Chapter Fourty-Five

3.4K 248 60
                                    


"Ameen Alhj na."

"Mey hakan ke nufi kenan Hjy Surayya? Kin hak'ura kin yafe mun kenan?"

"We all make mistakes Alhj amma ba dukan mu bane muke gano kuskurenmu har ma mu nemi tuban wanda muka wa laifi, shin meyasa bazan yafe maka ba tunda har kai ka gane kuranka ka kuma nemi tuba? Na yafe maka Alhj Allah kuma ya yafe mana gabaki d'aya" ta k'arashe tana murmushi. Daddy baze iya kwatanta irin farin ciki da murnan da kalamun Mummy suka sanyasa ba. Da murmushi kwance fal a fuskansa ya mik'a hannunsa ya rik'o nata "Thank you so much Hjy Surayya I can say my life has never been better until I met you, Allah ya cigaba da miki albarka ya kuma barmu tare."

"Ameen Alhj you're welcome."

"Kinsan wani abu?"

"Seka fad'a."

"I love you" yana sanar da ita bata san lokacin da ta fashe da dariya ba "Ji Alhj de, yaushe kuma muka fara wasan nan?"

"I'm serious Hjy Surayya saboda bana fad'a miki doesn't mean I don't love you, I love you like the day I just met you Hjy Surayya never forget that."

"Thank you Alhj."

"Thank you kad'ai? Ni bazaki cemin I love you in return ba?"

"Ka ga La'asar ya kusa gara ka tashi ka fice muyi niyya duka."

"Yau kuma? Toh sekin fad'a min zan bar nan."

"Lallai kuwa, nikam ka ga tafiya na" bata kai ga mik'ewa ba ya dakatar da ita ta hanyan kama hannunta. "Alhj ka sakeni mana!"

"Nak'i"

"Zan tara maka jama'a fah."

"Ni d'in Hjy Surayya? Ni d'in naki?"

"Toh ka sakeni."

"On one condition."

"Name it."

"Yaushe zaki dawo gida? Ina matuk'an kewarki."

"Kai da zaka k'aro amarya kode ka manta ne?"

"Amarya daban ke daban so yaushe zaki dawo keda 'yan'yan namu?"

"Zamu dawo karka damu."

"Promise?" Kai zalla ta gyad'a mar sannan ya saketa "Toh se anjima ki gaishe mun da Nazeefah da Khaleefah."

"I'll semun sake magana." Da haka ta fice ciki inda shi kuma ya mik'e ya yi tafiyarsa.
D'akinta da Nazeefah ta wuce direct inda ta tarar da Nazeefah mik'e kan gado kaman maciji ta zurfafa a cikin tunani ko makaranta tak'i fita. "Tashi ki zauna muyi magana" Mummy tace da ita bayan ta zauna a gefenta ta bakin gadon. Ba gardama ta mik'e ta zaune.

"Ina son ki saurareni da kunnen masu hankali a matsayinki na musulma me kar6an k'addara me kyau ko akasin sa." Tun anan gaban Nazeefah ya fara bugun d'ari-d'ari dukda cewan bata fahimci inda Mummy ta dosa ba.

"Ki sani cewa komai na faruwa ne bisa dalili fatan mu kawai Allah ya sa hakan kawai shi ne mafi alkhairi a gareku gabad'aya."

"Mummy ban fahimce kiba shin mey kike fad'i? Meya faru?"

Rana D'aya Where stories live. Discover now