*😭😭ĐÅŔĘŃ ÅÙŔĘŃÅ💔😭*
'''Łàbàŕį màį ťàbą žùçįÿą'''*Łábàŕį đà ŕûbùťáwą*
*Ńå*
*'Ÿåŕ mùťąń żàźźąù Ńââńâŕh M Śhâ'ábâń (Đįjąŕťÿÿ Łovę)*
08122188717*Follow me on instagram*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=1vzbjbvm85fw3&utm_content=k2qerlb
*Follow me on facebook*
https://www.facebook.com/naanerh.mshaaban.3*ku nuna min soyayyarku ta hanyar yin join d'in k'ungiyar wambai writer's association na facebook👇🏽*
https://www.facebook.com/groups/342151527397807/?ref=share_Kuyi hak'uri fans kwana biyu kun ji ni shuru wallahi na shiga busy ne, amman idan komai yayi dai² zaku ci gaba da ganin posting d'ina kamar da🤝🏼❤️💃🏽 nagode ina sonku son so fisabilillahi💔🌹_
Shafi na 40
"Karka k'ara cemin wani babyn Jabir dan ni ba babynka ba ce, babu ni babu kai ka ji na fad'a maka ka fita idona" Tayi maganar cikin kunar zuci, murmushi Jabir yayi ya ce "Ok am so sorry dear na dena, amman dan Allah ki daure ki saurareni ko da sau d'aya ne kinji baby boo" Teemarh tayi masa wani irin kallo "Ba ni da lokacin da zan saurareka, ka matsa daga kusa da ni dan manzon Allah","Hmmm!" Abin da Jabir ya iya cewa kenan sannan ya koma kan kujera ya zabga tagumi yana kallonta ta cigaba da kukan, wani irin haushin kansa ya fara ji saboda ya san Teemarh tana son shi sosai bai kamata yana yi mata abin da zuciyarta zata k'untata ba, kwantawa yayi a kan kujera a hankali bacci mai nauyi yayi awon gaba da shi, ita kuwa Teemarh sai da tayi kukanta mai isarta bacci 'barawo ya sace ta.
~*BAYAN WATA BIYU✨*~
A yau aka d'aura auren Alhaji Mukhtar da Hajiya Asiya bayan rigingimun da suka faru a tsakaninsu, dan da aka sallameta daga asibitin gidanta ya kai ta inda matarsa ta nuna ba za ta iya zama da ita ba tunda ba matarsa ba ce ta ya ya zai d'auko macen da ba muharramarsa ya kawo ta gidansa, nan suka huce suka bar ta tana ta 'ba'batu ya kai ta d'akinsa, kullum ya zamana ya na gurin Hajiya Asiya a cikin d'akin domin so ya ke ya shawo kanta ya gama da ita amman sam ta k'i yarda ta ce masa ita ba za ta yarda tayi zina ba sai dai ya aureta haka ya amince ba dan yaso ba, wannan shine dalilin da yasa a ka daura auren Hajiya Asiya.
*Ya ku ke ganin wannan drama fans Alhaji Mukhtar ya auri Asiya domin ya cika burinsa a kan ta akwai cakwakiyoyi sosai🤣✨*
Haka Alhaji Mukhtar ya dawo gida jikinsa na rawa dan yau burinsa zai cika, dole Asiya ta amince dashi yanzu ko ta k'i ko ta so, kai tsaye d'akinsa ya nufa inda ya tarar da Hajiya Asiya tana kwance a kan makeken gadon d'akin, hannunta rik'e da waya tana daddannawa, da kallo ta bi Alhaji Mukhtar har ya k'araso kusa da ita ya washe baki tare da cewa "Hajiyata an d'aura fa" Hajiya Asiya ta ya tsine fuska "To yayi" Tayi maganar tare da cigaba da danna wayar "To yanzu dai ai zancen 'boye-'boye babu shi, tunda kin zama mallakina" Ya k'arasa maganar tare da fad'awa kan gadon, a gigice Hajiya Asiya ta mik'e tana kallonsa tare da dafe k'irji tana cewa "Me zan gani, me ka ke shirin yi min, to karka so ma ka ji na fad'a maka ban shirya ba" Wani irin kallon kin raina min hankali Alhaji Mukhtar ya ke bin Asiya dashi "Lallai ma Asiya ba ki san ma wanene Mukhtar Sa'id Baba ba, ki je ki tambayi Sadiya za ta fad'a miki wanene ni, indai ina son abu to dole fa sai na same shi ko ta wane irin hali ne, wallahi Asiya tunda aka d'aura mana aure to a yanzun nan sai na samu abin da na ke so gwanda ki shafawa kan ki ruwan sanyi, ki amince tun kafin ki ga ba dai-dai ba" Wata iriyar mahaukaciyar dariya Hajiya Asiya tayi tare da cewa "Ka na tunanin zai amince ka kusance ni ne, to idan mafarki ka ke gwanda ka farka don kuwa ni Asiya wallahi na fi k'arfinka, ba zan iya amincewa d'an mafiya ya kusance ni ba, ko kuma nace matsafi" Ai tana k'arasa maganar ta ji ya d'auketa da wasu zafafan mari tun ina argawa har sai da na gaji na daina na ce Allah ya k'ara wallahi🤣.
![](https://img.wattpad.com/cover/282976445-288-k987421.jpg)