Chapter Twenty

2.5K 186 56
                                    


Sosai kan Mami da Papi ya d'aure barin ma ganin yadda ta shigo a guje da sukayi ko amsa kira batayi, toh kode wani abun ne ya bita? Da wuri Mami tabi bayanta ta lek'a waje don tabbatar da me ke faruwa chan kawai ta hango Afzal zaune kan benchi ya had'a tagumi. K'arisawa tayi ta zauna a gefensa sede har anan be lura da cewa ma wani ya zauna kusa da shi ba. "Afzal?" Ta kira sunansa se a karo na biyu ya amsa a firgice.

"Lafiya?" Ta tambayesa. Sam be 6oye mata mumunan halin da yake ciki ba. "Ba lafiya ba Mami" ya amsa tamkar wanda zeyi kuka.

"Meya faru? Kai da Baby ne? Yanzu naga ta shiga ciki a guje wani abun ne?"

"Mami Amal bata sona sam bata sona Abdul take so it breaks my heart watching her cry like this I can't take it anymore."

"Laaa! Bade kukan kai ma zaka yimun ba?" Ta tambaya da mamaki.

"Mami no."

"Toh ya kakeson ayi kenan?"

"Ni zan hak'ura yaso ta auri Abdul d'in kawai, farin cikinta ya fiye mun komai."

"Kaman yadda kaima lafiyarka ya fiye mata komai ba."

"Mami she's hurting alot please ku barta ta auri wanda zuciyanta keso."

"Yaushe ne zaka gane kaine za6in da Allah yayi mata Afzal? Kuma yanzu da kake biye mata d'in kai kuma ya zakayi da naka ran? Idan ban manta bafa likitanka ne yace rashin magance maka wannan matsala yana iya saka rasa ranka koba haka ba?"

"But Mami Amal's happiness comes before anything my life included."

"Kar ka kariya Afzal kar ka bari tausayinta ya rufe maka ido tabbas Amal abar a tausaya mata ce amman kai be kamata ka kariya haka gabad'aya ba. Amal na buk'atanka yanzu. Idan har bata sonka ya zame dole kenan ka koya mata. Mu mata munada laushin zuciya garemu, abu kad'an yakan karakato mana da hankali hak'uri zakayi ka nuna mata tsan-tsan so hakan ne kawai zesa ta iya mancewa da Abdul ka kuma maye gur6insa a zuciyanta amma idan ka kariya haka ai kaman ka bata dama ne ta cigaba da kewan Abdul d'in koda yaushe, Amal taka ce Afzal."

"Mami bana son ina ganinta cikin k'unci da hawaye haka duk laifi na ne gashi yanzu Amal ke shan wuya."

"Ka dena cewa haka Afzal kuskure de an riga anyisa ba kuma amfanin nanatasa kaide yanzu ne ya kamata ka nuna jarumtakarka wajen tabbatar da cewa Baby ta mance da Abdul idan ko kayi sakaci..."

"Thank you Mami."

"Karka damu duk lokacinda kake buk'atan wani abu kar ka 6ata lokaci ka taho ka sanar dani damuwanka ina nan zan kuma yi iya k'ok'arina inga na magance ma wannan matsala kaji?"

"Thank you so much."

"Ba komai zaka shiga ciki kokuwa?"

"A'a zan wuce gida but please ki samu Amal ki bata hak'uri tabar kukan haka nan."

"In shaa Allah" da haka ta rakasa gun motarsa bayan ya fice ta dawo ciki ta wuce d'akin Amal sede duk suratan da take tayi Amal tak'i tasowa ta koda bud'e mata k'ofar se kuka kawai take, k'arshe seda Papi yace ta hak'ura ta barta kawai. Tambayanta yayi ko meke faruwa inda ta zauna ta zazzage masa komai. Sosai ya tausayawa Afzal d'inma kansa tabbas ya cika masoyi na k'warai shima da har yake tunanin saudakar da rayuwansa gabad'aya saboda farin cikin Amal sede kaman yadda Mami ta fad'a kada ya kariya ya cigaba da nuna mata so a hankali zata koyi sonsa shima ta kuma manta da Abdurrahman.

Tun isan Afzal gida Nazeefah ta lura da yanayinsa gabad'aya ba walwala tattare da shi sa6anin yadda ya fita. Ko da tayi masa tayin dinner ma cewa yayi a k'oshe yake baze ci ba ya wuce d'akinsa amma bata sauraresa ba ta d'iban masa abincin ta d'au ruwa a fridge ta nufi d'akinsa. Knocking tayi bayan ya amsa ta shiga ciki. Tsince akan gadonsa ta samesa da wuri ya 6oye wayansa dayake ta faman kallon hotunan Amal k'ark'ashin pillow. Bayan ta k'ariso ta ajiye masa abincin akan side drawer tare da buk'atansa ya tashi ya ci. Beyi musu ba ya mik'e ya zauna.

Rana D'aya Where stories live. Discover now