Chapter Thirty-Four

2.1K 198 54
                                    


    Ko makaranta Amal ta kasa fita washegari saboda yadda jikin nata ya tsananta, gashi de ta fara shan maganin amma ba sauk'i. Kaman yadda Maamah ta d'au alk'awari haka tazo ta duba Amal da soft drinks nata, Safiyya ce ta amsa ta sa a fridge sannan ta kai ta d'aki inda Amal ke kwance akan gado ta duk'unk'une kanta acikin bargo se kakkarawa take. K'arya ne mutum ya ganta be tausaya mata ba.

   "Subhanallahi Amal!" Maamah tayi exclaiming cike da tashin hankali. "Amal dan Allah karki mutu" take idanunta suka ciko da hawaye tsan-tsan tausayi.

  "Amal mey kike yima kanki haka? Meyasa baki kira Mami ba? Meke damunki dan Allah?"

  "Maamah calm down ki kwantar da hankalinki."

  "Ya jikin naki? How are you feeling?"

  "Da sauk'i zuwa anjima zazza6in ze sauk'a morning fever ne."

  "Subhanallahi sannu ai baki fad'a mun zazza6in yayi tsanani haka ba what's wrong?"

  "Maamah I'm pregnant" ta sanar da ita.

  "You're what?!" Tayi exclaiming had'e da zaro ido waje.

  "Maamah ina d'auke da cikin Yaya" ta jaddada mata yayinda ta rushe da kuka. Hugging nata Maamah tayi tana kukan tare da ita sun dad'e a haka sannan ta janye Amal a hankali tana mey share mata hawayenta.

  "Amal I'm so happy for you, Allah ya inganta idan lokacin yayi ya raba lafiya."

  "Ameen" ta amsa chan ciki-ciki.

  "Ya Afzal ya sani?"

  "Ke na fara fad'awa ko Mami ban kira na sanar da ita ba."

  "Amal why? Ai Ya Afzal ya kamata ya fara sani ke bakisan wannan news shi ze zame sanadin shirya tsakaninku ba?"

  "Shirya tsakanin mu?" Ta tambayeta had'e da sakar da murmushin takaici "Maamah things just got worst kin san mey Yaya yamun?" Kai Maamah tayi saurin kad'awa.

  "Korana yayi daga d'akinsa shiyasa kika ganni anan bayan nan jiya yake ja mun Allah ya isa idan har na sake shigo masa da na miji gida Maamah zargi na Yaya yake, gani yake kaman duk zaman mu cin amanan sa nake."

  "Innalillahi wa inna ilai raji'un the fuck is wrong with Ya Afzal? Ya yake abu kaman wanda baida ilimi? Ai yaci ace yasan abinda zaki iya aikatawa da abinda bazaki iya ba daga gun wani d'an jakar uban yaji wannan batu? Waya gaya mishi kina shigo da maza gidan nan?"

  "Wallahi ban sani ba Maamah kinsan zurfin cikin Yaya bayi ta6a fitowa fili ya fad'awa mutum abu."

  "Amal dan Allah ki tattara kayakinki kibar mai gidan nan haka wannan walak'anci dame yayi kama? Se kikace mishi mey dayace kibar masa d'akin nasa?"

  "Mey kuwa zance masa? Pillow na kawai na ja na fice mey zance masa?"

"Hmm wallahi munafukar mey aikin ki d'innan nake zargi da ganin yadda fuskanta yake bak'i k'irin d'innan haka zuciyarta take in ba haka ba ina Ya Afzal zeji batun nan? Bawai zama yake a gida koda yaushe ba dole gaya mishi akeyi."

"Na gwada mata magana tace ba ita bace banida lafiya ban so jan maganan ba nace kawai shikenan."

  "Wallahi itace kinji rantsuwa ba kaffara ina gaya miki Nazeefah ba kishiryar arziki bace wallahi aiki suke tare da 'yar nan dalilin daya sa tun farko ta kawo miki ita kenan. Wallahi aiki suke tare."

   "Nazeefah kuma?"

  "Don't be fooled by her kind gestures makashinka na nan tare da kai duk inda kake, kiyi tunani ita munafukar Safiyyan ce take kai wa Nazeefah rahoton komi a gidan nan ita kuma mak'irar seta ce ke ce kika kira kika sanar da ita."

Rana D'aya Where stories live. Discover now