EDISODE 4

401 22 0
                                    

🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
      *😢DAREN AURENA💔*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸

*Daga Alk'alamin✍🏾*
*'yar mutanan zazzagawa Naanah M Sha'aban*

_Labari mai tab'a zuciya_

Shafi na 4

Tun k'arfe hud'u da aka shigar da Khadijatullah Emargency room har k'arfe 8pm na dare, Babu Wanda ya fito daga Emargency d'in daga nurses d'in har doctor Halima,hakan yasa Aunty Murja da Amatullahi suka shiga cikin matsanancin tashin hankali suna tunanin kodai Khadijatullahi ta mutu ne.

A b'angaren doctor Halima kuwa tunda suka shiga da Khadijatullahi suka shiga kok'arin ceto rayuwarta da ta d'an dake cikinta, yanayin Khadijatullahi ya tsananta domin numfashinta sai kok'arin d'aukewa yake yi, ga bugun zuciyarta sai bugawa yake da k'arfi tamkar ganga ake bugawa, gashi sai wata irin jijjiga take yi, sai da nurses kusan biyar suka rirrik'eta,hankalin doctor Halima ya tashi domin har ta fitar da ran rayuwar baiwar Allah, Anan take ta fara zubar da hawaye domin taga tashin hankali k'arara a fuskokin 'yan uwannata da suka kawota, yanzu idan aka ce ta mutu, ta san zasu shiga cikin mugun yanayi, anan take wani tunani yazo mata da sauri ta fita ta kofar baya office d'inta ta shiga taje ta had'o allurai ta dawo Emargency room d'in tayi mata, cikin ikon ubanjigi tana mata ko minti biyar ba'ayi ba, ta samu bacci, wata iriyar nannauyar ajiyar zuciya doctor Halima tayi tare da cewa "Alhamdulillahi Allah na gode maka" fita tayi domin ta koma office d'inta amman wannan karan ta kofar gaba ta fita, ai kuwa su Aunty Murja na ganinta sukai wajenta tare da wurga mata tambayoyi "doctor ya Khadijatullahi? Kodai ta mutu ne? Dan Allah ki sanar damu idan ta mutu" kamar had'in baki tambayoyin nasu suka zo dai-dai, "ku biyo ni office" tayi maganar a takaice, tare da yin gaba suka rufa mata baya da sauri, suna shiga doctor Halima ta huce kujerarta ta zauna, su kuma suka zauna a kujerar da ake ganin likita, bayan doctor Halima tayi d'an rubuce-rubucenta sannan ta d'ago tana yi musu bayani "A gaskiya 'yar uwarku tana cikin halin damuwa da kuma tsantsar tashin hankali, wanda a binciken da nayi na gano cewa ta dad'e a cikin wannan yanayin, kuma uwa uba wannan k'arar da ta suma ya k'ara sakata a cikin razana wanda har zuciyarta tana kok'arin bugawa, amman yanzu Allah ya taimaka mun shawo kan matsalar ta ta, amman in har zata cigaba da saka abu a ranta wanda har zai sakata ta dinga shiga damuwa to zata iya kamuwa da babbar matsala a zuciyarta kuma babyn cikinta zai iya samun matsala shima".

Wata iriyar wahalalliyar ajiyar zuciya suka sauke, doin tunda doctor Halima ta fara magana suka kafeta da idanu sai da ta gama bayanin, Aunty Murja ce ta ce "to doctor mun gode sosai,Allah ya saka da alkhairi, kuma insha Allahu zamu yi iya bakin kok'arinmu ganin mun fitar da ita daga cikin halin damuwar da take ciki".
Wata gajeriyar takadda ta mik'a musu Aunty Murja ta k'arb'a, doctor Halima ta ce "gashi nan magungunan da za'a siyo ne domin idan ta tashi sai a bata d'an ruwan tea ta sha ya d'an ratsata, sai ta sha maganin".
Godiya suka k'ara yi mata sosai sannan suka tashi suka fita, Emargency room d'in suka nufa domin ganin yaya jikin Khadijatullah d'in, d'akin da aka kwantar da ita suka tambaya wata nurse ta nuna musu, suka shiga da sauri Amatullahi ta k'arasa kusa da ita ta kama hannuwanta sai ta fashe da kuka tana magana ciki tashin hankali mara misaltu "dan Allah Khadija ki tashi kin barni a cikin matsananci hali, Allah ya isa tsakanina da Jabir bazan taba yafe maka ba, kai ka jawo mana duk irin halin da muke ciki yanzu da muna cikin kwanciyar hankali amman yanzu ka tsarwatsa mana farin cikinmu insha Allah sai kayi mummunan k'arshe sai kayi mutuwar da ba za'a iya gane gawarka ba shege,d'an iska, azzalumi mara tausayi, mara imani" duk tana kuka take yin wad'annan maganganu, dafata Aunty Murja tayi ita ma tana hawayen "haba Amatullahi ki daina irin wad'annan furucin a kan Jabir, tabbas mun san ya zalinceta amman haka Allah ya riga ya k'addara mana kuma kin san komai muk'addari ne, kuma kowane bawa akwai irin tashi k'addarar ki yi hak'uri kinji k'anwata" ta k'arasa maganar tana bubbuga bayanta, Amatullahi kuwa ta riga ta gama kaiwa k'arshe tabbas da ace Jabir zai bayyana a yanzu zata iya k'asheshi domin ta ramawa k'awarta abin da yayi mata, kallon takardar hannun Aunty Murja tayi wacce doctor Halima ta bata ta magunguna "Aunty bani takardar nan zan siyo magungunan kafin Khadijatullah ta tashi tunda ance tana tashi a bata tea sai a bata maganin" babu musu Aunty Murja ta mik'a mata domin daman ta ba san indai zata samu kud'in siyo magungunan ba, tana kan tunanin ko taje ta ari kud'i sai kuma Amatullah ta ce ta bata zata siyo, tashi tayi daman hijabi ne har k'asa a jikinta ta ce "Aunty Murja sai na dawo" kafin Aunty Murjan ta bata amsa ta fita da sauri.

DAREN AURENAWhere stories live. Discover now