Chapter Thirty-Three

2K 198 28
                                    


Se yamma Amal ta dawo gida bayan sun k'are karatu da Maamah. Driver na sauk'eta ta zarce d'akinsu inda ta tarar da Afzal yana shirin komawa gun Nazeefah ko sannu da zuwa beyi mata ba hasali yi ma yayi tamkar be ganta ba. Itace tayi gyaran murya ta gaishesa tukun ya amsa sama-sama.
"Zan koma gida gun Nazeefah ga kud'inki ajiye a gaban mirror" ya sanar da ita.

"Habib Albi tun yanzu zaka tafi?" Ta tambayesa tana mey duban agogo dududu 5:17 ne amma yake zancen nan bayan se pass 6 yake tafiya kullum.

"Eh wani abu ne?"

"Habib Albi ko ka mance da alk'awarin da kayi mun?"

"Na mey fa?"

"Kace kafin ka tafi zamuyi wanka tare I miss bathing with you Habib Albi, I really do" tayi admitting abun tausayi. Kau da kansa yayi gudun kar tausayinta ya kama sa.

"Nata jiranki baki dawo ba Amal ni kuma sauri nake maybe next time."

"Abinci fa kaci? Nasa Safiyya ta maka microwaving sauce d'in ta dafa maka white rice tayi?"

"A k'oshe nake karki damu na wuce."

"Yaya" ta kira sunansa da sauri lokacinda ya shiga takawa chak ya tsaya had'e da kewayowa.

"Wani abu ne?" So take tayi masa magana kaman yadda Maamah tace da ita amma inaa bata jin zata iya, mugun nauyinsa takeji bata son a sanadin hakan yaga kaman rashin kunya take son yi masa don haka kawai tayi shiru. "Sauri nake" ya sanar da ita.

"Ermm nace Allah dawo da kai lafiya ka gaishe da Nazeefah idan ka isa."

"Kaman dagaske" ya furta chan ciki-ciki.

"Na'am?" Ta tambaya kasancewar bata jisa da kyau ba.

"Nace naji" da haka ya fice Allah kare Safiyya dake sharan parlour tayi mishi sannan ya k'arisa.

Safiyya na ganin fitansa tayi hanzari ta kammala sharan nata da wuri ta wuce d'akinta inda tasa key ta danna wa Nazeefah kira bayan sun gaisa take ce mata, "Aunty bazaki amince da abinda nake shirin fad'a miki ba."

"Mene meya faru?"

"Hmm yanzun Uncle ya bar gida toh kafin ya fito ina cikin share corridon d'akinsu naji su suna magana da Aunty."

"Wai mey suke cewa?"

"Nide ban gane kan zancen nasu ba amma naji tana ce masa wai yayi mata alk'awarin zasuyi wanka tare se gashi kafin ta dawo daga makaranta har yayi wankansa ya gama shiri."

"Wanka tare?!" Nazeefah ta tambaya da d'umbun mamaki "Wanka tare de?" Ta sake nanatawa yayinda ta kasa amincewa da hakan.

"Wallahi Aunty."

"Kaiiii inaaaa! Baki ji su da kyau ba, wannan k'arya ne."

"Wallahi na jisu da kyau Aunty kuma daman tun ba yau ba ina zaton hakan dan akwai ranan da abokin Uncle yazo Uncle Sultan se yace inje inyi ma Uncle magana toh dana k'arisa d'akin nasu sena tarar da k'ofan a bud'e nayita sallama amman shiru chan dana kasa kunne najiyo hayaniyansu acikin bayin."

"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un wallahi Amal mak'ira ce, shegiya 'yar asiri toh dan ubanta bazeyi wankan ba kiji mun karuwanci fah! Wato har wanka ma sukeyi tare? Chab!"

"Hmm wallahi ko amma kuma kinsan tun dawowan Uncle wannan karan ko fita sau d'aya basuyi ba? Jiya kanma da tayi masa breakfast k'in ci yayi yace wai nice zan yi masa baya son nata. Bayan nan zama da sukeyi a parlour suyi kallo ma basuyi yanzu gashi banda d'ad'd'aure mata fuska ba abinda yakeyi yau tana da makaranta da safe amma yak'i kaita sa6anin kullum yace se de driver ya kaita shi yana da gun da zasa. Maganan da nake miki yanzu ko tsinke ban ga ya siyo mata ba tun zuwan sannan."

Rana D'aya Where stories live. Discover now