*🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸DAREN AURENA😭🔱⚜️❣️*
_Daga Alk'alamin✍🏾_
~*'Yar mutanan zazzagawa Naanah M Sha'aban*~_Labari mai tab'a zuciya❣️_
*Alk'alami yafi takobi❤️*
Shafi na 17
"Teemarh sai yau na tabbatar baki da mutunci, ashe ana baki abincina shine kike kai wa su wad'anchan matsiyatan, to wallahi baki isa ba tunda ba ubanki ne yake siyo abincin ba, shashasha 'yar gidan matsiyata" Jabir yayi magana yana cigaba da huci, Teemarh ta ce "To ai kai ne babban matsiyacin dan kuwa sun fika komai da komai wallahi, kuma da kake cewa ba mahaifina ne ya siya ba, na ji daman nace Abbana ne ya siya kuma haka nayi niyya su nake son na bawa abincin dan haka banga wanda ya isa ya hanani bawa su baba mai gadi abinci ba, kuma da kake ce min shashasha 'yar gidan matsiyata to sannu mai kud'i dan gidan k'aruna", Teemarh ta k'arasa maganar tana harararsa, Jabir ya gama fusata ya gama kaiwa k'arshe cikin zafin nama ya jayota yayi wurgi da ita kan kujera har sai da ta bugu da hannun kujerar goshinta ya fara zubar da jini, Jabir ya nufi kanta gadan-gadan Teemarh tayi saurin tashi tana nuna shi da yatsa "Jabir wallahi zaka san ni ka wurga kan kujera kuma...." bata k'arasa yin magana ba taji ya zabga mata mari har sau biyu hagu da dama ita ma kuwa tana d'agowa ta rama marin sai da ta jera masa sau hud'u sannan ta nufi hanyar fita da gudu tana kuka domin kuwa yau sai tayi wa Jabir sharrin da bazai tab'a mantawa da ita ba.
A babban falo ta tarar da mutanan gidan gaba d'aya ta je gaban Abba ta zub'e tana k'ara saka sabon kukan, Abba ya kalleta ya ce "Fatima meya faru" cikin kuka ta ce "Abba na shiga uku Jabir zai kashe ni, wai kawai yana shigowa d'akin ya fara dukana ya gwara min kai na a bango" Jabir da ke tsaye yana jin duk abin da ta fad'a dan Teemarh tana fitowa shima ya biyo bayanta "Wallahi Abba k'arya take yi wai fa dan......"wani irin mari Abba ya d'aukeshi dashi yana fad'ar "Ok k'arya take yi wannan jinin da yake zuba daga goshinta fa, shima k'aryar ne ko kana nufin ita da kanta zata jiwa kanta ciwo" ya rasa abin cewa domin kuwa Teemarh tayi amfani da wannan ciwon wajen yi masa sharri, haka ya juya jikinsa a sanyaye ya nufi d'akinsa, Abba ya kalli inda Teemarh take durkushe ya ce "ki yi hak'uri kin ji Fateema, Aliyu kira doctor ya zo ya dubata" Aliyu ya Amsa da "to" haka ko minti d'aya Aliyu bai yi da kiran doctor d'in ba sai gashi yayi sallama ya shigo da yake a unguwar yake, bandegi ya saka ya had'e mata goshin sannan ya rubuta musu magungunan da zata dinga sha, yayi musu sallama ya koma gidan shi, Teemarh ta ce "Nagode Abba Allah ya saka da Alkhairi" Abba ya ce "Amin ya Allah" haka ta tashi ta bi bayan Jabir zaune ta tarar dashi a kan kujera ya zabga tagumi, Teemarh ta shek'e da wata iriyar mahaukaciyar dariya tare da tafa hannu tana cewa "Jabir kenan ai yanzu wasan ya fara tagumi yanzu ka fara yin shi, ai wallahi sai ka gane kurinka, banza kawai" Jabir yayi murmushi tare da cewa "Teemarh kenan nii Jabir d'an tuwa kika yi wa wannan abin ko? To wallahi zan nuna miki cewa nii babban d'an iska ne, karki ga wai ina tagumi kiyi tunanin wai tsoron ki nake ji, to wallahi ba'ayi macen da zan ji tsoronta ko kuma ta takura min ba, Teemarh ki rubuta ki ajiye Jabir yana nan sai ya rugu rayuwarki gaba d'aya" Teemarh ta zauna a kan kujera tana murmushi tare da cewa "Me kake cewa maimaita inyi hadda" tsaki ya ja ya fita daga d'akin kai tsaye gurin da aka tanada dan ajiye motoci ya nufa ya ja motar da gudu har yana kok'arin kwarfe mai gadin da motar Allah ya taimaka ya kauce masa (ni kuwa 'yar mutanan zazzau nace wai Jabir an had'u da k'arfen k'afa ko nace gaba da gabanta Aljani ya taka wuta😂).
~*BAYAN WATA DAYA*~
Cikin Khadijatullahi yana k'ara girma dan yanzu watansa hud'u, duk da cewa yanzu ta rage yawan damuwa sai dai idan abin da Jabir yayi mata ya fad'o mata ta shige b'and'aki tayi kukanta mai isarta ta wanke fuskarta ta fito, ga laulayi ya sakata a gaba duk abin da ta ci sai ya dawo shiyasa kwana biyu basa zuwa makaranta ita da Amatullahi saboda Amatullahi ba za ta tab'a iya zuwa makarantar ba tare da Khadijatullahi ba, Hafsa kuwa tayi matuk'ar damuwar rashin zuwa makarantar da basa yi, shiyasa ita ma ta daina zuwa ya zamana kullum ita da Khalid suna gidansu Khadijatullahi, Aunty Murja da ta ga abin nasu ba na k'are ba ne, ranar wata Asabar bayan sun zo suna ta hira ta zauna tare da fara yi musu fad'a "Gaskiya mun ba ni mamaki sosai, yanzu ace kun daina zuwa makaranta saboda Khadijatullahi bata da lafiya bata zuwa, to insha Allahu gobe kowannan ku ya shirya zaku koma makaranta dan na gaji da zaman da kuke kullum kuka kullum cikin damuwa kuke ba za ku iya d'aukar k'addara ba kenan" Amatullahi ta kalli Aunty Murja cikin yanayin damuwa ta ce "Aunty Murja ba zamu iya zuwa makaranta ba tare da Khadijatullahi ba" Hafsa ta ce "Wallahi Aunty Murja gaskiya Amatullahi ta fad'a ba zamu iya zuwa makaranta ba tare da besty ba" Aunty Murja ta ce "Ai shine nace ku shirya gobe har Khadijatullahi dukkanku makaranta zaku tafi" suka amsa da "to shikenan Aunty Murja".
