SANADI.....

506 46 26
                                        

FAIROOOZ

Daga Alk'alamin Ayshnur pyaar

             BABI NA SHA TARA

Muryar Aunty Mami wato (Darweeshat) ya ji a daidai inda take fad’in,

“Kuma ko da ban rayu ba wajen wannan aikin da za’a mun, *BAN YARDA A FAD’AWA FAIROOOZ CEWA NI CE NA HAIFE SHI BA*.

Ta d’an sauke ajiyar zuciya irin na wanda ke jin ciwo, sannan ta ci gaba da cewa,

“Meri baheen (My sister) ki ci gaba da rik’onsa kamar yadda kika saba, Fairoooz d’anki ne, babu kuma buk’atar nace ki rik’e amanarsa, domin duk wani abin da ya kamata Uwa ta gari ta yiwa d’anta, kin yiwa Fairooz shi.”

Kowa a cikin d’akin k’wallah yake zubarwa saboda yadda maganganun Daweeshat ke dad'a karyar masu gwuiwa.

Bud’o k’ofar da aka yine yasa ko wannen su waigowa ban da Daweeshart wacce dama already fuskarta, tana kallon k’ofar.

FAIROOOZ suka gani tsaye hawaye sharkaf sun jik’a mishi fuskarsa.

Hafeez da Babansu Yusuf, suna tsaye daga gefen hagu na gadon da Darweeshat ke kwance da rigar Asibiti, irin wacce ake sawa Mutum in za’a shiga dashi d’akin tiyata.

Abbas kuma da Zeenat suna daga gefen dama, kallo d'aya za kaiwa fuskar Dr. Abbas ka gane d’umbin damuwar dake tattare dashi. Zeenat ko kuka take yi mara sauti sai hawaye da yake ta zubowa a fuskarta tana sharewa.

Da gudu Fairoooz ya nufe ta, durk’usawa tayi tare da bud’a masa hannuwanta, yana zuwa ya fad’a k’irjinta ta rungumeshi, kuka ya keyi sosai.

Zeenat rarrashinsa take tana shashshafa sumar kansa, can ya d’ago da kanshi yana kallon ta.

“Mami, da gaske wai bake bace kika haifeni ba?”

“Fairoooz kai d’ana ne! D'ana ne kai har abada!.” Ta bashi amsa cikin kuka.

D’ago kansa yayi ya d’an zamo daga jikinta kad’an, sannan ya kalleta ido cikin ido yace,

"Mamina, daman ba ki tab’a haihuwa ba? kece daman ya kamata in rink’a yiwa Addu'ar ki sami haihuwa ba Aunty Mami ba! Kuma shine baki tab'a fad'amin ba...'' Yasa hannu ya share kwallan daya zubo mai, wad’anda har yanzu sun gagara daina zubowa daga idanunsa.

Magana yake tamkar ba k'aramin yaro ba, sai kace Babban Mutum me cikakken hankali.

Gaba d’aya jikin kowa a d’akin yayi sanyi da kalaman da Fairoooz ke furtawa.

Sakin Zeenat yayi daga rungumar da ta yi masa, gadon da Mahaifiyarshi ke kwance ya nufa idanunsa sunyi jawur, sai da ya kai har inda take kwance, kawai sai ya tsaya yana kallonta, kallon- kallo suke yi da ita.

Shi Fairoooz idanunshi cike suke da alamun tambayoyi, ita ko Daweeshat kallo take mai wanda ke fassara abubuwa da yawa.

Alama tayi mishi da hannunta cewa ya matso inda take.

Sunkuyawa yayi daf da ita, hannunta tasa tana mai shafar k'uncinsa, k'walla na zubo mata, bai san lokacin da ya rungumeta ba yana ci gaba da kuka mai tsuma zuciyar wanda ke saurarensa.

Daidai nan Dr. Sa’eed ya bud’o k'ofar d’akin tare da wasu ma’aikata maza su biyar, suna biye dashi a bayansa.

Cikin sigar tausayawa yace “Kuyi hak’uri fa Babban likitan dana kira ya k’araso, shi zai yi aikin kuma lokaci yayi, za’a shiga da ita yanzu.''

FAIROOZ LITTAFI NA FARKO Dove le storie prendono vita. Scoprilo ora