rasulu ce ta kalli su hansai tace,  " ku kuwa wane tsautsayi ne yaja ku yin fada da ladidi harda damb'e wallahi yau kunshiga uku da makircinta, da kun sani baku biye mata ba, muma nan da kuke gani wallahi hakuri mukeyi da ita, muna hakurin ma ya yakaya bare ku daga zuwanku har fada ya hada ku" ladifa ta karbe zancen da, " ni wallahi da suka fara fadan ma har kifta musu ido nake yi akan su kyaleta amma basu lura ba gaskiya suwaiba kun janyowa kanku, aikin da ladidi ma zata dinga saku kadai ya isheku"

YAWON SALLR HJY IYA CompleteWhere stories live. Discover now