Chapter Twelve

2.4K 372 41
                                    


   Tun dawowan Afzal gida ta soma yi masa k'orafi ita ya saketa zaman ya isheta, be kaiga sa key a k'ofan d'akinsa ba ta hankad'e k'ofan tana masa ihu haka yadda ya dawo a gajiye da ciwon kai ya sake ficewa abun tausayi yabar mata gidan gabad'aya ko tanka ta beyi ba. Gida kawai ya nufa ya wuce site nasa inda ya watsa ruwa ya mik'e kan gado se bacci chan kaman a mafarki yaji ana yi masa knocking tamkar wanda baze tashi ba ya lalla6a ya bud'e segani Ummi yayi tsaye bakin k'ofan.

  "Ashe de dagaske ne ka shigo" ta soma da fad'i tana binsa da kallo na sosai, jin be amsa ba ta k'arisa ciki "Prince?"

  "Uhmm" ya amsa yana kakkafe lumsassun idanunsa wane wanda ya sha abu ya bugu.

  "Lafiya dai ko? Mey haka sekace wanda yasha wani abu?"

  "Ummi please we'll talk later, a gaje nake yanzu, kaina ciwo allow me to rest."

"A gidanka ba wajen hutu ne da seka zo nan zaka kwanta? Ba za ayi wannan rashin hankalin dani ba. Meye dalilin ka? Chan d'in meya samesa?"

  "Ummi please kiyi hak'uri kaina ciwo yake I'll explain everything to you later."

  "Fad'a min meke faruwa tukun ko sena kira Abbanka?"

  "Gidana ba lafiya and I need to rest right now please kiyi hak'uri" ganin yadda idanunsa ke kakkafewa kawai yasa ta fice ta ja mar k'ofar. Komawa yayi ya kwanta bashi ya tashi ba se bayan Maghrib, ya na idar da sallah ya nufi site na Ummi inda ya zauna a gefenta suka gaisa take tambayarsa meke faruwa.

   "Babu kawai mun samu misunerstanding ne da Nazeefah" yayi mata k'arya, har ga Allah beyi niyyan fasawa Nazeefah tyre ba saboda there's no point ma, k'arshenta kawai ze had'a kanta da iyayenta ne ya kuma zubar mata da mutunci da girma a idon Ummi.

  "Prince kalleni" ta buk'acesa. "K'arya kakeyi."

  "Kamar ya kuma k'arya Ummi? Wallahi matsala muka samu amman na tabbata yanzu ta sauk'o zan koma gida muyi negotiating komi idan Abba ya dawo ki gaishe shi."

   "Toh shikenan ka gaishe da Nazeefan kuma ka k'ara hak'uri kaji? Ko zaka tsaya kaci abinci? An kusa sauk'ewa."

  "A'a bana jin yunwa tea kawai zansha idan na isa gida."

  "Toh Babana bari in raka ka se hak'uri zama da mace kaji?" har gun motansa ta rakasa tana yi masa nasiha sannan ta dawo ciki. Da ikon Allah har ya isa gida ya shige d'akinsa Nazeefah dake bayi tana wanka bataji dawowansa ba se chan kusan k'arfe goma da ya fito d'aukan soda daga fridge suka had'u, ba wanda yace ga d'an uwansa ko k'ala kowa harkan gabansa ya cigaba dayi.

   Kusan sati Afzal ya jera yana kai Amal makaranta sannan ya samu wani me napep suka daidaita wanda ze na kai Amal makaranta yana d'aukota a k'arshen wata se a biya sa. Sosai Amal ta miyar da hankalinta ga karatu, daga bokon har islamiyyan bata bar ko d'aya ba.

   Ta fannin Afzal kuwa ababen sun soma canzawa suna ca6e masa wanda kuma ya rasa dalilin hakan, haka kawai yake tsintar kansa cikin wani irin nishad'i duk lokacinda yake kallon hotunan Amal kokuwa yake sauraron muryarta baya manta sati d'ayan daya jera yana kaita makaranta, a kullum tana sanye da three quarter hijabanta da side bag nata a gefe kokuwa ta rataya backpack nata a baya. Komin bak'in cikin da Nazeefah ta cusa masa muddin ya shiga kallon hotunan Amal toh seya nemi wannan bak'in ciki ya rasa. Yau ma kaman kullum yana zaune a office nasa gabad'aya ya zurfafa yana kallon wani hoton Amal da take sanye da wani navy blue hijab me hannu, yatsunta ta k'ayatasu da jan lalle wanda ta rik'e fuskarta dasu ta gefe yayinda hankalinta ya duk'ufa kan wani abu, da alama bata ma san an d'auketa hoton ba. Har Sultan ya bud'e k'ofa ya k'ariso cikin office d'in ya zauna Afzal besan ya shigo ba se ji kawai yayi an fisge wayan daga hannunsa kafin yace ze amshe har Sultan ya k'are wa hoton kallo.

Rana D'aya Where stories live. Discover now