Chapter Twenty-Two

2.6K 208 65
                                    




Har cikin ransa yaji dad'in kalamunta dukda cewan ya san ta fad'i komai ne don kawai yaji dad'i bawai don har cikin zuciyanta tana nufin hakan ba, yasani tausayinsa kawai takeji bawai sonsa take ba.
"Yaya why are you not saying anything?" Ta tambayesa a sanadin shirun da yayi. "Dan Allah kayi hak'uri."

"It's okay Lily you should get going thank you."

"Yaya fushi kake dani har yanzu?"

"Sanin kanki ne komin mey kikayi mun bazan ta6a iya yin fushi dake ba Lily."

"Shine ko kallona bazaka juya kayi kace ka hak'ura ba?"

"Will it change anything?"

"Please Yaya kayi hak'uri Wallahi bazan iya jure fushinka ba."

"Toh na hak'ura" ya fad'a had'e da juyowa yana kallonta kaman yadda ta buk'ata. "Bar kukan haka toh" hannu tasa ta shiga share hawayenta.

"Thank you so very much, barin koma toh Allah k'ara sauk'i."

"Ameen thanks too bari inyi ma Sultan magana ya kaiki gida."

"A'a no need daga school nake zan koma I still have one lecture to attend" tayi maganan tana duban agogon hannunta.

"Are you sure?"

"Yes Yaya" ta amsa had'e da sakar masa k'aramin murmushi.

"Alright you take care" a waje ta tarar da Sultan tayi masa sallama sannan ta fice.
Bada dad'ewa ba Nazeefah ta kawowa Afzal abincin, bayan ta basa ya ci ya buk'aci Dr'n da ya sallamesa.

****
Ta fannin Abdul kam k'aramin hauka ne kawai beyi ba, yau ko fita office ya kasa, banda tunanin Amal ba abinda yakeyi, gabad'aya ya rasa mey ke masa dad'i yau kwana nawa amma a rasa wanda zeje ya duba masa lafiyar Amal? itama Amal d'in kwana nawa yau amma bazata nemesa ba? Anya kuwa lafiya? Tunani de ba wanda beyi ba. Toh kode su Mami sunyi mata miji ne a gida suka hanata yin waya dashi suka amshe mata wayan ma gabad'aya? But ai bazasu ci amanar sa haka ba bayan seda ya tura su Baba da su sanar dasu shi yayi kamu then what could be the problem? Kwana yayi yana nazari, washegari da yamma ya kira Maamah. Har tsoron picking call d'in take amman haka ta d'aga don ba yadda ta iya.

"Maamah what is going on?"

"Game da mey Ya Abdul?" Ta tambayesa tamkar bata fahimci inda ya dosa ba.

"Please tell me meke faruwa meyasa line na Amal baya shiga?"

"Ya Abdul ban san-"

"Maamah we both know you're lying sarai kinsan meyasa, dan Allah nace please tell me it's been over a week bana samunta har Mama nasa aje aji mun ya take amma shiru. I can smell it something is not alright."

"Ya Abdul-"

"Ki fad'a mun kinji?" Ya katse ta "Idan ma abu ne yasamu Amal d'in kuke 6oye mun just tell me I promise bazanyi reacting ba."

"Ya Abdul ba abinda ya samu Amal, lafiyarta k'alau."

"Then meya faru? Meyasa bata picking call d'ina?"

"Ya Abdul I'm sorry."

"Fad'a mun kinji? Kar kiji komai."

"Kayi hak'uri amma bazan iya ba."

"Meyasa?"

"Na d'au alk'awarin komin yaya baza aji mutuwan sarki daga bakina ba, kayi hak'uri."

"Aure Amal zatayi ko?" Ya tambayeta a hankali daga yadda yake magana mutum zesan zuciyarsa a karye take, sosai ta sha mamakin yadda ya gano hakan ba tare da wani ya sanar da shi ba.

Rana D'aya Where stories live. Discover now