12

337 14 0
                                    

*🤦‍♀️🤦‍♀️ MIJIN BABATA NE🤦‍♀️🤦‍♀️*


*ZAFAFA WRITTERS FORUM....📚✍🏻*

               *Z.W.F.🏝️*

*Tsarawa da rubutawa*
*💞UMMU JA'AFAR💞*

       *Marubuciyar*

*Ƙawar ƴata ce*
*Umarnin saurayi*
*Ƙawaye ne sanadi*
*Auren biyayya*
*A chating muka haɗu*
                 And now
    *Mijin Babata ne*


*_INA MIƘA GAISUWA GAREKU ƳAN UWA KUMA MASOYAYA KUMA MASOYAYAN WANNAN LITTAFE NA MIJIN BABATA NE, COMMENT ƊINKU NA ƘARA SANI FARIN CIKI FIYE DA TUNANINKU, INA GODIYA SOSAI IRIN YADDA KUKA ƘARƁI WANNAN LITTAFI, ALLAH YA BAMU IKON KAMMALASHI LAFIYA YA_🤗*


*SHAFI NA 12*

Ƙara shigar da ita jikinta Mumy tayi haɗi dayi mata tofi, tana rarrashinta, kayan jikinta ta mayar mata haɗi da ƙara rarrashinta itako sai surutai take tana faɗin Mumy mijinki shine kwaetona ki taimake ni ki  rabani dashi!.

Tana cikin faɗar haka shiko dai-dai lokacin da yashigo ɗaki haɗi da rai kamar bai taɓa dariya ba, kallon mumy yayi irin kallon nan na tsana kana yace,

" Naji sharin da ƴarki take kullamin, to bari kiji idan gidan ubanta ne bata son na zauna ba sai ta naɗamin sharri ba, wallahi zan barshi har abada, ke koke zan iya rabuwa dake da tazo ta naɗamin sharri, dan haka yanzu basai anjima ba zan bar gidannan wallahi bazan kwana acikinshi ba, kuma da safe zan rubata ta karda akawo miki sai ƴarki taje ta tada ubanta cikin ƙabari yazo kuci gaba da zaman aure tunda ta nunawa duniya kishi take taya ubanta".
Yana faɗar haka yayi cikin ɗaki ya fara haɗa kayanshi.

Jikin Mumy na rawa ta ture Hansa'u daga cikin ta ta shiga bedroom  cikin tashin hankali.

Riƙishi tayi haɗi da sanya wani marayi kuka tana faɗin,

" Dan Allah kayi haƙuri wallahi ina tunanin mafarki ne take dan har yanzu idonta rufe suke bata buɗe, dan Allah ka tausayamin wallahi ina matoƙar sonka".
Ta kai ƙarshin zanci tana kuka haɗi da durƙusawa ƙasa ta riƙi ƙafarshi.

" Nizata nunawa bariki sai tagama iskancin ta waje maza sun gama lalubarta tazo tana cewa mafarki ne take wallahi banyarda cewa mafarki bane, tabbas akwai wanda ke shigowa gidannan yana anfani da ita, da zaran sunji mutsina ko naki sai ta koma ta kwanta tana ƙara tana cewa ƙarto yazo mata, dan haka datayi ciki ace nine gwara na bar gidan nan tunda na lura ke tsoronta kike ji ".
Ya kai ƙarshin maganar rai haɗe kamar abinda ya baɗa da gaske ne.

Wata ƙara mumy ta sanya lokaci ɗaya ta tashi da gudu ta isa falo wajan da Hansa'u take zaune tana kuka saboda taji duk abunda yake cewa  Mumy.

Mumy da zuwanta wajan Hansa'u bata tsaya komai ba tasa hannu tashaƙo wuyan Hansa'u haɗi da faɗin,

" Ni zaki cin amana kici amanar mijina, to wallahi kinyi ƙarya, ashe kice ke kawo ƙato yakwana dake dan kina shegiyar yarinya ki ce wannan bawun Allah ne, to bari kiji ƙarshin zamanki gidannan ya ƙare, dan wallahi da aurena ya mutu gwara nakasheki, dan haka ba sai gari ya waye ba, ki tashi kihaɗa duk wani abu wanda yakasance naki ne ki barmin gidana dan ubanki ko ƙwandala tashi babu  lokacin da zan sayin wannan gida dan haka yau kinji gida nawa ne ni kaɗai, dan haka kitashi ki kama hanyar zuwa gidan ubanki, dan ko wace ƴar tana tutiya ne da gidan ubanta ba na uwa ba".

Tana gama faɗar haka ta tukuɗa Hansa'u waje, Mumy kamar wata mahaukwaciya sabon kamu , haka taje ta ɗauko duk kayan Hansa'u tajefo mata su waja kana ta roƙon Hannun Hansa'u ta fitar da ita waje sannan ta maida ƙofar gida ta rufe.

Wajan mijinta ta dawo wanda abinda tayi ma Hansa'u ba ƙaɗan yayi mishi daɗi ba, amma bai wani nuna ba yaci gaba da haɗi fuska waishi a dole fushi yakeyi.

Rugumeshi mumy tayi tana bashi haƙuri akan dan Allah yaci gaba da zama tunda yanzu Hansa'u ta koma wajan kakarta Hajita Sa'a, da ƙar Mumy ta samu ya yarda yace ya haƙura, saboda daɗin da yaji wannan dare kwana yayi kanta yana mata abinda yasan tana so, lokaci ɗaya Mumy ta manta da abinda ya faru bare wata Hansa'u.

Hansa'u kallon Mumy kawai takeyi har tafitar da ita waje kuma ko waje cikin dare, wasu Hawaye ta shafe a fuskarta dai-dai wannan lokaci wasu samari suka ƙarasu  wajanta sai hura sigari sukeyi, suna wata tafiya da alamu cikin maye suke.

            Hauwa ba ita ta koma gida ba sai dare, bayan ta shiga gida kai tsaye ɗakinta tashiga tayi wanka tana shirin bacci sai ga Innarta tashigo riƙi da fitila a hannunta tace,

" Hauwa tun ɗazo sai nemanki muke, wai ina kike zuwa ne?".

" Kai Inna wallahi kin fiye tambaya, ai ni ba yarinya bace da zaki tsareni da tambaya".

" Allah ya shiryeki Hauwa, daman gaya miki ne zanyi ɗazo aka aiko akace agaya miki Ubanki na can kwance babu lafiya kuma babu mai kula dashi shine nace bari nagaya miki".

Tsaki Hauwa tayi tace,

" To ni Inna mi zan mishi? ko lokacin da ina ƙarama ya taɓa taimakona? ko yasani makaranta, ko ya taɓa bani wani taimako wanda zai nuna cewa shi ubanane?  dan haka ki rabu dani, can ƴan uwanshi da uwarshi su kula dashi".

Inna kallon Hauwa tayi haɗi da haɗi wani baƙin ciki wanda ya tokare mata wuya tace,

" Indai kin amice nice na haifeki, to gobe ina so ki tafi ki ganshi ko bai taɓa miki komai ba shine yayi sanadin zuwanki duniya, kuma wallahi kar nasaki jin irin wannan maganar ta fito daga bakinki".

Inna nagama faɗar haka tayi tafiyarta saboda zuciyar ta dataji zata fara mata cuyo.

Tsaki Hauwa tayi kana tace,

" Bai taɓa kullamiki komai ba amma kice  sai nabishi, bawani nabishi na kula har yanzu sonshi takeyi".

Tsaki taja haɗi da jawo abin rufa tayi kwanciyar ta......



*Comment and share*


*SUMMY M NA'IGE✍️*

MIJIN BABATA NEWhere stories live. Discover now