Chapter Five

2.9K 203 56
                                    




   "Assalamu Alaikum" ya fad'a a yayinda yake sa kai cikin parlon Abba.

  "Wa'alaikumus salam" Abba dake zaune akan kujera ya amsa tare da ajiye newspaper'n da yake karantawa yana mey maido da kallonsa ga k'ofar.

  "Shigo Prince bismillah" shigowan yayi inda ya nemi waje ya zauna a k'asa. "Ya zaka zauna a k'asa sekace wani bak'o?" Abba ya tambayesa da wuri "Take a seat please."

   A'a Abba I'll be fine here."

  "Non sense, take a seat please" be sake yin gardama ba ya koma kan kujeran ya zauna sannan ya gaishe sa cike da ladabi. Batare da 6ata lokaci ba Abba ya wuce straight to the point "Umminka tace ka makara yau baka samu daman fita office ba ko?"

  "Eh wallahi Abba" ya fad'a yana sosa temple nasa.

  "Toh dama batun maganan jiya ne nakeson in baka hak'uri" ido cike da mamaki da neman k'arin bayani Afzal ya d'ago yana kallon Abba da ya cigaba da magana. "Da kace yarinyan bata da kamun kai bai kamata in sake tilasta maka cewa lallai-lallai seka aureta ba saboda ko addinin musulunci ya hane yin hakan, so kayi hak'uri na maka ba dai-dai ba yanzu haka daga nan zan wuce gidan Alhj Abdallah zan basa hak'uri akan cewa auren nan ba ze yuwu ba ka na iya tafiya nagode."

  "Abba ni bakayi offending d'ina ba saboda koda ka tinkareni da maganan jiya ba lallai-lallai cewa kayi sena auri Nazeefah ba, hasali ma baki na ka tambaya ni kuma na baka amsa bisa rashin tunani. Abba farin cikin ka yafiye min komai a duniyan nan, bazeyi ka bani komai a duniyan nan ba nikuma don for once ka tambayeni abu in hana maka shi ba saboda son rai ko makamancin hakan, Abba na amince da auran Nazeefah idan har yin hakan ze farinta maka rai." A hankali kalamun Afzal suke shiga kunnen Abba suna kwanciya a birnin zuciyansa, don farin ciki ya ma kasa believing abinda kunnansa suka jiye mar, ji yayi son d'an nan nasa na k'ara dad'uwa a birnin zuciyansa, wani sa'in har tambayan kansa yake me yayi wa Allah daya azurta shi da d'a kaman Afzal, yaron da baisan meye kalman son kai ba, yaron da seya kawo tunanin wani kafin ya kawo na kansa, tabbas yasan yayi sacrificing alot to come to this decision, yasan wannan babban hukunci ne Afzal ya yanke ma kansa irrespective of whatever the outcome might be, ya sani idan da har za'a tone zuciyan Afzal ba son auren nan yake ba ya amince ne kawai don ya farinta masa rai kamar yadda shima ya fad'a kuma hakan da yayi ba k'aramin dad'i ya sanyashi ba.

  "Afzal?" Abba ya kirasa da asalin sunansa wanda ya juma beyi hakan ba.

  "Na'am Abba?" ya amsa kansa a sunkuye.

  "Afzal ka d'ago kanka ka kalleni" ya buk'acesa. Hakan yayi "Ka sake nanata abinda ka fad'a" Abba ya buk'ata. Sak abinda ya fad'an ya kuma nanatawa Abba can't help but to feel shocked, surprised and happy duka. Emotions ba wanda Afzal baisa shi feeling ba.

  "Afzal bana son a sanadin hakan rayuwanka ya shiga wani hali idan har kasan you don't mean this and you can't find it in your heart to love that girl somday karkayi forcing kanka nasan yadda zan 6ullowa Alhj Abdallah da wannan magana I want you to consider youself  first."

  "Abba I mean it your happiness means the world to me" ya sake tabbatar mishi.

  "Alhamdulillah Alhamdulillah Afzal ban san da wani bakin zan soma maka godiya ba, tabbas bansan ya rayuwata zata kasance ba idan ba kai, mahaifiyar ka batayi k'arya ba da tace mun babban kyautan da zan iya samu a duniyan nan shine kyautan ka da tayi min, yanzu nake sake jaddada hakan. Afzal Allah yayi ma albarka, Allah cigaba da sa albarka acikin rayuwan ka kamar yadda ka farinta min yau Allah ya farinta maka haka kaima, Allah ya baka yaran da zasu maka fiye da haka kaima wataran, k'arshe kuma Allah cigaba da kai rahama kanarin marigayiya."

  "Ameen Abba."

  "Nagode, nagode sosai Allah yima albarka."

  "Abba godiyan ya isa haka please idan har akan d'an wannan kake gode min haka ni kuma da kamin komai a duniyan nan ya kakeson inji? That am an ingrate?"

Rana D'aya Where stories live. Discover now