EPISODE FOURTHY THREE&FOURTHY FOUR

190 24 0
                                    

EPISODE:43&44

Wani irin zagaye su aka yi da sai da suka tsorata dan kuwa dandazon mutani ne ba kaɗan ba a wurin abin ban mamakin kuma bai wuce ta yadda suka gano inda su Juda suke ba da har aka masu dirar miƙiya..
Kallon kallo suka aikawa junan su tunani kowa ke yi a ransa ta yaya zai yi galaba akan waɗannan mutani ba tare da an mai rauni ba..
Duk tunanin su ƙafewa yayi a wuri ɗaya sakamakon rashin madafa amna sun san ko ya nene dole su samo mafita ɗaya..
Duk wannan tunane tunanen a seconds aka aiwatar da shi duba da yanayin mutanin babu wani wargi ko wasa a tattare da su sai kawai masu baiwar sihiri suka yanke hukuncin yaƙar su da sihirin su kafin marasa shi su ɗauko abubuwan yaƙin su dan dai suyi distracting waɗannan mutani..
Kamar haɗin baki hukuncin da suka yanke da zuciyoyin su kenan amma kamar a zahiri suka yi sa..
Kallon hadarin kaji biyu daga cikik mutanin da suka yi dandazon suka aikawa su Juda kafin ɗayan ya tofar da yawu yana masu kallon ƙyama da ƙasƙanci sai da abin ya harzuƙa Agneta tayi kamar zata tunkare su dan tsabar wulaƙanci tsakanin su wa ya kamata ya karɓi kallon ƙasƙanci da ƙyama sama da su da suke yi,hana ta motsaywa Berenice tayi tana mai girgiza mata kai akan ta ƙara tsumayen su kafin su faɗi abin da ya ɗare su dan su yi faɗa da hujja..

Takowa ɗaya daga cikin su ya fara yi yana ƙare ma Fianna kallo dan duk ta fi su girman jiki,daga ita sai Berenice a girman jiki dan haka ana iya kiran ta mai girman halitta a cikin su su biyar ɗin..
Yana zuwa ya tsaya daidai ibda take tsaye ya rinƙa ƙare mata kallo yana bin ta da kallon zalama da kwaɗayi sai dai ta daure bata ce komai ba jira kawai take ya kawo hannun sa jikin ta ita kuma ta yanke dan takaicin ƙazamin duk ya ishe ta ga ƙazantaccen bulls da suka taho da su masu warin aladu duk sun cika mata hanci..
Bai taɓa ta ba amma haka ya rinƙa zaga ta kamar zai taɓa ta kamar zai lashe ta dan zalama..
Sai da ya shafe lokaci mai tsayi kafin ya dawo ta gaban ta ya kafe ta da ita,duk babu wanda ya tanka mai a cikin su sai bin sa da kallo da suke yi sai kuma kamar an tsungule sa ya fara dariyar tantirai marasa jin magana..
Duk a nanma babu wanda ya tanka mai sai da ya ji dariyar ta mai sannan ya tsagaita ya buɗe baki yana magana kamar dai yadda bulls ɗin nan ke gurnani babu daɗin ji haka shima muryar sa kamar ganga ta fashe ya fara magana
"Wai ke da ku duk masu iya riƙe razanar su ko?gani kuke dan kun ɓoye razanar ku ni zan wani yarda ne har in bar ku haka nan koh?wai shin ya aka yi ma ban iya yi maki komai ba ke mai farin rigar nan(wato Fianna dan kalar kayan jikin ta fari ne kuma da shi ta fito tun daga masarautar su),?uhum?kema baki sani ba ko?toh sai na taɓa ki dan na kwaɗaitu da ke duk da duban gari muka zo yi daga masarautar Sultan ba zan bari garaɓasa babba haka ya tsallake ni ba sai na lasa"..haka ya rinƙa magana kuma maganar na ta shiga kunnen Fianna ga wani haushin sa da take ji..
Sai kawai dariya ta kaure tsakanin mutanin da ya zo tare da su..
Wani juyawa yayi da alfahari ya kalle su yana faɗin
"Ku ma lu zo ku zaɓi naku dan ni dai wannan ita ce zaɓi na yarinyar akwai kyau,duk mace ɗaya maza biyar su huta da ita ni na baku wannan odar"!!sam bai lura cewa akwai namiji a wurin ba kasancewar Balik haka yake da fuskar mata ga yanayin da yayinda sumar sa kamar yadda mata ke ɗaurewa su naɗe sai wannan mutumi ya rinƙa masu kallon duka mata ne babu namiji a cikin su..

Daɗa matso Fianna wannan mutumi yayi yayin da sauran garorin dake tare da shi suka matso suma da zumar ɗaukar ko waceace ɗaya,ga wani wari warin da suke yi ga lashe bakim da suke yi kamar wasu karnuka sannan su su Juda tsoron su kar suyi wani ƙwaƙwaran motsi waɗannan bulls su haukace amma hakan ba yana nufin zasu yi ta tsayuwa bane dole su aiwatar da wani abin..
A daidai lokacin da wannan mutumi ya kawo hannu zai sauke saman ƙirjin Fianna sai kawai ya ji kamar hannun baya a jikin sa,dan haka ya ɗauke wuta ya tsaya cak na wasu mintuna,duka ƙasa da zai yi sai ya ga gunduwar hannun a ƙasa ga dungun a jikin sa,..
Waro idanu waje yayi yana kallon hannun sa a ƙasa yana kallon su Juda dake tsaye ga sauran da suka ɗebi jiki wai zasu tunkari su Juda..
Ai babu shiri ya sake wani razanannen ƙara da ya karaɗe dajin har ya saka bulls ɗin matsawa baya suna nemar mafaka dan sun tsorata..
Su kan su mutanin sai da suka ji kamar su gudu tsabar kaifin ihun sai ya fara magana cikin azaba
"Ku yanke su matan nan mayu ne sun cire min hannu na ku yanyanke suuu"!!!da ƙarfi ya ida maganar ƙarshe..
Toh dama Agneta ta gaji da halin da yake ta nuna masu sai kawai ta yanke hukuncin amfani da sihirin ta akan sa ta fara da shi kafin ta koma kan sauran..
Ai kuwa mutanin nan na nufo su wani irin guguwa ya taso ƙasa ya rufe masu idanun su ko da guguwar ta lafa sai suka ga su Berenice da takubba a hannayen su dama guguwar dan yayi distracting nasu ne kar su yunƙura su biyo su Juda har sai bayan sun ɗauko takubban su...
Wani irin mummunar yaƙi ne ya kaure a tsakanin su shi dai da aka guntilewa hannu yana can gefe yana faman kallon hannun dan yana tsoron kar ya fuskance su a kuma raba sa da hannu ɗayan in suka mai hakan sun gama da shi..
Faɗa ba na wasa ba five of them against the little crowd da zasu kai talatin da wani abu,babu wasa haka aka rinƙa kaiwa ana komowa..
Babu ƙarar abin da ke tashi a wurin nan sama da ƙaran takubban su da numfarfashin su dake ta tashi a wurin kwata kwata babu sauƙi faɗan,..
Lokaci mai tsayi suka ɗauka suna yaƙin nan har sai da aka yi jina jina aka zubar da jini faca faca kamar an yanka dabbobi..
Ko da abin ya lafa Callee ta sami rauni a hannun ta na dama ta sama sannan Juda ta sami yankewa a laps ɗin ta bayan su babu wanda yayi rauni sai gajiya da suka yi amma kaf jama'ar mutumim nan an ƙarar da su saboda nuna mai ƙasƙanci ma har kawunan wasu Juda da Berenice suka yankewa su wurgowa uban gidan nasu da ya basu odar yin abin da suka yi..

Juyawa yayi ya ga ko ina an gama da mutanin sa da ya taho da su sai ya fara rarrafen miƙewa zai nemi hanyar gudu,ashe dama ƙaryar iskanci yake yi yana da tsoro.
Dubawa yayi ya ga kamar hankalin su baya wun sa sai kawai ya tashi tsaye ya arta a guje sai dai yana tsaka da gudun ne kuma yaji an halbo sa da wani wuƙa daidai tsakiyar bayan sa..
Faɗi yayi a wurin yana shure shuren mutuwa,cikin sauri Callee ta ƙaraso ta cakumo shi tana tambayar sa
"Ina Sultan yake?in suke ajiye mutanin da suka yi garkuwa da su"?kallon ta yayi ya ga desperation a fuskar ta da muryar ta sai kawai yayi wani dariya mai tafe da ciwo da azaba ya ce da ita
"Ba zan bayyana ba kuma ku sani ba kun yi yaƙi da mu da ni ni Khalais kun tsira lafiya ba?toh gagarumin yaƙi na nan dumfaro ku ku tsaya ku gani sai zaman dajin nan ya maku wahala"!!!...tun kafin yayi nazarin furta wani abin ta yanke sa a wuya sai numfashin sa ya tsaya cak,alamar dai mutuwa yayi daga haka ta take sa ta wuce sai ga Juda cikin hasala ta zo ta ƙarasa raba kan da jikin sa ta aje gefe..

BAMBANCIN ƘASA {Battle to reach} Where stories live. Discover now