EPISODE THIRTY SEVEN&THIRTY EIGHT

197 23 0
                                    

WATTPAD:FOLLOW@SIYAMAIBRAHIM

EPISODE:37&38

Cikin sauri Agneta ta riƙo ta daga bayan da ta kusa faɗi tana faɗin
  "Ya haka me ke damin ki Juda"?faɗi tayi warwas a jikin Agneta daga haka bata san inda kan ta yake ba har sai bayan shafewar lokaci sannan ta dawo daidai..
  Buɗe idon ta yayi daidai da juyowar wanda ya firgita ta dan haka ta maida idanun ta ta rufe sai dai babu jimawa ta kuma buɗe su ta sauke kan wannan mutumi kafin daga bisani ta taahi ta zauna tana ƙarema ɗaukacin ƴan wurin kallo..
  Cikin sauri Berenice ta matso ta tana faɗin
  "Thank goodness kin farka na ji tsoro dan na rasa menene abin nan da ya firgita ki meke faruwa dake"!!
  Kasa cewa komai Juda tayi sai ma kallon mutumin nan da tayi tana son yin magana kuma ɗaukacin mutanin wurin sun gane tana son yin magana ne
"Me ya kawo ka nan kuma me kake yi a nan ina mun gama da shafin ku tun ba yau ba"?abin sai ya basu mamaki sai Berenice ta ɗan rufe mata baki tana faɗin
  "Juda meye kuma haka baki ga halin da suke ciki bane shi da matar sa"!?ƙyale ta Juda tayi tana cigaba da kallon su sannan daga baya ta ce
  "Ban ji amsar ka ba me ya kawo ku kusa da mu ko aiko ku aka yi ku zo kuyi garkuwa da mu"?har Agneta zata yi magana sai yayi saurin tsayar da numfashin ta ta hanyar fara yin magana
  "Ba komai abin da ya faru shine a jiya aka ɗaura aure na da na mata ta amma tun bayan ɗaurin auren nan babu kwanciyar hankali sai kawai ta rikiɗe min duk kuma mutanin dake wurin suka guje mu da fari nayi zaton abin zai sassauta amma sai gani nayi abin yayi yawa,ɗaukar ta nayi muka koma gida saidai ko da muka shiga gidar sai na rasa ya aka yi kawai buɗe idon da zan yi sai na tsinci kai na a nan ki yarda da ni ban san ya aka yi na zo nan ba dan hasalima a tsarin da muka yi ni da matata mun yi ne akan bayan auren mu sai mu koma ga masarautar su mu nemi afuwar mahaifiyar ta ta yafe mana in ya so sai muyi rayuwa irin ta kowa amma sai abin ya girmewa tunanin mu,..a nan na tsinci kan mu sai kuma na haɗu dake na kuma tuna na san ki a watannin baya shi yasa na zo nemar taimakon ki amma sai na ga kina gudun taimaka mana amma mun gode dan yanzu ta dawo daidai dan gashi har ta iya zama da kan ta kuma godiya gare ki da abokan tafiyar ki dan su suka taimaka mana"!..
  Wani irin mugun takaici ne ya kama Juda da jin wai su Berenice ne suka taimaka ma waɗannan mutanin abin ya kawo mata har wuya kamar ta shaƙe su dan takaici amma ta haƙura har sai sun keɓe dan ta ji haushi ba kaɗan ba..

  Bata amsa masu ba dan haka sai su Berenice da Agneta suka zamo masu maganan while Juda ta ƙyale su sai ma tashi tayi tayi shigewar ta cikin tantin ta ta kwanta..
  In za'a saka mata wuƙa ko takobi a wuya toh ba zata iya faɗin abin da ya sa take jin takaicin taimakon da su Berenice suka ma Cahal da gimbiya Ondrea ba ita dai ta san bata ji daɗi ba kuma ran ta ya ɓaci matuƙa..
  Har bacci ya ɗauke ta bata sani ba amma tsabar zullumi da ƙwallafawa ran ta abin sai da tayi mafarkin abin da ya faru ɗazu a baccin ta dan haka tun kafin gari waye ta shirya ta fita ta nufi hanyar rafin dake dajin dan yin wanka..
  Haka suke neme ta suka rasa da suka farka kaaancwwar ba addini ne da su ba sai kowa ya kama gaban sa har sai bayan rana ya ɗaga sannan suka dawo matattarar su suka zauna zaman jiran Juda yayin da Cahal ya tafi nemowa matar sa abinci dan ta sami ƙarfin tafiya saboda a jiyan bata wani samin baccin natsuwa ba duk a hargitse tayi sa sai daga baya ta yi baccin natsuwa amma duk ya kasa kwantar da hankalin sa dan bata saba da wannan halin ba..
  Iya tunani yayi yayi linking matsalar da ta same su da kiranyen sarauniya Zinaida sai kuma daga baya ya natsu ya zauna yayi nazari mai zurfi sai gano kamar ahalin sa ne ke mai wannan abin dan ya san shi dai rabon sa da gida da ahalin sa sama da shekara ashirin kenan kuma tun bayan barin sa gida bai kuma marmarin komawa ba sai a daren jiya da abin ya bijiro mai bayan doguwar tunani da nazarin da yayi..
  Baya so ya tuno past life event nasa dan ba mai kyau da daɗin ji bane amma ya san koma dai menene,a nan ƙasar aka haife sa a nan ƙasar ya bar iyayen sa da kuma abokan sa amma ba zai iya tuna ga takamammen inda suke residing ba sakamakon shafewar tunanin da ya riske sa tun bayan rabo sa da gida da aka yi...

BAMBANCIN ƘASA {Battle to reach} Where stories live. Discover now