Chapter 24

42 6 0
                                    

*B̆ĂK̆'ĂR̆🤦🏻‍♀ĞŬĞŬW̆Ă*
🧶🧶🧶🧶🧶
       🧶🧶🧶🧶
   🧶🧶🧶
           🧶🧶
             🧶

S⃠t̾o̾r̾y̾ & W⃠r̾i̾t̾t̾e̾n̾
         *ცყ:✍🏻*
R⃠αвí'αt ѕвѕ
         *(ცıɠ ɠąι)*

*©-Aɴᴀ ᴛᴀʀᴇ Wʀɪᴛᴇʀs Assᴏᴄɪᴀᴛɪᴏɴ ✍🏻*
(wє ѧяє ṭһє ɞєśṭ ѧṃȏṅɢ ѧʟʟ wяıṭєяś)📚
https://m.facebook.com/Anatarewritersassocian/

_Aυтa na'eмa ιna yιnĸι over ιrιn ѕoѕaι d'ιnnan_

*fαδῖlα αlῖϒῠ ϻῠsα (ϻα δῖlαlα ) αshα kαrαtῠ lαfῖϒα ❤*


*P⃠age➡24*


        Juyowa Alhaji yayi dan ganin abinda yake faruwa, koda ya juyo sai yaga Zarah kwance kashirb'an a k'asa a sank'ame al'amarin da yayi matuk'ar tada masa hankali kenan ya tambayi zuciyarsa me yake shirin faruwa?, wai meya same ta? be jira samun amsar tambayarsa ba, da sauri ya koma inda Zarah take kwance, wani gumi ne me tsananin zafi ya fara karyo masa yayin da yake dubanta yana kiran sunanta da k'arfi, amma ina!bata ko motsawa balle ta amsa, Haj. Usaina banda kuka da jijjigata babu abinda take, Kiran sunanta take tare da fad'in "ki tashi dan Allah Zarah, ki tashi karki tafi ki barni Zarah" duk wannan abun da take har kawo i-yanzu babu wata alama da take nuna cewa Zarah zata mik'e, wani matsanancin tausayi ne ya ziyarci zuciyar Alhaji Kabeer be san lokacin da wata kwallah me tsananin zafi da rad'ad'i ta fito daga cikin kwayar idanuwansa ba, ya k'ara duban Hajjiya Usaina ya dubi Zarah wadda ke kwance a k'asa ya kauda kallonsa daga kansu shi kad'ai yasan irin matsanancin bak'in cikin da yake ji, addu'a kawai yake iya janyowa a zuciyarsa wadda bata wuce ta Innalillahi wa inna ilaihirraji'un ba, abinda yake ta maimaitawa kenan cikin zuciyarsa, da sauri Hajjiya ta mik'e ta d'ebo ruwa ta zuba mata amma bata tashi ba, ganin hakan yasa hankalin Alhaji ya k'ara tashi matuk'a da sauri ya mik'e ya fara neman inda ya ajjiye wayarsa da kyar ya iya gano inda take ya d'auko ya fara neman number doctor Shu'aib kira d'aya yayi masa ta shiga yayi sa'a yana kusa da wayar dan haka ya gaggauta sanar da shi irin halin da suke ciki, ya Kuma umarce shi daya tawo da dukkanin kayan da suka kamata dan yi mata gwaje-gwaje, doctor shu'aibu ya amsa da cewa "ok! gani nan isowa", Hajjiya nata kuka tana fad'in "duk kai ka janyo Alhaji inda ka bari nayi magana da duk hakan bata faru ba" taci gaba da kuka tana jijjiga Zarah, shi kuwa Alhaji kabeer tunda yasan shi ya janyo koma mene be mayar mata cikin zafi ba sai ma ya saukar da murya k'asa-k'asa "ki kwantar da hankalinki tunda yanzu likita zaizo ya dubata babu abinda zai sameta insha Allahu" wani irin kallo ta watsa masa wanda yake nuna alamar bata son jin maganarsa domin kuwa laifinsa ne tana kuka tana magana "ko menene Alhaji kaine ka jawo kai ka ja, sai da nayi k'ok'arin yi maka magana amma ka hanani yanzu ai gashi nan ka janyo zamu rasa 'yar mu sabida son zuciyarka" taci gaba da kuka bayan ta gama maganar, shi kuwa Alhaji kabeer yama rasa me yake masa dad'i ya mik'e tsaye yana shirin fucewa Hajjiya na kife a kan 'yarta tana rusa kuka, kamar Alh.Kabeer ya Kira Imran sai kuma ya fasa yayi waje ba tare da Hajjiya tasan inda ya nufa ba, ta bishi da kallo tana ci gaba da kukan da take.
________________★
  Acan gidan su Yesmin kuwa tun lokacin da Haj.Saratu suka yi magana da k'awarta Hafsatu kan maganar had'a auren Yesmin da d'an wajen Haj.Hafsatun bata sanar da mijinta ba bare kuma Yesmin d'in kanta. A yau ne ta yanke shawarar sanar da mijinta maganar da suka tattauna da k'awarta. Sai da ta bari yaci abinci ya huta sosai sannan ta fara sanar da shi maganar da suka yi da Haj.Hafsatu bata rage komai a zancenta ba ta kwashe labari tun daga farko har k'arshe ta zayyane masa, bayan da Alh. Sani ya gama saurarenta ne kuma ya ja guntun ajjiyar zuciya tare da fad'in "Ni ina ganin ba yanzu ya kamata a fara yiwa yarinyar nan maganan nan ba dan har yanzu da sauran k'uruciyarta karki manta karatu take karatun ma secondary be kamata ayi mata zancen wani saurayi yanzu ba, ya kamata a bari har ta kammala karatun ta na secondary tukunna sai ayi mata magana idan ta amince shikkenan in kuma bata amince ba sai mu kyaleta ta kawo mana wanda take so, amma yanzu ina ita Ina wani zancen saurayi" yana gama fad'ar hakan ya gyara kishingid'ar da yayi da pillow yayin da Haj.Saratu ta bishi da kallo yana magana har sai da yazo dai-dai nan a zancensa sannan tace "Amma Alhaji baka ganin a yanzu ta san komai na soyayya karfa ta fara soyayya da wani can daban lokacin da muke k'ok'arin sanar mata da wannan d'in lokaci kuma ya ruga da ya k'ure, Haj.Hafsatu ba zata ji dad'i ba zata yi tunanin muna sane hakan ta faru dan muna gudun had'a zuri'a da ita, kasan Alhaji in kuka taso da mutum tun daga k'uruciyarku har girmanku baku tab'a samun sab'ani ba kuna tare abunda yafi kawo samun sab'ani a irin wa d'annan matsalolin ne mutum ba zai tab'a tunanin wanne irin hanyoyi kabi dan ganin yaron ya amince ba, naka laifin zai gani, Ni ina ganin abinda ya kamata mu sanar mata tun yanzu idan tana sonsa shikkenan zance ya wuce sai ya jira har lokacin da zata kammala karatun nata sannan a fara zancen aure" Alhaji Sani wanda ya zuba mata kallo tana magana yace "ba zaki gane ba, yanzu da k'uruciyarta bata san menene so ba balle ma tasan tana sonsa ko bata sansa,koda kin mata maganar zata d'auki zancen wasa sabida bata san komai ba" guntun dariya Haj.Saratu ta saki tare da fad'in "Alhaji kenan tunanin zamanin baya kake amma banda wannan zamanin domin kuwa a wannan zamanin duk yarinyar data shiga makarantar  secondary ta san komai wadda ma bata shiga ba zata sani sabida rayuwar yanzu data baya akwai banbanci, musamman wannan wayoyin hannun da suka shigo ko ita ba tada ita k'awarta nada ita balle itan ma tana da waya". Dariya Alh.sani yayi  ba tare daya shirya yinta ba yace "a'a babu wata soyayya da zata sani balle tayi yarinya k'arama ace tana soyayya? Yaushe ta shiga secondary d'in bare har ta san soyayya?, Ni bana son rugujewar karatunta" Sake sakin guntuwar dariya Haj.Saratu tayi tace "wallahi ka bani dariya Alhaji yaran yanzu ai sun san komai wa 'yanda ma basu kaita ba sun san zancen saurayi bare kuma ita wadda take secondary school, har yanzu ka kasa fahimta ta, a haka ne zaka runk'a ganinta yarinya k'arama wadda bata san komai ba amma hakan ba wai yana nuna cewar bata san komai d'in bane, ya kamata Alhaji ka bani dama na fara tuntub'arta naji in har ta amince da shi d'in" sai da Alh.Sani yayi d'an yi shuru na wasu 'yan dak'ik'u kafin yace "naga alama dai ba kya son ran k'awarki ya b'aci shikkenan ki tambayeta d'in, amma zaki dawo ki fad'a mun abinda na fad'a miki" dariya Haj.Saratu tayi "Alhaji ai wanda kuke tare ba zaka so ganin b'acin ransa ba in har ba hakan muk'addari bane amma tabbas bana son abinda zai yanke mana alak'ar mu da ita" ta mik'e tana shirin fita kenan Alhaji Sani yace "Ina kuma kike shirin tafiya?" Haj.Saratu tayi murmushi "zanje na tambayeta mana" "haka da gaggawa? Saurin me kike? ke da kuke tare kullum, a'a ki kyale ta zuwa gobe in Allah ya kaimu sai kije ki tambayeta yanzu ai dare ne" Haj.Saratu ta kuma murmushi yayin data dawo ta zauna tace "shikkenan Allah ya kaimu goben lafiya da yau da goben ai duk d'aya ne gurin ubangiji" Alh.Sani yace "haka ne sai ki k'arashen d'aya labarin da kika fara bani" daga nan dai suka shiga wata hirar.
   Alh.Sani da matarsa Haj.Saratu suna zamansu cikin rufin asiri, tunda suke ba'a tab'a jin kansu ba, suna zaune lafiya cikin farin ciki da walwala duk da cewa ba wasu manya ne sosai wanda suka manyanta ba amma  komai nasu da suke sai ka d'auka dattijai ne, Alh.Sani mutumin kirkine wanda be wuce shekara arba'in da biyar ba kamar yadda itama Haj.Saratu take da shekaru talatin da bakwai itama kuma mutuniyar kirkice dan ba'a tab'a jinta a unguwar da suke ba, Alh.Sani ma'aikacin wani company ne na mayukan shafawa wanda yayi fuce ya kuma shahara a fad'in duniya, suna zaune cikin wadata da arzik'i gidansu me kyau matsakaici ga duk wanda ya gani yasan suna jin dad'insu, babu abinda Yesmin ta nema ta rasa a wajensu shiyasa ma ta zama 'yar lele take shagwab'a san ranta, basu tab'a nuna mata wani banbanci ba ko kyara, sun d'auketa tamkar su suka haifeta wannan yasa suke gudun duk wani b'acin ranta.
_________________★
    Can kuwa Alh.Kabeer be jima da futa ba ya shigo tare da doctor Shu'aib ganin shigowarsu yasa Hajjiya Usaina ta d'aga kanta daga kan Zarah data kifa tana kuka, ta zama kamar wata zararriya sai surutai take, doctor Shu'aib yace "Relax your mind Hajjiya, I will check it now,  insha'ah Allah ba abinda kike tunani bane". Sai a sannan Haj.Usaina ta d'an sassauta kukanta, doctor shu'aib ya fara fudda kayan aikinsa, Alh.Kabeer be iya cewa komai ba yaja ya tsaya yayin da doctor Shu'aib yake sak'ala stethoscope a kunne dan yi mata wasu gwaje-gwajen, tunda ya fara idanuwan Haj.Usaina na kansa tana lura da yanayin fuskarsa yadda take sauyawa a kowanne gwaji da yayi, daga bisani kuma taga ya tsaya cak! yana kallon Zarah kamar me wani nazari duk wannan abun da yake Haj.Usaina bata d'auke kallonta daga kansa ba ganin hakan yasa hankali ta ya k'ara tashi fiye dana farko cikin d'imaucewa ta sake fashewa da wani matsanancin kuka tare da fad'in "likita ta mutu ko? Ka fad'a mun ta mutu ko? Dan Allah ka fad'an" bece da ita komai ba tana ci gaba da kuka Alh.Kabeer ne ya daure yayi magana "Kinga ya isa ki jira yayi magana" har yanzu doctor Shu'aib bece dasu komai ba, Zarah dai babu alamar motsinta shi kansa doctor Shu'aib d'in be san me zaice musu ba, a hankali ya kau da kallonsa daga kan Zarah yayin da ya bud'e baki yana shirin ce musu_____________





*💅🏻B⃠ıɠ ɠąι ¢ɛ✍🏻*

BAK'AR GUGUWAWhere stories live. Discover now