Babi na 16

937 72 0
                                        

Abincin gaban shi har yayi sanyi bai ma ko kalli inda yake ba yayi shiru kamar me d’aukar darasi,hakan yayi daidai da isowar Afreen cikin d’akin cin abinci domin a tunanin ta har ya gama ci ya bar wajen, turus tayi tana duban shi cikin nutsuwa har na tsawon dak’ik’ai sannan ta k’arasa inda yake ta tabbatar koma me yake tunawa yayi nisa ,tayi ta dariya sannan ta saka hannu cikin wani kwanon ruwa ta yarfa masa a fuska bai san lokacin da ya mik’e tsaye ba ba shiri nan ta kwashe da dariya tace ” idan kaga zaki yayi shiru duk da ga namun dawa kewaye da shi bai kuma lura da su ba balle har ya kai musu farmak’i toh lallai akwai abu a k’asa ” murmushi yayi murya k’asa k’asa yace ” toh sarkin iya surutu me kika zo yi a nan?”  Aiki mana yanzu ma zuwa nayi in duba ko ka gama na tattare ” Haba jameelah ban hanaki kiyi aiki a nan ba? Ni na baki wannan y’ancin saboda kin chanchanta” murmushi tayi ta sake yarfa masa ruwa a fuska nan ya d’auki ruwan ya bita da shi sai zagaya d’akin cin abincin suke yi gyaran Muryar da Sarauniya Ruqaiyah tayi ne yasa duk suka daskare cikin k’arfin hali Afreen ta fara tattare kwanukan abincin ta fice simi simi kai a k’asa yayinda shi kuma ya nemi guri ya zauna , a hankali take takun ta cikin k’asaita ta k’araso inda yake itama ta zauna ,tabbas taji dad’in ganin walwalar shi kuma bai dameta ba Wai don da waye d’an nata yake soyayya in dai har hankalin shi zai kwanta, ” Tashi yayi shima zai fita ,cikin sauri tace ” ina zaka je haka?” Babu ! Umm dama zamu d’an fita wajen gari ne nida Afreen ,tace bata tab’a ganin hamada ba a rayuwar ta ,shine zan kaita gurin” murmushi Sarauniya tayi sannan tace ” Amma fa kar kuje da nisa sosai * kai kawai ya gyad’a mata yace toh”.

               Tafe suke kowanne a saman doki sai hirarsu suke tayi ,suna isa wajen gari kawai Nawaz ya dubi Afreen yace ” Jameelah rufe idonki babu musu ta rufe ,ko da ya umarceta ta bud’e gurin da take ya matuk’ar bata mamaki ,(Kar fa ku manta masu karatu Nawaz yana tare da Asad) Zunzurutun hamada ne a gurin iska na tashi a hankali ,nan ta durk’usa tana shafa yashin gurin sai dariya take kamar sintacciya. Haka suka ci gaba da tafiya  cikin hamadar sai wasannin su suke in ka gansu gwanin sha’awa Kwatsam k’afar Afreen ta sark’e da wani igiya take inda take tsaye ya Burma tayi ciki gami da sa wani uban qara a take shima Nawaz ya bi bayanta ya afka cikin wannan makeken ramin wanda ya ta waje ya rufe kansa tamkar babu abunda ya tab’a Burma shi balle ya afka ciki:

GUGUWAR HAMADADove le storie prendono vita. Scoprilo ora