*😭😭ĐÅŔĘŃ ÅÙŔĘŃÅ💔😭*
'''Łàbàŕį màį ťàbą žùçįÿą'''*Łábàŕį đà ŕûbùťáwą*
*Ńå*
*'Ÿåŕ mùťąń żàźźąù Ńââńâŕh M Śhâ'ábâń (Đįjąŕťÿÿ Łovę)*
08122188717*Follow me on instagram*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=1vzbjbvm85fw3&utm_content=k2qerlb
*Follow me on facebook*
https://www.facebook.com/naanerh.mshaaban.3*ku nuna min soyayyarku ta hanyar yin join d'in k'ungiyar wambai writer's association na facebook👇🏽*
https://www.facebook.com/groups/342151527397807/?ref=shareShafi na 37
*'BANGAREN ALIYU💔💍*
Da wuri ya dawo daga Office saboda ya d'auko su Khadijatullahi, ko gida bai je ba ya huce gurin da Shahida ta ke yin aiki ya kirata a waya ta ce masa yanzu zata fito ya jirata ta gama komai, ko minti d'aya ba'a yi ba sai ga Shahida ta fito gaban motar ta bud'e ta shiga, Aliyu ya ja motar ya huce makarantar su Khadijatullahi, ai kuwa yayi sa'a yana isa makarantar ana tashin su Khadijatullahi fitowa su ka yi daga motar suka jinjina a jikin motar, Khadijatullahi wacce tun fitowarta ta ga shigowar motar Aliyu gabanta yayi muguwae fad'uwa haka kawai ta ke jin wani irin abu a cikin zuciyarta, Amatullahi da Hafsa kuwa ba su gansu ba, sai da su ka zo daf dasu sannan Amatullahi ta gansu murmushi tayi tare da kallon Khadijatullahi "Besty ga mijinki ya zo d'aukarmu" Kallonta Khadijatullahi ta ce "Yaya Aliyu ai na ganshi tunda mu ka fito" Tayi maganar cikin wani irin yanayi dan ba ta son ran bestyn na ta ya b'aci.
K'arasawa gurin da suke tsaya su ka yi Hafsa ta rumgume Shahida tana cewa "Oyoyo sister ina Sister Nafisa" Shahida tayi murmushi ta ce "Nihal tana chan gidanta, ta koma yau satinta uku kenan da komawa" Hafsa ta ce "Allah sarki zan kirata kuwa" Sai kuma ta kalli Aliyu ta ce "Yaya Aliyu ina yini" Murmushi yayi sannan ya ce "Lafiya alhamdulillahi, ya karatu?",mun gode Allah" Hafsa ta fad'a tana kallon motar Yaya Safwan wacce ya kunno hancin motar cikin makarantar yayi parking sannan ya fito ya nufo gurin da su Hafsa suke dan ya gansu tun shigowarsa, hannu ya mik'awa Aliyu su ka yi musafaha Hafsa ta ce "Yaya Safwan wannan shine Yaya Aliyun da nake baka labarin cewar shi zai auri bestyna Khadijatullahi" Murmushi Safwan yayi ya ce "Ai na sanshi Aliyu Mansur Jikamshi"Aliyu ya ce "Wato Hafsyy har kin ba shi wannan labarin kenan" Yayi maganar cike da jin dad'in maganar Hafsa sannan ya dora da cewar "Ai mun san juna ni da Safwan sosai" Hafsa ta ce "Au to ai shikenan ma" Haka su ka yi d'an hira da bata huce minti biyu ba, Hafsa tayi musu sallama suka jera ita da Safwan suka shiga mota Hafsa tana d'agowa su Khadijatullahi hannu har suka fita daga makarantar.
Aliyu ya bud'ewa Khadijatullahi gaban motar ta shiga dan su Shahida tunda motar su Hafsa ta fita daga makarantar suka bud'e bayan motar suka shiga, suka bar Khadijatullahi a tsaye ita da Aliyu, shima zagayawa yayi ya zauna mazaunin driver ya ja motar suka nufi gida, Aliyu yana tuki yana satar kallon Khadijatullahi ita kuwa tana lura dashi dan tana kallonsa ta jefen idonta amman ta nuna kamar ba ta san abin da ya ke yi ba.
Suna isa gidan Aliyu yayi parking sannan ya fito daga cikin motar cikin takunsa na isa da tak'ama ya zagayo ya bud'ewa Khadijatullahi motar ta fito su Shahida ma suka fito suka shige cikin gidan, Aliyu ya kalli Khadijatullahi ya ce "My heartbeat idan kin shiga gida kin huta ki zo falon bak'i ina son ganinki keda yarona","To Yaya Aliyu" Tayi maganar a sanyaye tare da nufar hanyar shiga gidan, shima ya bi bayanta zuciyarsa cike da farin ciki, ta huce zuwa falo, shi kuma Aliyu ya shige d'akinsa.
Wajen k'arfe 8:00pm na dare sai ga Khadijatullah ta nufi falon bak'i tana rumgume da Affan a k'irjinta, ta shiga falon bakinta d'auke da sallama "Assalamu alaikum" Ido biyu ta yi da Aliyu yana zaune yana kallon bbc hausa "Wa'alaikissalam Matata" Ya amsa mata sallamar ciki muryarsa me jan hankalin mutane da kuma rud'a 'yammata.
![](https://img.wattpad.com/cover/282976445-288-k987421.jpg)