Chapter Thirty-Eight

2.6K 210 10
                                    



  "Amal why aren't you saying anything?" Ya tambayeta a maraice bayan dogon shirun da tayi, shirunta a garesa ba k'aramin tashin hankali bane but he really can't force it ya zama masa dole ya hak'ura ya bata space da take buk'ata har izuwa lokacin da za ta huce.
    Tabbas mutum ya guji fushin mey hak'uri koda wasa be ta6a tsammanin Amal zatayi masa fushi haka ba saidai bai ga laifinta ba ko d'aya saboda shi ya turata har bango, idan da wata ce da tun ranan da ya korata daga d'akinsu zatayi mai fushi amma dukda hakan bata fasa yi masa ladabi ba, he's sure with time she'll come by.

Envelope da ya tanadar mata ya zare daga aljihunsa ya ajiye mata a kan gadon daga gefenta sannan ya mik'e "I have to go now, Allah k'ara miki lafiya I can't wait to see you back on your feet I love you so much my adorable Kitten" badan yana so ba ya mik'e ya fice juyawanda Amal zatayi hawaye ya tsiyaya daga d'ayan idonta. Tabbas har yanzu tana son Yaya amma idan ta tuna da abinda yayi mata se taji gabad'aya ya fita mata a rai, she never wished for things to turn out bad between them two like this, amma ya ta iya? She can't change the past only can she make the future better. Gyara kwanciyanta da tace zatayi taji k'aran paper, a hankali ta miyar da idonta wajen nan taga envelope da ya ajiye mata da hannunta d'aya ta d'aga ta zazzage inda ta tarar da kud'i da dama aciki, sabin dubu d'ai-d'ai. Da hannunta d'aya ta irga taga dubu ashirin ne sannan ta miyar ta ajiye a gefe.

***
  Koda Afzal ya shiga cikin mota ya kasa kunna engine d'in, be hankara ba kawai yaji hawaye na tsiyaya masa daga ido yau ina ze sa kansa? Ya ze rayu idan ba Amal a kusa da shi? Gani yake idan har bata dawo a garesa ba ze mutu saboda zuciyarsa bazata iya jure rashinta a kusa da shi ba da k'yar ya iya kunna motan ya koma office. Hud'u nayi ya tashi. Gabad'aya ya mance da labarin Hindu se yanzu ta fad'o masa a rai, gidan Nazeefah ya biya inda ya sameta kwance a d'akinta tana bacci, tashinta yayi sannan ya kira driver'n Amal da ya kaita gida bayan sallamarta da yayi. Tana isa gida Ummansu ta rungumeta tana kuka tun jiya take kuka har zuwa d'azu da taje ta duba Safiyya. Dama tun farko ita bata goyi bayan kawosu birni ba dan gudun sharri irin wannan. 

   Se k'arfe shida Afzal ya wuce police station d'in yayi magana akayi releasing nasu Nazeefah. Da gudu ta fito ta fad'a jikinsa tana kuka "Ya Afzal dan Allah kayi hak'uri ka yafe mun na tuba bazan sake ba" hannunsa yasa ya janyeta "Don't misinterprete my intention, ba wai don ina so nasa akayi setting naki free ba Nazeefah se don Abba ne ya buk'aci hakan, idan da ta ni ne da se kotu ta yanke miki hukuncin da yake dai-dai da laifin da kika aikata sannan zanji dad'i because I want you to change, canji na tsakani da Allah bana muzurun da nake da tabbacin kikayi ba. Bazan 6oye miki ba Nazeefah, da abinda kikayi kinsa na tsaneki kaman yadda Amal ta tsaneni yanzu, ko k'aunan gani na Amal bata so a haka kike cewa kina sona? A tunani na idan kana son mutum har abinda yake so zaka so, kin san ina son Amal but you still went ahead and hurt her I'm still mad at you Nazeefah I might forgive you someday amma bazan ta6a mancewa da abinda kikayi wa Amal d'ita ba let's go home." Driver'n Amal ya kira yazo ya d'auki Safiyya itama kud'in sallamarta yabata sannan ya buk'aceta da idan ta isa gida ta tattare ina-inata tabar masa gida yayinda shi da Nazeefah suka koma nasu gidan suma.

   Babban akwatinta ya d'auko mata "Here start packing your clothes ki bar min gida bana k'aunan ganinki anan Nazeefah as long as kika cigaba da zama anan zakina sani tunawa da munanan abubuwan da kika rink'ayi wa Amal d'ita wanda hakan ze sa in sake tsanar kine kawai so its better ki koma gida gun su Mummy." Kuka take sosai ta k'arisa inda yake tsaye had'e da sauk'a k'asa akan guiwarta "Ya Afzal dan Allah karka mun haka, dan Allah don't send me home I'm terribly sorry please forgive me wallahi na tuba bazan k'ara ba dan Allah kar ka sakeni Ya Afzal bazan iya rayuwa ba kai ba please don't divorce me" ta k'arisa cikin tsananin kuka. Hannu yasa ya d'agata "Bazan sake kiba Nazeefah saboda despite everything I still love you and I cherish the moments we spent together, I just need some space and alone time anytime I'm ready zan dawo dake but you really have to go now." Rungumesa tayi tana kukan cire rai "Please don't send me away Ya Afzal I can't live without you dan Allah kayi hak'uri ka yafemun please don't send me home I'm so sorry" kuka ta cigaba dayi ajikinsa na sosai ta basa tausayi shima bawai dan yana so ze korata gida ba dan kawai bayida wani option ne saboda zamanta acikin gidan nan kawai sake sanyasa tsananta zeyi shi kuma baya son hakan saboda idan ya tsani abu ya tsanesa kenan no turbing back, so it's better ta tafi gida kawai. A hankali ya sauk'e hannayensa a bayanta hugging her back sun d'au tsawon lokaci a haka sannan ya janyeta na k'arfi dan yadda ta kankamesa kuka take sosai tana kad'a masa kai "Please don't do this Ya Afzal please don't."

Rana D'aya Where stories live. Discover now