*JIDDO*
(Gidan Aurena)_Story by_
*MAMAN NABEELA*
( _SIHIBAR {D. A. W. A_}(_TEAM JAJURTATU 6_)
*BAYAN RAI (KHADIJA ISHAQ)*
*JIDDO GIDAN AURENA(MAMAN NABEELA)*
*JINANE(ZAITUN MAMAN FAUZAN)*
*IN BA KAI(OUM AFREEN)*
*SAIFUL ISLAM(OUM AMRA)*
*NURHAAN(SHUATY)**DASHEN ALLAH WRITERS ASSOCIATION*
*HAƊAKA PALACE GROUP*
*TALLA! TALLA!! TALLA!!!*
*MAMAN NABEELA DATA SERVECES*
_We buy Data from the afoderble price._
*MTN, AIRTEL, GLO, 9MOBILE;*
*500 MB➡️150*
*1.GB ➡️300*
*2.GB➡️600*
*3.GB➡️900*
*4.GB➡️1200*
*5.GB➡️1500**MTN DATA BLNC:*461*4# or *310#*
*AIRTEL https://chat.whatsapp.com/Cl5xn2qD4wF24JErear0iF*Follow my whatsapp channel on:* https://whatsapp.com/channel/0029VaEXHzuBPzjTpTqZm13y: *228#*
_Sannan da akwaI airtime na;MTN, AIRTEL, GLO, 9MOBILE_'''7042808467 Firdausi Rabi'u Abubakar Opay bank
Or 0203632498 Firdausi Rabiu Abubakar Union bank
Sai shedar biya ta 07042808467'''*PAGE* 2️⃣4️⃣
“Kasa a ranka ya bar gidan, dan a yau ba sai gobe ba Farzillo zata ziyar ce shi ya koma inda ya fito hhhhh.” Shugaban nasu yayi maganar yana ƙara ke ce wa da dariya.
Cike da farin ciki ya kuma gurfana guwiwoyinsa yana ce wa“godiya na ke shugaba” Suwiɗi yayi maganar cike da farin ciki yana ci gaba da karanto wasu dalasiman tsafinsu, take madubin ya koma babu komai cikinsa kamar sanda ya ɗauko shi.
A ranar kuwa Jazuli ya bar gidan da tawagarsa.
Dariya Suwiɗi ya kuma kecewa da ita tuna yadda Jazuli ya na ce kan ya dawo kenan“ɗan jakal uba ko zaka dawo gidan nan ai sai amfaninka ya taso” Suwiɗi ya kuma maganar kamar zarare yana dariya shi ɗaya a cikin ɗaki.
Shuuuu yaji abu ya gilma ta gefen kunen shi take dariyar da yake ta tsaya ya hau waige-waige ganin babu komai yasa ya ci gaba da murmushi yana ƙisima yadda da an shiga kotu, aka ce ana buƙatar ya saki JIDDO zai ce ba zai saketa ba.
Da alƙali ya ce sai ya saketa zai laftu iyayen kuɗi ya ce sai an bashi kuɗin da zai auri wata sannan ya saketa.Dariya ya kuma shiƙewa da ita yana ce wa a fili “Sai ni Suwiɗi shegen kai na, da alama shekarar bana da nasarar cimma muradaina ta kama.
Bayanin shugaba ya tabbata jininki shine mabuɗin nasarah ta”
Suwiɗi yayi maganar yana kuma sheƙewa da dariya, shuuuu gilmawar wata inuwa ta gefen kunen shi haɗe da kecewa da dariya yasa shi yayi ɗif daga maganar da yake yana dariya, ya dafe kunen shi jin sautin dariyar na neman fasa masa kai.Ɗif sautin dariyar ya tsaya haɗe da talle masa ƙeyya, wanda yasa har ya hantsila daga gurin da yake ya kusa ci da baki.
Tamkar gilawar walƙiya haka yaga ana gilma masa a cikin ɗakin, zoben dake hanunsa yake ƙoƙarin murzawa wanda aka bashi shi lokacin da aka ɗaukeshi da ya karye wanda da zarar wani abu ya same shi yana murza shi za'a bashi kariya, fitt yaje zoben ya fice daga hannunsa yana lilo a iska .
Zare idanunsa yayi, ya tashi yana ƙoƙarin kamo shi tasss yaji an ɗaukeshi da mari saurin dafe kuncinsa yayi yana waige-waige cike da tashin hankali tuna azabar da yasha lokacin da ya karye ya ce“wai waye ne?” yayi maganar yana waige-waige haɗi da maƙalewa jikin bango.
“Hhhhhhh!!! Ba dai har ka fara tsorata ba, ai so muke ka nuna mana da gaske kai ƙwallon shegen ne! Wato da muka ce ka fita harkarta baza ka fita ba ko? Shene kake shirya wata muguntar toh a yau ɗin nan idan baka saketa ba sai mun nuna maka mu mun fika sheganta”sautin murya da gilmawar inuwa tana zagaye Suwiɗi ya fito.
