Chapter 20

38 3 1
                                    

*B̆ĂK̆'ĂR̆🤦🏻‍♀ĞŬĞŬW̆Ă*
🧶🧶🧶🧶🧶
       🧶🧶🧶🧶
   🧶🧶🧶
           🧶🧶
             🧶

S⃠t̾o̾r̾y̾ & W⃠r̾i̾t̾t̾e̾n̾
         *ცყ:✍🏻*
R⃠αвí'αt ѕвѕ
         *(ცıɠ ɠąι)*

*©-Aɴᴀ ᴛᴀʀᴇ Wʀɪᴛᴇʀs Assᴏᴄɪᴀᴛɪᴏɴ ✍🏻*
(wє ѧяє ṭһє ɞєśṭ ѧṃȏṅɢ ѧʟʟ wяıṭєяś)📚
https://mobile.facebook.com/Anatarewritersassocian/

*fαδῖlα αlῖϒῠ ϻῠsα (ϻα δῖlαlα ) αshα kαrαtῠ lαfῖϒα ❤*


*P⃠age➡20*


     "Me kake so ka fad'an ya Nauman? Jamila ba bak'uwa bace ko menene zaka iya fad'a a gabanta" murmushi yayi tare da fad'in "wannan magana ce tsakanin yaya da k'anwarsa, ina so kiyi hak'uri ki fara rakata idan kin dawo sai mu tattauna kan maganar" ranta a b'ace take kallonsa jamila dake tsaye tana saurararsu murmushi kawai tayi tare da cewa "ba sai kin raka ni ba, ki tsaya ki saurare shi qawata ni zan tafi" tayi gaba, da sauri Zarah ta bita a baya yayin da zuciyarta take cike da damuwa k'irjinta nata bugawa dan tsoron abinda zai ce yazo. Ganin hakan yasa jamila fad'a mata cewa "ki danne zuciyarki ko me zai sanar da ke ki tsaya ki saurare shi kiyi kamar dai yadda na baki shawara d'azu, in kikai hakan zai fi." godiya zarah tayi mata ganin yadda take k'ok'arin kyautata mata, sai da suka shafe tsawo mintuna suna dad'a tattaunawa a waje sannan Jamila ta tafi. Duk dad'ewar da suka yi Nauman na tsaye yana jiran k'arasowar ta, mamaki ne ya kamata ganin yadda ya b'ata lokacinsa a banza d'aura fuska tayi yayin da take k'arasawa inda yake tsaye tana isa tace "to gani ya Nauman me kake so ka fad'an" ji yayi ya kasa maganar ya bita da kallo kawai ta kuma magana "ko ka fasa fad'an maganar da kace zaka fad'an?" har yanzu shuru yayi ganin ba shida ta cewa yasa ta juya tare da fad'in "bari na tafi tunda ba kada abin fad'a" da sauri yace "karki tafi Zarah haba k'anwata" murmushin takaici tayi musamman yadda taji ya kirata da k'anwarsa ta tsaya tana kallonsa cike da rashin fahimtar inda ya dosa "ina jinka sauri nake" a hankali ya runk'a magana ba tare daya kalli kwayar idonta ba "daman ina so na fad'a miki cewa...." ta tsure shi da kallo tana suararensa "ka fad'a mini me?" ya kuma maimaitawa cikin muryarsa ta in-ina "daman ina so na fad'a miki cewa ina sonki" bakin nasa ta bi da kallo yayin da yake furta kalmar sa'annan tayi murmushin takaici "hmm kana sona?" shima murmushi yayi na farin ciki tare da rausaya kai "kwarai" sai da tayi ajjiyar zuciya me k'arfi kafin tace "sai dai kuma ka makaro ya Nauman dan wani tuni ya ruga ka na ruga dana mallakawa mamallakin zuciyar zuciyarsa sai dai kuma ka nemo ta wata amma banda tawa" dai-dai nan ta fara wani tunanin na daban jikinta ne yayi sanyi bayan data gama furta kalmomin ba komai ta fara tunani ba sai inda zata ga Najeeb a guje ta k'arasa gida ta bar shi nan tsaye baki bud'e yana mamakin irin maganar data furta masa shikkenan tana nufin ya rasa ta? Abune wanda ba zai tab'a sak'uwa ba, zuciyarsa ce take raya masa hakan, ya d'aure fuska ya futa daga gidan. Zarah na shiga bata kalli inda mommy take zaune ba, kai tsaye d'akinta ta wuce tana kuka, Hajjiya Usaina dake zaune tana jiran k'arasowar Abban Zarah ta ganta ta shigo tana kuka ganin Zarah na kuka yasa ta bita da kallo tare da fad'in "lafiya?" wucewa Zarah tayi ba tare data tsaya ba ta nufi d'akinta, Hajjiya Usaina ta gama lura da irin halin da 'yarta take ciki na damuwa sai dai kuma ta kasa yi mata bayanin komai ta mik'e da nufi shiga d'akin Zarah kenan ta ji yo sallamar Abban Zarah ya dawo fasa shiga tayi ta isa inda yake ta karb'i jakar hannunsa tare da yi masa sannu da zuwa suka k'arasa sashin sa.
__________________★
   Haj.Saratu na tare da k'awarta Hajiya Hafsatu suna hira a falo ta mik'e ta nufi kitchen dan duba girkin data d'ora shigarta keda wuya ta jiyo muryar Yesmin na rafka sallama da sauri ta fito daga kitchen cike da mamakin dawowarta Yesmin ta shigo hannunta ruk'e da jakar kayanta, mamaki ya k'ara kama Hajjiya Saratu tace "lafiya? ya naga kin dawo ke da kika ce kwana biyu zaki? meya faru kika dawo?" ala dole Yesmin ta saki ranta dan kar Hajjiya Saratu ta gane damuwar dake fuskarta tace "fasawa nayi sabida munyi waya da fadila tace zata zo, naga ba dad'i tazo taga bana nan gari ya gari shiyasa na dawo" sai a lokacin zuciyar Hajjiya tayi sanyi jin yadda tayi mata bayani tace "kinyi tunani sosai amma dai ba da kanki kika tawo ba ko?" dariyar yak'e Yesmin ta kuma yi sannan tace "ba ni kad'ai na tawo ba Isah driver na yiwa waya yaje ya d'auken" sosai Hajjiya tayi farin ciki tace "shiga ciki ki ajjiye kayan naki nima yanzu zan shigo" Safara'u me aiki ce ta tawo da sauri ta karb'i jakar hannun Yesmin suka k'arasa ciki. Tana shiga taci karo da Hajjiya Hafsatu zaune ta k'urawa TV'n dake falon idanu, durk'usawa Yesmin tayi har k'asa ta gaida ita fuskarta cike da walwala ta amsa daga nan Yesmin ta wuce d'aki, Hajjiya ce ta shigo ta nemi waje ta zauna Haj.Hafsatu tace "sannu da aiki, kina k'ok'ari ga 'yar aiki amma kike shiga kitchen da kanki? Shiyasa fa 'yan aikin suke sangarcewa suna samun damammaki da yawa, nifa kin ganni nan? babu wata 'yar aiki da zan d'auko na barta ta huta ni na aikatu" duk wannan bayanin da take Hajjiya Saratu murmushi take tana saurararta har sai da ta zo dai-dai nan a zancenta sannan tace "Hmm.. Ba wai haka bane bana barinta tayi masa girki idan iya namu ne sai tayi amma na mijina bana bari tayi masa komai da kaina nake masa shi kansa baya yarda yaci girkin da ba ni na girka ba" dariya Hajjiya Hafsatu tayi "shiyasa ni ba ruwana da wata 'yar aiki ni da kaina ya wadatar ba sai na janyowa kaina abinda yafi k'arfi na ba, zancen kuma baya son cin duk girkin da ba naki ba hhh...bar maza Hajjiya Saratu ba'a yabonsu dan muddin kika yabi namiji yanzu yasa kiji kunya dan sai su baki mamakin da baki tab'a tsammani ba, nifa ko ba zan tab'a yadda da d'ad'in bakin d'a namiji ba yana fad'an ta ke wucewa ta d'aya kunnen zaki yi mamakin namijin da zai ce shi baya son abu kaza sai na matarsa. a waje in kika ga yadda yake sai kin ruk'e baki ni ai naga darasi irinsu masu cika bakin sunfi kowa tsiya ke dai kawai ki iya takun ki" shuru Hajjiya Saratu tayi tana sauraranta har ta gama sannan tace "Allah ko?" tace   "sosai ma ba ga sa'adatu ba mijinta ba irin yabonta da baya yi yana cewa har abada ba zai tab'ai mata kishiya ba kullum yana nan-nan da ita duk inda ta shiga tana cika bakin irin son da yake mata da kuma cewar da yayi ba shi ba yi mata kishiya k'arshe sai ranar d'aurin aurensa da aka taru za'a d'unguma gidan su amaryar taji labari kinga ai namiji ba abin yarda bane" mamaki ne ya kama Hajjiya Saratu tace "maganarki da k'amshin gaskiya ni kaina wani lokacin in na zauna ina nazari sai wata zuciyar tace mun ki kyale kawai insha Allahu ba zaki samu wata matsala ba sai kiga na ware" Hajjiya Hafsatu tace "sai dai addu'a zamu runk'a taya su da shi kin san ance addu'a takobin mumuni, hmm naga Yesmin ta girma yarinya ta zama budurwa yanzu tana wanne ajji ne?" "yanzu tana ss 1 bata dad'e da shiga ajin ba, Yesmin nada garin jiki girman kawai ne duk babu wani shekaru" "duk da haka in akai mata aure tsaf! zata zauna" murmushi Hajjiya Saratu tayi " aure kuma? Ai tayi yarinta da yawa"  dariya Hajjiya Hafsatu tayi "Me zai hana ta zauna? ake yiwa 'yan shekara sha biyu ma bare ita?" fidda idanu Hajjiya Saratu tayi tare da fad'in "ko dai baki ganta sosai ba ne?" nan ta kwalawa Yesmin kira dai-dai lokacin da Yesmin take gurshek'an kuka  jiyo kiran da ake mata yasa ta tsaida kukan da take tare da share hawayen dake kwaranyowa daga idanuwa ta zuwa kuncinta tunda ta shiga ta d'auki mintuna tana kuka tun lokacin data shiga d'akin ta fad'a gado ta fara tuna abubuwan da suka faru tsakanin Ya Imran da kuma Jamila taji ta tsane jamila bata son lokacin data fara zubda hawaye masu zafi daga cikin idanuwanta ba har ta ara gurshek'an kuka. Sai da ta goge fuskarta tas dan kar a gane tayi kuka tukkunna ta futa ba tare data kalle su ba  ta durk'usa k'asa "gani" binta da kalli Hajjiya Hafsatu tayi sannan tayi dariya tace "masha'Allah yarinya ta girma wallahi ta girma ta isa aure" gaban Yesmin ne ya yanke ya fad'i cikin zuciyarta tace "lafiya to?" hajjiya na kallonta tace "ya naga kamar idonki yayi ja?" da sauri Yesmin tace "na fara bacci ne" Hajjiya tace "ok shiyasa, tashi ki je kiyi kwanciyarki" Yesmin ta mik'e ta koma Hajjiya saratu tace "yanzu kin yarda da ni?" Hafsatu tace "hmm na fad'a miki yarinya ta girma ta isah aure" dariya Hajjiya saratu tayi, Hajjiya hafsatu ce ta kuma magana "nace me zai hana a k'ara dank'on zumunci?" cikin rashin fahimta Hajjiya Saratu ta ce "dank'on zumunci a ina?" dariya Hajjiya Hafsatu ta tuntsire da shi "ina nufin Salim da Yesmin me zai hana mu k'ulla aure tsakaninsu kinga zumuncin mu sai ya dad'a k'ulluwa fiye da yanzu" shuru Hajjiya saratu ta d'anyi bayan wasu 'yan dak'ik'u tace "kuma fa kin kawo shawara, amma kina ganin hakan ba zai iya kawo mana wata matsalarba?" dariya Hajjiya Hafsatu ta sake yi tare da fad'in "matsala kuma? Insha Allahu babu wata matsala" murmushi Hajjiya Saratu tayi yayin da take cewa "Allah ya yarda kinga kuwa da nafi kowa farin ciki wanda ka sani ai yafi wanda baka sani ba, in ya dawo zamu tattauna da shi akan maganar" haka dai suka ci gaba da hira yayin da ita kuma Yesmin take can kwance cikin d'aki tana ci gaba da gurshek'an kuka Kan lamuran Ya Imran.
   Yesmin bata tab'a sanin Ya Imran yayanta ne na jini ba kuma babu wanda ya tab'a fad'a mata hakan, hasalima bata san Hajjiya Saratu ba ita ta haifeta ba duk ganin da takewa Hajjiya Usaina matsayin yar mahaifiyarta take ba wai wadda ta haifeta da cikinta ba, haka ma Zarah da Imran tunaninta duk 'ya'yan yar babarta ne bata tab'a sanin 'yan uwanta ne na jini ba. Tun tasowar Yesmin babu namijin daya tab'a kwanta mata a iya shekarunta face Ya Imran shi kad'aine wanda zuciyarta take muradi take kuma farin cikin gani, tun bayan daya tafi bautar k'asar take kewarsa farin cikinta be wuce na ya dawo ta ganshi ba, a bacci ko a farke shi kad'ai take iya gani, tunaninta ma shi ne, ko a makaranta in suna hira da k'awayenta labarin Imran kawai take basu ta ruga data gama kamuwa da soyayyarsa, ta kuma gama tsara rayuwarta da shi, haka zuwan da take gidan su tana zuwane dan kawai taga Ya Imran shiyasa ma bayan daya tafi suka daina ganinta akai-akai sai a yanzu daya dawo, sai dai kuma dawowar tasa be zame mata farin ciki ba face b'acin rai, musamman yadda taga ya kamu da son wata daban ba ita ba wannan shi ne babban dalilin daya b'ata mata rai har ya sata kuka wanda kuma shi yasa ta kasa daurewa har tayi tawowarta gida sai dai duk da cewa ta dawo gida hakan be sa zuciyarta ta sassauta daga irin rad'ad'in daya addabeta ba, ta kasa tsaida zuciyarta waje d'aya wajen sak'a mata wasu abubuwan da bata tunanin faruwarsu, haka ta ci gaba da tunani gami da sak'e-sak'e had'i da tunane-tunane da gurshek'an kuka wanda ta kasa tsayarwa, ta kai har dare tana cikin wannan hali ba tare da kowa ya sani ba.
_________________★
    Shi kuwa Nauman a fusace ya k'arasa gida be tsaya ko ina ba sai d'akin mahaifiyarsa yayi tsaye a gabanta yayin da take kwance kan sallaya, sai nunfarfashi yake kamar wanda aka doka ko yake shirin kai duka, sai cika yake yana batsewa da sauri safiya ta mik'e zaune daga kwanciyar da take ta dube shi sosai taga ba kamar yadda ya futa ba cikin mamaki tace "lafiya na ganka cikin damuwa? Meya faru? Da k'yar yake magana saida ta tambye shi sau uku be ce da ita komai ba nan ta gane tabbas yana cikin tsananin damuwa wanda ba zai iya furtawa ba, kwantar da murya tayi ta fara lallashinsa "wa ya tab'a mun kai ne? Fad'a mun d'ana na kaina kasan bana son ganin duk wata damuwarka zauna nan ka fad'an" tayi masa nuni da kusa da ita,yana tsaye yana kallonta ba tare da yace da ita komai ba ta kuma magana "zauna mana" da kyar ya iya zaunawa ji yake kamar ya fashe da kuka ta kuma magana me ya faru? Allah yasa ba waccen yarinyar ce ta b'ata maka rai ba" kallonta yayi cikin fushi yace "itace mama" nan take itama ta b'ata rai "me tayi maka" ransa a b'ace yake magana "na fad'a mata tace wani ya ruga ni ita bata so na" a fusace Safiya tace "ba ta me?" yace "wai bata so na, tana da wanda take so". cikin fushi Safiya ta fara fad'a "bata isa ba tayi kad'an wallahi babu wanda zata aura sama da kai, ka kwantar da hankalinka, akan wannan ne ma zaka wani damu? Ka daina damuwa zanje na samu mahaifin nata karka manta sama nake da shi dole ya bi duk kanin umarni da zan gindaya masa kuma ba zata auri kowa ba face kai, har zata b'ata maka rai ka zauna kana damuwa? wannan ai abu ne me sauk'i, yanzu ma dan dare yayi da a yanzun nan zanje na samu mahaifin nata amma ba komai Allah ya kaimu gobe zanje na same shi a cikin satin nan zaka ji maganar auren ku kai dai kawai ka fara k'ok'arin gyara inda zaku zauna cikin sati biyu za'ayi komai a gama" ta saki wata muguwar dariya yayin da shi kuma ya fara murmushi yanzu ne zuciyarsa tayi sanyi ya yarda da zancen mahifiyarsa dan ya ruga da ya san halinta sakin fuskarsa yayi ya ci gaba da walwala suka ci gaba da hira har ya koma d'akinsa.
_________________★
    Bayan Alh.Kabeer  ya gama kintsawa yasa aka kira wo masa Imran suka gaisa da juna, sosai yayi farin ciki da dawowarsa. Sai da suka shafe tsawon lokaci suna tattaunawa Hajjiya Usaina na zaune gefe guda tana saurarensu wata maganar ta saka baki wata kuma tayi shuru, sun juma suna hira har sai da abokan Imran suka yi masa waya sannan ya tafi sashinsa dan tararsu. Alhaji ne yayi magana bayan da Imran ya futa "me yasa yarinyar nan bana ganinta a falo yanzu? saina shigo bata san na shigo ba bana jin d'uriyarta ko dai wani wajen kike barinta tana tafiya idan bana nan?" "ko kad'an Alhaji kasan ba zan tab'a barinta ta futa ko ina ba tare dana sanar da kai ba, iya k'ok'arina ina yi wajen bata tarbiya ni kaina ai ba zanso ace yau yarinya ta tarbiyyarta ta lalace ba ina saka ido a dukkanin lamuranta sai dai..." tayi shuru Alhaji yace "sai dai me" kamar Hajjiya ta fad'a masa abinda ta kula game da Zarah irin yanayin da take cikin sai wata zuciyar ta hanata sabida tasan halinsa ba lallai ya bita ta lallami ba tace "sai dai kuma ba mamaki tana tare da k'awarta jamila ne dan tun d'azu suna cikin d'aki ko ta tafi kuma yanzu? ban sani ba" Alhaji Kabeer yace "Kinsan kiwon mutum ake ba dabba ba ya kamata kici gaba da kula da shige da fucenta da kuma su k'awayen da suke zuwa wajenta dan yanzu zamanin sai addy'a kana yiwa yaranka tarbiyya a gida k'awaye na zuwa har gida suna b'ata musu tarbiyya, amana ce Allah ya bamu" Hajjiya tace "haka ne" sai yanzu ya tuno da sak'on daya bayar yace da Hajjiya usaina "kin kuwa yi mata maganar,kin tambayeta?" Hajjiya yace "A'a" "ya kamata kiyi mata magana yanzu sabida bana son abinda zai kawon b'acin rai a runk'a magana babu dad'i", Hajjiya tace hakane bari naje na same ta naji ta bakin nata" Fucewa tayi ta k'arasa zuwa d'akin Zarah ta kwankwasa k'ofar, Zarah na jiyowa tayi saurin goge idonta sannan ta bud'e k'ofar Hajjiya ta kalleta sosai idanuwanta sunyi jawur kamar gauta cikin mamaki tace "lafiya naga idanuwanki sunyi ja?" Zarah ta saki fuskarta tare da murmushi "ba komai mommy abu ne ya fad'an idon kuma na cire" tab'e baki Hajjiya tayi kad'an ta sami bakin gado ta zauna  "Ina so za muyi wata magana dake dan haka kizo ki zauna ki bani hankalinki nan" gaban Zarah ne ya yanke ya fad'i ta runk'a bin mommy da kallo yayin da take k'ok'arin zaunawa sai da ta zauna ta nutsu sannan Hajjiya tace "a kullum ina lura da ke kina cikin damuwa amma in na tambayeki kina b'oye mun, ba kida wadda ta fini da zaki fad'awa damuwarki, babu sama da ni a wajenki, to ina so a yanzu ki sanar da ni zuciyarki domin kuwa akwai Alhaji D'ahiru yazo nemawa yaronsa Sagiru aurenki" gaban Zarah ne ya yanke ya fad'i tun kan Hajjiya ta k'arasa maganar da take ta fara tunanin waye sagiru? Hajjiya taci gaba da magana "dan haka ina so naji wa kike so  shi Sagir d'in ko kuwa yayan naki Nauman?" gaban Zarah ya sake fad'uwa Sagir! kuma? Nan take ta tuna sunan tababs shi ne saurayin daya janyo samun sab'aninta da Najib zuciyarta ta buga da k'arfi ganin Zarah tayi shuru kamar tana tunani Hajjiya ta kuma cewa "duk wanda kike so cikin su ki fad'a zanje na sanarwa mahaifinki yanzu" da sauri Zarah ta d'ago kai ta kalli mommy tace____________

  




*💅🏻B⃠ıɠ ɠąι ¢ɛ✍🏻*

BAK'AR GUGUWAWhere stories live. Discover now