Chapter Twenty-One

2.6K 214 33
                                    


Kasancewan jikin Nazeefah a gida Afzal yayi sallah ya jasu tare, bayan sun idar da sallan ne ya shiga shirin office inda tace zata had'a mishi breakfast. Take ya hanata akan ta kwanta ta huta tunda bata da lafiya, he can manage. Haka ya shirya ya had'a breakfast nasa ya ci sannan yayi mata sallama. Kaman yadda ya saba kiran Amal ko wani safiya haka nan ma yayi yau sede har yanzu Amal bata sakewa dashi sama-sama suka gaisa sannan ya katse.

Da yamma bayan Amal ta dawo daga school ta la6e a d'akinta se hira suke a waya da Abdul not knowing Mami na la6e tana sauraronta tun d'azun. Ashe de har yau bata fasa waya da Abdul ba, shin wai meke damun Amal? Ta tambayi kanta, ace mutum an bada shi ma wani amma ya zauna yana hira da wani na daban? Bata yi mata magana ba ta koma ta cigaba da aikin dake gabanta. Bayan dawowan Papi ne ta zaunar dashi take fad'a masa abinda ke faruwa. Amal d'in ya kira bayan ta k'ariso take mai sannu da zuwa.

"Yauwa Mamana ya makaranta?"

"Alhamdulillah."

"Nace yaron nan Abdul ai baku waya yanzu ko? Kuma kin canza sim naki kaman yadda iyayensa suka buk'ata?" Shiru Amal tayi dan ko k'aryan da takeson yi d'inma ta gagara, kum taji bakinta ya kullu.

"Baby?" ya kirata.

"Na'am Papi" ta amsa.

"Baki jini bane? Kode har yanzu kuna waya ne dashi?" Nan ma shiru. "Ba magana ake miki bane Baby?" Mami tasa baki.

"Eh Papi" ta amsa murya chan ciki-ciki.

"Haka kukayi da iyayensa? Ke bakisan cin amana kike ba yanzu Baby? Taya bayan an bada ke ma wani amma ki tsaya kina hira da wani na daban? Kina ganin kin kyauta wa shi Afzal d'in kenan Baby?" Shiru tayi ta kasa cewa komai yayinda take nazarin rabuwa da Ya Abdul.

"Iyye? Kina ganin kin kyauta masa kenan?"

"A'a" ta kad'a kai a hankali.

"Toh kije na baki nan da kwana biyu ki canza sim kuma kar in sakejin kina waya da Abdul d'in kinji?"

"But Papi-"

"Ko baki jini ba? Har yaushe kike son ki cigaba da yaudarar sa? Kefa kikace kin amince zaki auri Afzal kodan ki biyasa alkhairin da yayi miki a baya yanzu kuma kice ba haka ba Baby?"

"Papi bawai dena waya da Ya Abdul d'inne bazan iya ba, naga tunda ba auran Yaya zanyi ba yanzu ai ba laifi idan muna gaisawa da Ya Abdul, Papi dan Allah karkace a'a."

"Kaman ya Baby? Ni da na d'au da jimawa ma kin canza layin naki? Ke bakisan alkhairi ne miki ba idan kika rabu da Abdul d'in tun wuri, kema zaki fi samun kwanciyan haka shima a hankali Allah ze yaye masa son da yake miki kuma gaisuwa ne kad'ai kuke ko hirar masoya?"

"But Papi-"

"Ya isa haka Baby baki cika sa6awa dokokin da nake kafa miki ba, kar kiyi hakan yanzu nan da kwana biyu bana son in sake jin kina waya da Abdul idan kuma ba haka ba zan yima iyayen Afzal magana dama su basu k'i ko a satin nan a d'aura auren ba, se suzo ayi magana asa rana."

"Papi dan Allah kar kayi mun haka."

"Toh kiyi kaman yadda nace." Kai ta gyd'a a hankali tana share hawayenta "Tashi ki fice Allah yayi miki albarka" ko amsawa batayi ba ruga d'akinta a guje ta baje kan katifarta ta shiga aikin kuka. Wayanta ta jawo had'e da shiga photos tana kallon pictures nasu tare da Ya Abdul yayinda kukan yaso yaci k'arfinta. Chan dare kaman yadda ya saba kiranta haka nan ya danna mata kira bata 6ata lokaci ba ta d'aga suka sha firarsu sam bata nun masa wai da akwai matsala a k'asa ba sede ko da yakeson yi mata seda safe tak'i amincewa ya katse wayan ita wai suyita hira kawai. Haka ya biye mata dukda cewan bacci yakeji, wayan suka yita yi har zuwa lokacinda ta zarce bacci se anan yayi mata goodnight yayi hanging call d'in. Washegari bayan ta taso daga school ta wuce Post office ta sai sabon sim sannan ta dawo gida. Video call ta dannawa Ya Abdul shi kansa beyi expecting ba dan tun tafiyansa sau d'aya da sukayi video call basu kuma ba. Haka nan tayita masa hirar shirme har seda kud'inta ya k'are sannan ya kirata suka cigaba har anan bata nuna masa cewan akwai wani abu ba. Da daren ranan ne bayan sun k'are wayan ta karya sim d'in ta sa sabuwa tana kuka haka ta zuba pieces d'in a bola. Ranan ko bacci batayi ba, kuka ta kwana tana yi washegari idanun nan sun kumbura tim ko school ta k'i fita. Dama normally kowani safiya da good morning text messages na Ya Abdul take tashi se gashi yau wayam ba komai. Ba yadda Mami batai da ita ta fito ta karya ba amman tak'i.

Rana D'aya Where stories live. Discover now