*🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸DAREN AURENA⚜️🔱*
_Daga Alk'alamin✍🏾_
~*'Yar mutanan zazzagawa Naanah M Sha'aban*~_Labari Mai tab'a zuciya❣️_
*Alk'alami yafi takobi🤺*
Shafi na 15
Jabir ya nufi inda Khadijatullah take tsaye idanuwansa a kan cikinta "naji ance wai kina da ciki" sai Kuma yayi wani irin murmushin mugunta tare da ya mutse fuska sannan ya ce "Wayyo ni Jabir ina da k'arfin jini ace daga kwanci da mace sau d'aya har ta harbu ciki ya bayyana" cikin dakewa Khadijatullah ta fara magana "kaii tsinanne kayi gaggawar barin kofar gidan kafin na saka an jagaliya suyi min yaga-yaga da naman jikinka, shege d'an gidan shegiya" tayi maganar cikin zafin nama domin kuwa yau zata koyawa Jabir hankali zai san ita ma bawai k'anwar lasa ba ce Jabir ya kalleta sosai ya ga irin hucin da take kamar tsohuwar zakanya ya shek'e da wata iriyar dariya sannan ya ce "duk ki gama zagina karki ga nazo nan kofar wannan matsayacin gidan naku ki ce zaki yi min rashin mutunci ai kin san waye Jabir kuma kin san ba k'aramin aikina ba me wallahi yanzu a gaban kucakan 'yan layin naku nayi miki abin da ya faru ranar Asabar 26 ga wata march k'arfe 1 zuwa 2 na dare" wani irin a zababben mari ta wanke shi dashi hagu da dama sai da ta jera Masa sau biyar sannan fara magana "Eh tabbas nasan waye kai, Kai d'in ba kowa ba me in Banda dabba, Kuma ka sani idan a wanchan ranar kayi min ba yadda zan yi to yanzu baka Isa ba Jabir nima d'in nan da ka ke ganina ba k'aramar tantiriyar mara mutunci ba ce, wallahi Jabir na tsane ka na tsani duk wani Abu da ya dangance ka, Jabir idan baka bar nan kofar gidan ba zan iya kashe ka" magana take cikin wani irin yanayin bak'in ciki muryarta duk a shshshak'e, Jabir yaji matuk'ar jin zafin Marin da Khadijatullah tayi Masa domin kuwa tunda yake babu Wanda ya tab'a Marin shi, cikin zafin nama yake nuna Khadijatullah da yatsa Yana cewa "ba ni kika mara ba, wallahi ki jira zaki ga abin da zai biyo baya Kuma ki rubuta ki ajiye ni Jabir zan k'ara aurenki a Karo na biyu Kuma sai nayi miki abin da yafi Wanda nayi miki a baya" Yana fad'ar haka ya nufi motarsa ya bud'e zai shiga ya ji maganar Khadijatullah "Lallai Jabir sai yau na tabbatar Kai ka fi dabba ma, wa zaka aura?to Ina Mai tabbatar maka ni Khadijatullah na fi k'arfin ka, sai dai ka auri wannan shashashar uwar ta ka domin ita ce dai-dai kai, banza a jawo dak'ik'i Kuma insha Allahu sai kayi mutuwar da sai ana tattaro naman jikinka sai kayi mutuwar da ba za'a iya gane gawarka ba, na tsane ka na tsane shege Mai hali timakai" tana gama fad'ar haka ta shiga gida da gudu tana kuka, Jabir kuwa murmushi yayi domin kuwa yasan Yana zuwa gurin wad'annan kawun nata ya basu kud'i dole ko tana so ko Bata so a d'aura auren (ni kuwa 'yar mutanan zazzau nace Jabir ka makaro😂)
Ya shiga motarsa ya ja ya nufi gidansu kawun Khadijatullah, ko da ya je ya ga gidannasu gaba d'aya an ruguje shi, Nan ya tambayi wani saurayi a kan meya faru aka ruguje gidan Kuma Ina mutanan gidan, nan saurayin ya fad'a Masa duk abin da ya faru sannan ya d'ora da cewa "yaran gidan Kuma tun ranar da aka kawo gawarsu Kawu Sani suka tattara suka bar garin babu Wanda yasan inda suka je" Yana gama sanar dashi ya juya yayi gaba Jabir ya daki motarsa yanzu shikenan sai ya auri Teemarh damar abin da yaso shine ya samu a mayar da aurensa da Khadijatullah hakan ne zai saka ba zai auri Teemarh ba, gashi duk Shirin da yayi Yana nema ya ruguje, haka ya shiga motarsa ya nufi gida zuciyarsa cike da tashin hankali, Yana zuwa gidan ya tarar gaba d'ayansu suna falo Abba sai zagaye yake a falon kallo d'aya zaka yi masa ka tabbatar Yana cikin fushi ga Hajiya Asiya a gefe sai kuka take yi ita da Nihal saboda yau Alhaji Mansur tunda ya tashi ya tambaya Ina Jabir? Aliyu yace ya ganshi ya fita nan ya saka Hajiya Asiya a gaba yana Mata bala'i a kan ita ta saka shi a kan wannan tarbiyyar, Kuma yake shaida musu cewa Aure zai k'ara domin ya samarwa 'ya'yansa uwa ta gari shine fa suke ta kuka ita da Nihal, (ni kuwa nace wallahi Alhaji Mansur ka min dai-dai👏😂) Shahida da Aliyu basu ji haushi ko bakin ciki ba domin kuwa sun San tabbas Abbansu Yana buk'atar macen da zata kula dashi saboda Mami Sam Bata damu da ta kula dashi ba ita dai kawai tana zaune dashi ne saboda Yana da kud'i.
