Episode 53&54

198 17 4
                                    

*TAUFEEK*
NA
*Hafsat A Garkuwa*


*Episode 53&54*
… Da sauri yasa hannunsa na dama a saitin zuciyarsa tare da rintse idanunsa ji yake kamar zuciyarsa za ta fashe ƙirjinsa ta fito, jijiyoyin jikinsa ne suka fara wani irin mimmiƙewa duk wani lungu da sauƙo na jikinsa yaji yana bubbuɗewa hannunta da ke cikin hannunsa ya fara kurzawa da ƙarfi ƙarfi ko zaiji sassaucin da zuciyarsa take masa amma ina kamar ƙara angiza ta yake da sauri ya sake mata hannu jin bugun zuciyarsa na ƙaruwa.
Ganin ya saketa ne yasa da sauri ta buɗe murfin motar ta fita wanda a lokacin su Sweetie suka fito dan tuni an shigar da kayansu amma suka jisu shiru hakan yasa suka kasa hakuri sai da suka biyo sawo.
Tana fitowa tayi ido huɗu dasu Sweetie, Ka'aaf, Samha da kuma Huda da Nazmar a guje ta tawo dan ta mance ma da wani cikin da ke jiginta gudun take kamar wanda ba komai dake tattare da ita tana zuwa ta faɗa jikin Sweetie cike da farin ciki
"I miss u so so much My Sweetie."
Ta faɗa cike da bege, so ƙauna.
Rungumeta Sweetien ma tayi cike da ganin Ɗiyartata yadda take fidda wani irin sihirtaccen kyau duk da ta ɗan rame shima kuma saboda laulayin da tayi ne cike da farin ciki tace
"Wai Nabeeha kin mance abun da kike tattare da shine ko so kike mijinki ya ɗauremu har igiya ta saura in cikinsa ya samu matsala?"
Ta faɗa da alamar faɗa tana kallon motar da ɗannata yake ciki wanda yaƙi fitowa.
Da sauri ta sake Sweetie cike da kunya ta nufi Ka'aaf da ya haɗa girar sama da ta ƙasa dan fushi yake akan bata kulasa ba ta kula Sweetie
Sunkuyawa tayi tare da rungumesa a tare suka sauƙe ajiyar zuciya tace masa
"Tuba nake My love nasan nayi laifi ban fara kulaka ba na kula Sweetie a yafe ni."
Gaba ɗaya suka saka dariya ganin ya sake fuskar sannan Samha tazo ta rungumeta ita da Huda cike da farin ciki  Nazmar ne ya ƙariso inda take cike da fara'a yace
"Oyoyoo Ƙanwata kuma Auntyna munyi kewarki over wlh."
Dariya sukayi cike da mamaki take kallonsa ganin bata ga Jawaad ba dube-dube ta fara tace
"Bayin Allah banga fa Jawaad ba ina yake?"
Ta tambaya cike da damuwa.
"Yana gidan Mom tun jiya muka tattara muka koma chan nayi-nayi yazo mu tarbeki kuma yace bazai zo ba saboda baya jin daɗi."
Cike da tausayin ɗan uwan nata kuma abokin wasanta tace "Allah sarki Allah ya bashi lafiya."
Dan bata kawo komai a ranta ba falon suka shiga yana nan a yadda yake sai baza ƙamshi yake kamar ko da yaushe dan Sweetie ba baya ba wajen tsafta da ƙamshi a falon suka zauna aka fata hirar yaushe gamo Sweetie kuma kitchin ta shiga ta kawo mata ferfesun hanta wanda yaji kayan ƙamshi da Tambarin juice dan tasan me ciki a falon ta baje tanaci sai da ta kusa cinyewa tas tana zuba hira da santi sannan rasha juice ɗin ganin an fara ƙiran sallah ne Sweeetie ta raraka Nazmar ganin hirar baza ta ƙare ba su kuma suka rankaya ɗakinsu.
Tana shiga tace
"Allah sarki ɗakina nayi kewarka."
Samha ne cike da zolaya tace
"Yanzu dai ba ɗakin ki bane aro muka baki za kuma ki tafi ki bar mana kayan mu.
Hararar wasa ta galla mata ba tare kuma da tace mata komai ba ta shige bathroom Alwala ta ɗauro kana ta gabatar da sallah sai da akayi sallan i'sha sannan suka tashi akan dardumar suka fito falo.
Taufeeq kuwa tun da ta fita yaga gudun da take kamar ta mance tana da jiki ji yayi kamar ya fita ya hanata gudun nan da har cikin ransa yake ji amma kuma ya kasa harara ya wulla mata wanda ita dai bata san yanai ba, bai ƙara jin haushi ba sai yadda tayi ta rungumarsu tana shirin taƙushe masa hancin baby jiya yayi kamar ya fesgota ta dawo kusa dashi, ganin sun juya sun tafi ba tare da sun jira fitowarsa bane ya ƙara ɓata masa rai a fili ya furta
"Wato yanzu ni ba a damu da ni ba ko?"
Ganin babu mai bashi amsa ne yasa ya fito a hankali dan har yanzu zuciyarsa zafi take masa ta ƙofar baya ya shiga part ɗinsa yana nan fes kamar ko da yaushe Alwala yayi ya nufi masallaci dan an fara ƙiran salla.
A masallacin suka haɗu da Nazmar da Papa wanda dawowansa kenan ya ji ana ƙiran sallah shiyasa bai shigo ba ya nufi masallaci a tare suka shigo su ukun bakinsu ɗauke da sallama banda Taufeeq wanda yayi nasa chan ƙasan maƙoshi wanda daga shi sai zuciyarsa fuskar nan kuwa ya dake haɗeta kamar Zaki da fara Papa ya shiga yana faɗin
"Mutanan Abuja kun iso kenan?
Kayinta ta ɗan sauƙar cike da ladami tace
"Eh Papa ina wuni."
"Lafiya ƙalau Dota ya jiki dafatan dai kinji sauƙi?"
"Ai Papa na warke ma."
Ta faɗa cike da kunya tana dake sunkuyar da kanta ƙasa dan har ga Allah a karon farko kunyar mahaifin nata take ji.
Taufeeq ne ya ƙariso falon ya zauna a tare Samha da Hudah suka gaishesu kai ya jinjina musu ba tare da ya musu magana ba fuskar nan babu walwala.
A hankali ya buɗe baki yace
"Sweetie barka da dare."
"Barka dai."
Ta faɗa a ɗakile.
Kallonta yayi jin yadda ta amsa masa kwaɓe fuska yayi kamar zaiyi kuka yace
"Sweetie fushi kuma? ba gashi na kawo miki ita ba dan Allah kiyi haƙuri ni bana son fushin nan."
Ya ƙarisa maganar da alamun magiya.
Dariya Papa yayi yace
"To yau dai za aji kanku kenan?"
Murmushi Sweetie tayi kana tace
"Babu mai jin kammu My son naji daɗi sosai da ka kawo min ita Allah ya muku albarka."
Da "amin"
Ya amsa ciki da farin ciki dan a rayuwarsa babu abun da yafi ƙauna fiye da farin cikin iyayensa a ko da yaushe yana ƙaunar yaji albarka ta fito daga bakinsu zuga garesa.
Su Samha kuma suna zaune kamar gumaka dan ko kyakkyawan motsi basayi numfashi ma a hankali suke sauƙe shi kamar sun ga mala'ila dan fuskar san nan tam.
Nabeeha kuma mamaki take ganin sauyawar Abwaan ɗin nata lokaci ɗaya duk da dama tun da suka taho walwalar fuskar tasa ta ɗauke amma yanzu ya ƙara tamketa.
Papa ne yace
"Wato dai kun sake haɗakan to dai a juri zuwa rafi."
"Watarana tulun sai ya fashe."
Cikin haɗe baki Taufeeq da Sweetie suka faɗa dariya sukayi wanda Taufeeq kuma murmushi yayi dan har yanzu salam yake jinsa idanu ya zubawa Nabeeha wanda yake jin wani abu na daban na ƙara ziyartar zuciyarsa yace
"Ni yunwa nake ji."
Still yana ƙara kallon Nabeeha Sweetie ne ta miƙe ta nufi kitchin ta haɗo masa duk wani abu da ya sabaci a falon ya zauna yana ci amma idanunsa na kan Nabeeha su Samha dai a hankali suka zame suka bar falon Papa ma sama ya haura dan yauɗin a gajiya ya dawo ya rage falon daga Taufeeq sai Nabeeha da Sweetie.
Sweetie ne ta kalli Nabeeha ganin kamar a takure take cike da kulawa tace
"Maza tashi ki shige ɗakin ku naga kamar bacci kike ji."
Aiko kamar tasan a matse take da sauri ta miƙe har ta na haɗa hanya ta nufi ɗakinta na da.
Wani ƙululun ɓakin ciki ne ya tokare masa maƙoshi dan sam baiso hakan ba taya mutum da matarsa za a wani ce ta tafi wani ɗaki ji yayi abincin ya isheshi hakan yasa ya ture plate ɗin daga gabansa a hankali Sweetie ta ɗago tana kallonsa.
Langwaɓar da kai yayi kamar zai sa ihu yace
"Amma Sweetie ya za kice ta tafi chan bayan gasu Samha da Hudah a ciki ai zasu takurata da surutan su na banza da hofi me zai hana ta tafi part ɗina."
Murmushi Sweetie tayi har kuma za tayi magana sai ta fasa tace
"Kuma haka ne bari naje na sa ta tafi part ɗin naka tunda chan babu surutu sai dai tumurmusa."
Ta faɗa cike da gano inda ya dosa.
Shiko a karon farko farinciki ya cikasa dan tun da yazo gidan ba a masa abun da ya sashi farin ciki kamar wannan ba tashi yayi tun kan su fito yayi part ɗinsa damar kuma itace damuwarsa dan yasan bazai iya rintsawa ba in bata jikinsa.
Tana shiga ta samu sai hira suke zubawa babu alamun bacci a tattare da ita cike da kulawa tace
"Taso Nabeeha kije mijinki yana ƙiranki yana part ɗinsa."
Gabanta ne ya faɗi jin haka duk da tana son kasancewa da mijinta amma tasan baza su zauna haka wani abu bai faru ba cikin sanyi tace
"Tom Sweetie."
Daga haka ta fita tare suka fito Sweetie ta nufi ɗakin Papa domin kai masa abincin sa ita kuma ta nufi part ɗin mijintan.
A hankali take tafi kamar baza ta taka ba duk jikinta a sanyaye yake da sallama ta shiga falon a zaune ta hangesa yana zuƙan sigari a hankali yana fesar da iskar.
Har ga Allah bata ƙaunar shan sigarin da yake so take ta masa magana akan shan sigarin da yake amma tana matuƙar tsoro kar ya mata wannan marin nasa da baza ta taɓa mancewa ba.
A hankali ta ƙaro ta nemi kujera chan nesa da shi tana me toshe hanci saboda bata son warin ganin hakan da tayi ne yasa yayi saurin kasheta dan yayi tunanin ko cikin nata baya son warin hannunsa ya ware alamun tazo garesa.
Miƙewa tayi ta ƙaraso inda yake hannunsa ya jawota ta shige jikinsa ajiyar zuciya suka sauƙe cikin mayen sonta ya sanya hannunsa cikin rigarta tare da kama Nimple ɗinta yana wani irin murzawa cike da ƙwarewa.
Dama tasan hakan ce zata faru dan ta gama gane waye mijinta baya tasa gajiya da mace a falon suka gama taɓe-taɓensu da tanɗe tanɗe kana suka shige bathroom a tare sukayi wanka suka zube a kan gado baccin gajiya yayi awun gaba da su.


                          *******

Sai a lokacin taji wasu hawaye masu matuƙar zafi da ƙuna suka samu damar fitowa daga cikin idanunta a hankali ta ɗago ta kalli Abba cike ƙaunarsa tun da take a rayuwar bayan iyayenta bata taɓa ganin wanda ya sotsa tsakani da Allah ba irin Abba ita kanta tana jinsa a jikinta ji take ina ma shima ɗaya daga cikin ahalinta ne da tafi kowa farin ciki da murna sai dai kuma tasan hakan bazai taɓa faruwa ba goge hawayen da suka zubo mata tayi tare da gyara zamanta tace.
Abba duk wani zaɓin da kaga ya dace dani ka aura min ni mai bin umurnin ka ne in ma makaho ne ko kurma Abba ko da kuturu ne in ka aura min shi zan zauna da shi ni bai biyayyace a gareka Abba Lamir kuma Allah yasa hakan shine mafi alheri a gare mu baki ɗaya Allah ya bashi wacce ta fini.
Ta ƙarisa maganar tana goge wasu hawayen da suka zubo masa.
Abba cike da tausayinta ya kamota tare da goge mata hawaye yace
"Amatullah ba Kuturu ba ne ba kuma makaho bane ba kurma ba ne kuma in sha Allah ke kanki za kiyi alfahari da zaɓin da na miki ba kowa na zaɓa miki ba face ɗana kuma jinina mafi soyiwa a gareni wato Yayanku Saifudden.
A matuƙar firgice ta ɗago tare da dafa ƙirji cike da tsoro da kuma son tabbatarwa tace
"Yaya Saif Abba?"
Kai ya kaɗa mata alamar "eh" 
Wani jiri taji ya ɗibeta sai ji yayi ta faɗi ƙasa tim!
"Innalillahi wa'inna ilaihi rajioun Amatullah! Amatullah Amatullah!!!
Ya ƙirata tare da nufarta da sauri cike da tashin hankali jijjigata yake amma babu alamun rai a jikinta a daidai lokacin Ammy ta shigo domin za ayiwa su Amatullah ƙunshi ganin halin da take ciki ne cike da tashin hankali tayi kanta tana faɗin
"Subhanallah Me ya faru da ita Alhaji?
Ta faɗa tare da riƙota tana jijjagata amma babu alamar motsi a Tattare da ita Abba ne ya ɗauko ruwa tare da watsa mata amma babu alamun akwai wani sauran numfashi a tattare da Amatullah.
"Innalillahi wa'inna ilaihi rajioun!
"Allahuma ajirni fi musibati wa'akilni khairan minha…!

*My pan's yanzu tafiya ce miƙaƙƙiya muke ba tare da gargada ba in kun bani haɗin kai wajen yin zazzafan comments yanzu zamu kammala wannan littafi ba tare da ɓata lokaci ba, maza ku cigaba da mazgo comment ni kuma naci gaba da sambaɗo muku posting Ina sonku irin jibga jibga ɗin nan.*😘😘💋


#Vote
#Comment
#Share
#Taufeeƙ

*ONE LOVE💞🤞🏻*
08132761212

TAUFEEƘWhere stories live. Discover now