Chapter Twenty-Five

2.8K 199 33
                                    


Shirye-shiryen biki kuma aka shiga yi na sosai, kaman yadda akayi bad'ad'in bad'a haka aka kuma. Kyautan gida Abba ya sake yiwa Afzal a matsayin gudumawan da ya bayar. Sosai Ummi take taimaka wa Afzal, kusan komi ita takeyi, duk wani abinda yake buk'ata fa toh tun kafin ya furta zata tambaya masa gun Abba. Akwatuna har guda ashirin da d'aya aka had'a wa Amal sannan na Nazeefah kuma set mey k'waya shida na fad'an kishiya. Kusan duk zannuwan da suke cikin na Amal akwai su a na Nazeefah babancin kawai na Amal sunfi yawa ne. Abinda ya kama daga kan kayan kitchen, gadaje, kujeru, show glasses, rugs, da komai Ummi ne suka siya, ba yadda Mami batayi da ita ba akan ta bari ko wani abu k'adan ne su kawo yaso se a had'a kud'in ayi siyayyan amman Ummi tak'i kasancewar Afzal ya rok'eta da komin yaya karta yadda ta amsa koda kobo ne daga gun su. Sude kawai suyi focusing akan abincin da za'a dafa.

Mutum na iya rantsewa 'yar Ummi ce zatayi aure don kalan kayakin d'aki masu tsada da alfarman da ta sai wa Amal. Gida yayi kyau sosai se wanda ya gani. Yau ana saura sati uku d'aurin aure kenan.

***
"Halo Yaya?" Tace bayan ta d'aga wayan.

"Na'am Baby" ya amsa.

"Yaya wai yaushe ka fara kirana da Baby?" Yau kam ta kasa hak'ura seda ta tambayesa. Kusan sati kenan yana kiranta da hakan, kuma da gan-gan yake gano bata so.

"Jimin 'ya da ba sunanki bane?"

"Ni Amal ne suna na."

"Baby'n fah?"

"Sunan gida ne."

"Ni d'in ba d'an gida bane?"

"Ni ba haka nake nufi ba kawai na gwammaci kana kira na da Amal ne."

"Toh nak'i ni Baby nafi so."

"Toh Allah taimake ka, ina yini?" ta gaishesa.

"Lafiya d'an fito waje kinji?"

"Yaya ka fa san an fara yimun gyaran jikin."

"Se akace baki sake tako waje?"

"Toh ai Yaya idan na rink'a fita muna had'uwa bazaka ga effect na gyaran jikin ba."

"Nide fito ina jiranki." Nan da nan ta janyo hijabinta tasa ta fita taje ta samesa.

"Tabarakallah gaskiya Allah yayi halitta anan" ya ce da ita lokacinda ta shiga motan "Masha Allah, Abba yayi gaskiya da yace na iya za6i kin ganki kuwa?"

"Kai Yaya kadena zolayata mana."

"I'm damn serious wai ma yaushe ne auren? I can't wait any longer."

Wani irin ruwa cikinta ya d'auka, ba shiri ta had'iye miyau had'e da tambayansa,
"Uhm so what brought you here?" Don canza topic d'in.

"Is it a crime idan ango ya zo ganin amaryarsa sati uku kafin aurensu?"

"Ba wai haka nake nufi ba I mean akwai matsala ne?"

"Ohh wato ma haka kika miyar dani se idan akwai matsala nake tahowa ko?"

"Goodness! Nifa ba haka nake nufi ba."

"Toh yaya ne?"

"Babu nayi shiru."

"Yauwa da yafi kam so jiya kika gama bada haddanki duka wai ko?"

"Eh."

"Congratulations then, Allah sanya albarka aciki yasa idan kika tashi haifo mun yara ki haifa mun hafizai kaman ki Lily I'm so proud of you."

"Ameen Yaya thank you" ta amsa tana mey jin kunyansa.

Rana D'aya Where stories live. Discover now