*B̆ĂK̆'ĂR̆🤦🏻♀ĞŬĞŬW̆Ă*
🧶🧶🧶🧶🧶
🧶🧶🧶🧶
🧶🧶🧶
🧶🧶
🧶S⃠t̾o̾r̾y̾ & W⃠r̾i̾t̾t̾e̾n̾
*ცყ:✍🏻*
R⃠αвí'αt ѕвѕ
*(ცıɠ ɠąι)**©-Aɴᴀ ᴛᴀʀᴇ Wʀɪᴛᴇʀs Assᴏᴄɪᴀᴛɪᴏɴ ✍🏻*
(wє ѧяє ṭһє ɞєśṭ ѧṃȏṅɢ ѧʟʟ wяıṭєяś)📚
https://mobile.facebook.com/Anatarewritersassocian/*Ana тare wrιтerѕ aѕѕocιaтιon* ĸυna nan a raιna вan ware ĸowa вa, dυĸ rυnтѕι Ana тare🤝🏻
*_ѕannυ da ĸ'oĸ'arιn poѕтιng ѧтĸ_*
_нaѕѕan тanĸo_*fαδῖlα αlῖϒῠ ϻῠsα (ϻα δῖlαlα ) αshα kαrαtῠ lαfῖϒα ❤*
*P⃠age➡22*
Yaga sak'onni tare da kiran wayar da ya rasa (missed calls) nata shigowa, sak'onnine masu yawan gaske wanda beyi tsammanin ganin yawan su ba, fuskarsa cike da mamaki yake duban wayar shi kuwa Aamir dake gefensa na dama kallon yadda fuskar Najib d'in take canjawa daga walwala zuwa akasin hakan yake, har yanzu Najib cike yake da mamakin irin yawan sak'onnin daya gani, gani yake kamar ya shekara be kunna wayar ba koda sak'onnin suka gama shigowa cikin wayar fara duba sunayen wanda suka kira shi yayi kafin yaje ga duba sak'onnin da suka shigo, fuskarsa cike da mamaki ya k'ara fidda kwayar idanuwansa ganin wani kira yayi, yana dubawa yana murmushi Aamir na ci gaba da kallonsa kamar wani zararre, daga can kuma ya saki wani k'ayatac-cen murmushi ya ci gaba da duba wayar, zuciyarsa cike da farin ciki, kamar wanda aka yiwa albishir zuwa k'asa mai tsarki dan sauke farali. Haka yaci gaba da kalla yana murmushi banda kallon bakinsa da duban wayar da yake kallo babu abinda Aamir yake shi dai ya rasa me yake sashi haka, wanda yasa har fara'ar sa take fitowa fili? sosai ya sake matsawa kusa da shi dan ganewa idanuwansa abinda yake kalla yake murmushi, sai dai kuma shi bega komai ba face wani suna daya gani wanda ya tabbatar masa da cewa tabbas yana da nasaba da sunan Zarah musamman yadda yaga an rubuta Zarnaj. Ganin hakan ya tabbatar masa da cewa sunan Zarah ne da Najib d'in ya had'a da nasa, wai me yasa Najib ba zai bar yarinyar data hulak'an ta shi ba? Nifa da ace ni tayi wa haka wallahi babu abinda zaisa na kuma sata a raina har na runk'a tunaninta, ya fad'a cikin zuciyarsa yayin da yake k'ok'arin matsawa daga wajen Najib d'in zuwa can wani gefen daban dan shi a ganinsa wannan b'ata lokaci ne tsagwaransa. shi kuwa Najib ci gaba da kallon wayar yayi bayan ya gama k'arewa sunan nata kallo, ya nufi wajen text message dan duba sak'on nin da suka shigo wayar. binsu yayi d'aya bayan d'aya yana karantawa wasu yana da lambobin su wasu kuma ba shida su, irin 'yan matan nan ne masu bibiyarsa suce suna sonsa sune suke samo number sa su tura masa sak'onnin soyayya amma shi sam! Ba a gabansa suke ba dan babu me burgeshi sama da Zarah sai da ya fara tun daga farkon sak'on daya fara shigowa wayarsa har zuwa kan na k'arshe daga nan kuma ya b'ata rai ya d'aure fuskarsa kamar wanda ya sha mad'aci, duk wannan abin da yake Aamir na kallonsa ba tare da yace da shi komai ba face wayarsa daya d'auka yake latsawa, ganin yanda ya had'e girar sama data k'asa yasa Aamir sake kallonsa tare da jan d'an guntun tsaki sai a lokacin yayi magana "ba kada aikin yi ne ka zauna kana kallon sunan da ba shida wani amfani a gareka, kana ji da kanka kana k'ok'arin cutar da kanka a banza" ba komai ne ya b'atawa Najib raiba face duk yawan tilin sak'onnin da suka shigo wayarsa babu sak'o koda kwaya d'aya daya fito daga wajen Zarah, anya kuwa Zarah bata daina sona ba? Ya tambayi Zuciyarsa wadda itama ba tada amsar tambayarsa, kallon Aamir d'in yayi "nasan ba zaka tab'a ganewa ba koda kuwa nayi maka bayani soyayya ba abota b'ace domin kuwa ita tafi abota wata abotar ce take fin soyayya amma abune guda d'aya sai dai dole akwai mafi rinjaye ciki yayin da zuciyarka ta kamu da son abinda kake so to babu shakka zuciyarka ba zata tab'a samun sukuni ba har sai ta mallaki abinda take da muradin mallaka, nasan dole jina kake kana ganin wautata ba haka bane, ba kuma laifi na bane laifin zuciyata ne data kasa cire son Zarah ba zan iyaba, bana ma so ta cire mun sonta ina sonta, ina kuma so son nata yaci gaba da dauwama cikin zuciyata" Mamaki ne ya mamaye zuciyar Aamir musamman yadda yaga Najib ya zage yanata baya ni kamar wanda ya zauce kallonsa kawai yake ya kasa cewa da shi komai wannan wanne irin so ne me haukatar da zuciya?kodai yarinyar nan da abinda tayi masa? Yana cikin tambayar zuciyarsa yaji Najib yace "Ka daina mamakin maganata idan kana so ka san irin abinda nake ji ka fara soyayya, nasan tabbas kaima zaka zama kamar zautacce idan har kayi dace, kai koda ma ace baka yi dacen ba muddin kai d'in zuciyarka ta aminta da ita zaka zama kamar zautacce sai dai idan daman ba soyayyar ba ce abota ce, wata abotar ma takan zama tamkar soyayya". Bud'e baki Aamir yayi yana kallon Najib dake gefe guda zaune yana ta jawabi yama rasa me zai ce da shi dan haka ya tsaya yana ta saurarensa, Najib yaci gaba da magana "wallahi ina son Zarah, bana son rabuwa da ita, da ace nasan zata kirani ba zan tab'a yarda na tafi asibitin nan ba koda kuwa zan mutu gwara na mutu bayan munyi waya da ita" Aamir ya dad'a fidda kwayar idanuwansa waje fuskarsa cike da manakin maganar da Najib yake fad'a a hankali yace "lallai ka zauce a soyayya sai dai nace Allah ya yaye maka sonta dan wannan ai masifa ne" da sauri Najib yace "Ba amin ba dan ni bana fatan sonta ya ragu a zuciyata koda da d'igon kwayar hatsi ne, ka daina kira mun masifa dan Allah, son Zarah ba masifa bane alkhairi ne gareni". jinjina kai Aamir yayi tare da fad'in "lallai kam! Allah to ya kyauta" najib ya amshe da "Amin, ko yanzu ma ba komai ne ya b'atan rai ba face rashin ganin message d'inta da nayi" dariya Aamir ya kyakyace da ita tare da cewa "ai kaji inda matsalar take rashin damuwa da Kaine yasa ta hakan, inda ta damu da kai ai da bata yi maka hakan ba, kai daka damu da ita har kake k'ok'arin cutar da kanka sak'onni nawa ka tura mata? Amma babu wanda ta kalla balle ta dawo maka da reply ba tada lokacin ka" bak'in ciki ne ya kama zuciyar Najib shi baya so yaji ana kushe Zarah koda kuwa tayi abinda ba dai-dai ba shi dai-dai ne a wajensa. A fusace yace "kaga dan Allah ya isa a bar maganar haka" Aamir ya bishi da kallo yace "to tattabara uwar soyayya ai shikkenan", daga nan be sake magana ba yaci gaba da danna waya shi kuwa Najib ya hau tunane tunanen Zarah ya rasa menene tak'a maiman abinda yake faruwa game da soyayyar su? Ko dai ta daina sonsa ne be sani ba ko kuma wani ta samu ya janye mata zuciya? Kai taya ma haka zata faru? Amma kuma idan har haka ne me yasa ta kira wayata? Kai amma abin da mamaki kuma fa hakan sai ya iya faruwa tunda kiran nata ya kai wajen sati guda ko dai ma kira tayi ta sanar mun cewa ta samu wani?" duk wannan zuciyarsa ce take sak'a masa hakan da sauri yake katse tunanin, abinda yafi d'aure masa kai shine taya tsawon lokacin data kira bata samu ba ba zata turo text ba? Tabbas Zarah ta daina sona duk zuciyarsa ce take raya masa hakan sai dai kuma ya k'udurci cewa ba zai tab'a zuwa gidan su ba tare data bashi damar zuwa ba balle kuma yanzu da suke cikin wannan hali da har yanzu basu sasanta ba bare ya samu yaje.
_________________★
Yau ita ce ranar da aka bawa Zarah damar kawo saurayin da take so tun wayewar gari take ruk'e da waya dan ganin kiran Najib ya shigo amma ina! bata ga kiran ba da ta ji ringing d'in waya sai tayi sauri ta kalla tunaninta Najib ne ya kira sai kuma taga ba shi ne ba, al'amarin da yayi matuk'ar dagulamata tunani kenan data kira jamila tambayar da ta yi mata shin ta kuwa tura masa sak'on da tace ta tura masa?amsawa Zarah tayi da cewar ta tura masa tun a lokacin amma taya za'ayi ace sak'on be je masa ba dan da ace yaje dole zai kirata ko kuma yayi reply sai dai kuma ai wayar a kashe take, to ko dai wayar ce ta samu matsala?, ko kuma dai yayi blocking layin nata ne shi yasa bata samu idan ta kira?, ko dai ya sake layin waya ne? Kai! wannan abu da ban mamaki yake, zan tukan da suka runk'a tattaunawa kenan wanda kuma suka kasa gane amsarsu k'arshe ta hak'ura ta kyale, har zuwa dare Zarah bata samu sakewa ba, bata kuma kira wayar Najib d'in ba a wannan rana illah sake duban wayar ta da tayi dan tabbatarwa da zuciyarta cewa wannan sak'on data tura ya isa gareshi kuma hakan ta gani ya shiga wayarsa me yasa be kira ba? Wannan tambayar take taiwa zuciyarta wanda ba tada amsarta. Tana cikin wannan tunani Hajjiya Usaina ta shigo d'akin gaban Zarah ne ya yanke ya fad'i dan ta ruga data san lokacin da take gudun zuwa yayi Hajjiya tace "na zata baccin naki da kika saba kike? Kizo inji Abbanki" da sauri Zarah ta kuma duban Mummy gabanta yaci gaba da bugawa da k'arfi nan take taji kanta ya sara, Hajjiya usaina bata saurareta ba ta wuce ta koma sashin Alhaji, Zarah kuwa nan ta fara tunane-tunane da sak'e-sak'e gami da zancen zuci bata san me zata ce da Abbah ba idan ya tambayeta, "wayyo! Allah na" ta fad'a a zuciyarta itace ranar da bata son isowarta, ko dai nace musu ba shida lafiya? Karfa na d'ora masa cuta, to kuma idan ya daina sona fa? in akace in ya warke yazo ya zanyi? Duk zuciyarta keta raya mata tana cikin nazarin abinda zata je ta fad'a musu kenan ta kuma jiyo muryar Hajjiya na cewa "kefa ake jira kink'i fitowa" da sauri cikin rawar jiki Zarah ta janyo hijab ta saka sannan ta fita zuwa sashin Mahifinta kanta a k'asa tayi sallama ta shiga d'akin kamar wata malama, gefe guda mahaifinta yayi mata nuni data zauna bayan sun amsa sallamar da tayi ta nemi waje ta zauna kamar wata bak'uwa sannan ya fara da cewa "kamar yadda nasa mahaifiyarki ta tambayeki game da yaron da kike so kuma ta tambayeki kika sanar mata to Alhamdulillah naji dad'in hakan sosai" wata masifaffiyar kunya ce ta lullub'e Zarah ji take kamar ta hak'a rami ta shige ciki ta rufe dan kunya yaci gaba da magana "sannan shi yaron daya turo mahaifinsa d'an wajen Alhaji D'ahiru naje na same shi tun washe garin ranar na basu hak'uri da shi yaron ya nemi wata alhamdulillahi mahaifinsa ya fahimce ni" Hajjiya Usaina dake gefe guda tayi murmushi, yayin da Zarah gabanta yaci gaba da bugawa dan bata san me zaice a magana ta gaba ba, yaci gaba da magana "Sanin kanki ne ba zamu zauna da ke muna kallonki ba, lokaci yayi da kika mallaki hankalin kanki kema ya kamata ace kina d'akin mijinki, duk macen da kika gani babu wadda take k'are rayuwarta a gidansu sai dai gidan mijinta, in har ba wai Allah ya k'adarto cewa ba rayayyu bane, wasu da kud'i suke samo mazajen auren wasu kuma su zauna a haka gasu da kyan da komai amma babu mazajen aure sai an had'a da rubutu da rok'on Allah, ke kuwa fa? Ba rok'a kika yi ba babu wanda ya nema miki zuwa suke babu adadi me ya kamace ki kiyi? Kamata yayi ace kema kin zab'i wanda kike so tun kan lokacin rasa su yayi, dan da yawa damam-maki na zuwar wa mutane amma wasu mutanen su suke janyowa kansu rashin samun damar, lokacin da mace take da dama sai tayi watsi da damarta ta bi rud'in duniya da sharrin shaid'an wanda a k'arshe babu abinda zai amfanar da ita face b'acin rai" Hajjiya tace "gaskiya ne wannan" wasu hawaye ne masu zafi suka fara kwaranyowa kan kuncin Zarah ji take kamar lokacin barinta gidan ne yazo ta saka hannu ta share wanda ke k'ok'arin gangarowa Alhaji yaci gaba da magana "kamar yadda nasa a sanar dake cewa ki turo wanda kike so na baki zuwa sati d'aya sanin kanki ne yau itace ranar daya kamata ki turo shi amma banga alamarsa ba" tunda ya soma wannan maganar gaban Zarah ya k'ara yankewa ya fad'i Alhaji yaci gaba da cewa "idan babu ne kiyi magana ni zan zab'a miki wanda ya dace da ke d'an mutunci idan kuma Sagir d'in kike so kiyi magana tun kan lokaci ya dad'a nisa ni zan iya samun mahaifinsa muyi magana mutumina ne ba shida matsala mutum ne mai saurin fahimta na tabbata yaronsa ma ba shida wata matsala" tunani Zarah ta shiga yi ko dai tace Sagir d'in take so ta huta wa ranta tunda gashi ta jira isowar wayar Najib amma shuru babu alamarta, ta kuma wani tunanin a ranta cewa da a bani Nauman gwara nace Sagir d'in nake so dan duk cikin masu zuwa wajena Sagir yafi mun su. Hajjiya na kallonta tayi kasak'e ganin ta kasa magana Alhaji yace "idan kuma ba zaki iya sanar damu ba sai mu kira yayanki shi ya tambaye ki" Hajjiya tace "duk hakan b'ata lokaci ne Alhaji gwara kawai ta fad'a, dan be zama lallai shima d'in ta sanar da shi ba kiyi magana kina ji ana tambayarki" Zarah ta bud'e baki zata yi magana kenan suka jiyo wani k'aramin yaro yanata kwala sallama tare cewa "wai ana Sallama da Zarah" kallon-kallo suka yi tsakanin Alhaji da Hajjiya Zarah kuwa da sauri ta d'ago kanta fuskarta cike da hawaye baki bud'e take kallon k'ofar d'akin da take jiyo sautin muryar da ake magana.___________*💅🏻B⃠ıɠ ɠąι ¢ɛ✍🏻*

YOU ARE READING
BAK'AR GUGUWA
RomanceLittafi ne me cike da abubuwan ban mamaki, al'ajabi, cin amana, da rugujewar zumunci da dai sauran su.