Chapter Four

3.2K 213 35
                                    





"Ashe abinda ya faru kenan toh Allah kare aukuwan na gaba" fad'in Abba.

"Ameen Abba thank you" ya amsa a nitse. Numfashi me nauyi Abba ya fisga sannan yace, "I'm sorry for my outburst on you, yaci ace na baka dama kayi min bayanin abinda ya faru kafin in yanke hukunci."

"Ba komai Abba ni ya kamata in baka hak'uri I'm sorry in shaa Allah hakan baze k'ara faruwa ba" ya amsa cike da girmamawa da kansa a sunkuye.

   "Masha Allah, Dama Alhj Abdallah ne keson ganinka."
Alhj Abdallah? Afzal ya nanata a ransa, wani Alhj Abdallah d'aya? And saboda meh?

"Alhj Abdallah Abban Nazeefah" Abba ya sake fad'a ganin kaman ya jefa d'an nasa cikin duhu.

"Ohh!" yayi exclaiming se yanzu ya fahimci wa Abba ke nufi. Alhj Abdallah Abban Nazeefah wanda ya kasance aminin Abba kuma second neighbour'n su, gida d'aya ne a tsakanin su. "Abba ina fatan lafiya dai ko?" Ya tambaya a takaice.

"Eh toh it depends, kafin nan ina son muyi wata magana da kai Prince shin ka nada tsayayyiya kuwa?" Zuciyarsa yaji ya mugun har6a bade aure Abba ke shirin masa ba don kuwa be shirya ba, sam ba mace d'ayan da ta ta6a yimasa acikin jerin 'yan matan da Allah ke had'asa dasu. To cut the story short, shi baida ko budurwa d'aya ma balle ace ya cire tsayayyiya a cikin su. Ko da yake London karatu 'yan mata ke binsa and not the other way round, kuma koda wasa be ta6a saurara masu ba haka zalika da ya dawo Nigeria ma yanzu, kusan a kullum se 'yan mata sunzo gunshi a office bayan wanda ke binsa har gida. A sanadin hakan ya hana secretary'n shi barin kowa cikin office nasa in ba wanda ya sanar da ita da zuwan su ba.

"Kayi shiru ko kafi son ku tattauna da Umminka ne tukuna?" Fad'in Abba jin shirun yayi yawa.

"A'a Abba ba abin tattaunawa don a gaskiya banida tsayayyiya" ya basa takaicaccen amsa bayan nazarin daya samu yayi.

"Toh Alhamdulillah" Abba ya saki hamdala wanda ya d'aure wa Afzal kai. Meh hakan ke nufi? Kafin ya kawo wani tunanin a ransa Abba ya cigaba, "Dama Alhj Abdallah ne ke tunanin had'a ka da 'yarsa Nazeefah" wani irin mumunan buguwa zuciyan Afzal yayi wanda sanadin hakan yaji zazzafan ciwon kai na neman afka masa.

"Aure fa kenan Abba?" Ya tambaya cike da mamaki.

"Yes Prince aure kuma kaga jifa yazo dai-dai da zama kenan tunda kace baka da tsayayyiya." Holy crap! Ji yayi kaman ya kashe kansa domin haushi, meyasa bema Abba k'arya yace mar da akwai tsayayyiyar ba a farko? But he can't blame himself saboda baida masaniya akan wannan zance Abba ke shirin sanar dashi. In da kuma k'aryan yayi yace yanada tsayayyiyar and Abba ya buk'acesa da yayi introducing nata ya zeyi? Meyasa Ummi bata sanar dashi wannan ne maganar da Abba ke shirin sanar dashi ba? Nazeefah fah? Wancan fand'ararriyar yarinyan da sama da friends nasa uku sunyi dating nata. 'Yar karamar yarinya amman se shegen rawan kai da falli, idan za'a k'irga samarukan cikin Maiduguri masu ji da kansu toh d'add'aiku ne basu fita da ita ba sam batada kamun kai ga d'an banzan rainin da take ji dashi a takaice de ya tsaneta. Meyasa Abba ze yarda da k'udurin abokin nan nasa? Meyasa ze yarda ya bada only son nasa wa 'yar da batada ko kamun kai? He need answers.

"Prince kayi shiru" fad'in Abba sede har yanzu Afzal besan da wani bakin zai soma magana ba couple with the fact that baida ra'ayin aure ko kad'an yanzu. For crying out loud he's just 25 years old ina laifin abar shi yakai koda 30 ne. "Afzal?" Fad'in Abba for second time.

"Nnn... na'am Abba" yayi stuttering.

"Bakace komai ba" ya sake ce dashi.

"Abba bansan me zance ba, Abba yarinyan can batada kamun kai dan Allah kar ka amince da wannan k'udiri" ya fad'a cike da tashin hankali.

Rana D'aya Where stories live. Discover now