Chapter Twenty-Nine

3.2K 162 22
                                    


A rayuwa ba abinda yake rikita wa Afzal lisafi kaman sautin ihun Amal, kad'an ya rage be fad'i a k'asa ba. "Haba Kitten!" Yayi exclaiming yana murza kunnensa "So kike ki kurmantar da ni ne?"

"Toh Yaya haka ake shafawa mutum man zafi ne? Ba a hankali ake yi ba kasan mey? Bar shi ma kawai in shaa Allah ze warke da kansa."

"Raguwa kawai."

"Ayya Habib Albi amma ai kasan k'arfin mu ba d'aya ba ko?"

"Toh Baby tsaya in miki a hankali" da zaran yace ze murza seta sa ihu dan ba wasa ba cinyoyin nata sun mugun yin tsami, ganin fa ba bari zatayi ya shafa mata ba ga shi lokaci se tafiya yake kawai ya had'e hannayen nata gu d'aya ya danneta sannan ya shiga murzawa maganin, duk kalan ihun da takeyi hakan besa ya saketa ba seda ya murza ya kuma tabbata maganin ya shiga ciki tukuna.

Kuka take sosai harda majina yayinda cinyoyin nata suke yi mata zogi, ba k'aramin dariya ta basa ba amma ya moze, gaban mirror ya nufa ya kawo mata tissue "Hungo share hawayenki Kitten kukan ya isa haka" ko ta kansa batayi ba se lek'a k'afan nata take yayinda take jin yadda maganin ke shiga jikinta.

"Haba Baby naa yi hak'uri kinji? Yaya is sorry" Yayi maganan had'e da zama a gefenta yana k'ok'arin fara share mata hawayen, cike da takaici ta k'wace tissuen nan ta shiga sharewa da kanta bayan ta gama ya amsa yayi disposing "Let's sleep okay?" Ko kallonsa batayi ba taja pilonta izuwa k'arshen gadon ta kwanta, murmushi yayi sannan ya kashe musu wutan ya haura gadon ya kwanta. Pillonsa ya matsar kusa da nata had'e da ya6a hannunsa akan cikinta wanda ta cire da sauri. Mayarwa ya sakeyi itako ta sake cirewa.

"Haba my Baby yi hak'uri bazan sake ba" shiru ta mai bata amsa saba.

"I'm sorry bazan sake ba, yi hak'uri ki juyo mu kwanta my arms feels so empty without you."

"Haka kawai don kaga kafini k'arfi kayita mun mugunta ba, ni gobe zan koma gida gun Mami na."

"Laaa yi hak'uri beyi zafi haka ba Kitten" cike da dabara ya juyo da ita had'e da aza kanta akan k'irjinsa yana mey shafa bayanta a hankali. "Sannu kinji? Yi hak'uri, kika tafi ai bazan iya rayuwa ba" da haka har bacci mey nauyi ya d'aukesu duka.

Ko a washegari Afzal be bari suka fita d'in ba saboda gani da yake kar cinyan nata suji tafiya su k'ara yin tsami. Sosai ya tausaya mata barin ma idan yaga yadda take k'ingishi, banda wanka be sake bari ta koda d'aga tsinke ba.
Da k'yar Amal ta barsa ya fita siya musu abinci ita sam wai ita zatayi girki shi kuma ya rantse seta samu sauk'i tukun. Gidan Nazeefah ya fara nufa dan duba lafiyarta, shi kansa kunya yakeji ace tun da ya k'ara aure be lek'o uwar gidansa ya duba lafiyarta ba sede suyi magana a waya, yau yini na uku kenan.

Sallama yayi yayinda ya shiga parlourn kasancewar bata nan se ba wanda ya amsa. K'arisawa yayi ciki ya lek'a kitchen ganinta da beyi ba seya zarce d'akinta knocking yayi sannan ya bud'e zaune kan gado tana waya ya tarar da ita.

"Ya Rouhi!" Tayi exclaiming had'e da katse wayan, a guje ta mik'e taje tayi hugging nasa, "My Rabba'atul Bait I miss you" ya furta yana mey matse ta gam a jikinsa. Sun d'au tsawon lokaci a haka sannan ya sakota a hankali.

"Ashe zaka kewayo nan."

"Kuma wani irin magana kike haka Rabba'atul Bait?"

"Eh mana Ya Rouhi gashi tun da kayi amarya ka mance ni."

"Ba haka bane Rabba'atul Bait-"

"Toh yaya ne?" ta katse sa "Nayi maka uzuri a ranan farko amma ai yaci ace ka lek'o ni jiya koba haka ba?"

"I'm really sorry Nazeefah nasan nayi miki laifi but forgive me okay?"

"Ba komai dama nasan baka damu da ni ba."

Rana D'aya Where stories live. Discover now