Chapter Nine

3.1K 186 76
                                    

BY MIEMIBEE
PAGE 09

"Quite alright nasan ina k'ona mata miya but tun kan alk'awarin dana d'aukan maka wallahi ban sake ba se yau, kawai tana neman huce haushi na da takeji ne taketa nanatawa haka nan" ta fayyace mai hawaye na tsiyaya daga idanunta.

"Meyasa baki sa hankalinki ba kika bari har girkin ya k'one? Bance idan Mami ta saki aiki ki bar duk abinda kikeyi ba muddin ba sallah bane kisa hankalinki?"

"Ka fad'a" ta amsa tare da dukar da kanta.

"Then what happened?"

"Yaya duk hankalina baya jikina, na rasa ina zan sa kaina da abinda Abdul (yaron me markad'e) yayi min kuma wallahi ba wani novel d'in nake karantawa ba hasali ma ina zaune cikin kitchen d'in amman banma san miyan na k'onewa ba seda ta shigo ita kuma ta dage sam wai novel nike karantawa shi ya d'auke min hankali."

"Shikenan ya isa, bar kukan haka kinji? Am here for you bari Mami ta dawo zan yi mata bayani."

Bayan isowan Mami Afzal ya sa Amal ta amshi cafanin ta shiga sarrafawa acikin kitchen yayinda shida Mami suka zauna suna tattauna batun Amal da Abdul. Sam Mami tak'i yarda da abinda Afzal ya fad'a mata a cewarta wai kawai Amal ta tsara Afzal d'inne don ya tausaya mata, ita da ta ga abu da idonta Amal ta kwanta jikin Abdul ne kuma za'a tsaya ana mata wasa da hankali? Daga k'arshe ba don tana so ba se don tana jin nauyin Afzal ta nuna masa ta yarda komi ya wuce. Rok'anta sosai Afzal yayi cewa kar ta fad'awa Papi nan ma de tace taji baza ta fad'a mar ba amman dukda haka Afzal be yarda ba seda yasa ta d'au masa alk'awari. Nan ya zazzage tsaraban daya siyo musun, sosai tayi farin ciki da godiya da addu'a har ta buk'ace sa daya tsaya ya jira abinci amman ya nuna daga gida yake don haka a k'oshe yake. Amal ta kira ta nuna mata kayakin inda itama ta nuna farin cikinta sosai dukda cewa chan k'asa hankalinta a tashe yake. Godiya ba adadi tayi masa itama sannan suka rakosa waje, yau zuwa bakin k'ofa Mami ta rakasa tace su k'arisa da Amal kasancewar miyan dake kan wuta. Wajen motansa suka nufa suka shiga ciki suka k'arisa bakin layi gun markad'en su Abdul.

   Plan daya shirya yayi ma Amal bayani sannan ya mik'a mata wayarsa bayan ya nuna mata inda zata danna da zaran sun fara magana da shi Abdul d'in. Daga cikin motansa ya zauna yana hangensu yayinda ta k'arasa ta sami Abdul.

"Abdul inason magana da kai" tace dashi ba gardama ya mik'e harda d'an guntun murmushinsa ya nufo inda take tsaye. A tunaninsa wai ko tazo ta fayyace mar soyayyan da take masa ne.  Nan Amal ta danna button na play had'e da b'oye wayar k'ark'ashin hijabinta gudun kar ya gani sannan ta fara kamar haka;

"Yanzu Abdul abinda kayi min ka kyauta kenan?"

"Mene? Ban fad'a miki cewa na lahira seya fiki jin dad'i ba muddin kika k'i bani had'in kai?"

"Toh Abdul ana soyayyan dole ne? Ka gane mana bana sonka."

"Ni kuwa sekin soni in ba haka ba ki shirya wa tashin hankalin dayafi wanda kika shiga a baya."

"Mey kake nufi da hakan?"

"Ina nufin a shirye nake da inyi komi domin inga na mallakeki."

   "Kana nufin zaka iya ta6a lafiyata idan banyi yadda kakeso ba?"

  "Sosai ma kuwa har kisan kai zan iyayi a kanki."

"Lallai kuwa kasani Allah ya fika kuma ma ranan mey kasa min na zame?"

"Aww ma tambaya kike? 6awon ayaba na ajiye miki bayan nasa Mami ta biyoki ranan don ta tabbatar da abinda na fad'a mata akanki."

Rana D'aya Opowieści tętniące życiem. Odkryj je teraz