Dont forget ur vote really count*
*💦WACECE ITA?💦💦*
*PAGE 20*
*NA UMMU ZAID👌🏽 ** se yamma likis muqaddas yasamu yashiga gida saboda seda yayi biye biyen gidan abokansa,knucking yayi a bakin gate din gidan, baba megadi yabude masa, baba megadi cikeda mamaki yayi murmushi yace: welcome sire, muqaddas ya amsa, sannan ya amsa jakarsa suka shiga cikin gida, gidan seyamasa fili kasancewar ya dade bezoba, shiga main parlourn daze sadashi da shi da dakin umminsa yayi, da sallama ya shiga parlourn yanemi waje yazauna kamar wani bako yasan be kyauta b, ummi tafito da hijab ajikinta da alama daga wanka tafito, ido biyu tayi da yaron ta wanda taga yamata duhu batace komae ba tajuya takoma bedroom din ta don bakaramin fushi tayi dashi ba, far'ar fuskarsa ce ta koma ganin irin tarbar da mahayfiyarsa tamasa, binta yayi dakin tareda tsugunawa har kasa yasa gwiwoyinsa akasa," ummi am sorry nasan kinyi fushi dani kiyi hakuri kiyafemin please! Wlh ummi ba'ason raina bane" kauda kanta tayi gefe guda ya raraffo tareda saka kansa a cinyar ummi, besan sanda hawaye yafara zubo masa ba, jin dumin hawaye tayi a cinyarta yasa tayi sauri tadago Kanta, muqaddas meyafaru dakai? Memuka maka hka kamanta damu? Tafada cikeda kewa da tausayin yaron nata, muqaddas yace" ummi am lost, ki yafemin bansan abinda ke damuna ba ummi" dafa kanshi tayi tareda fadin" tashi hakanan nayafe maka jeka kayi wanka kaci abinci, tukuna kajiko?" Murmushi yayi sannan yatashi yashige toilet din ummin yayi wanka yahado da alwalar sallar magrib don 5:30 yayi, ummi tacika masa gabanshi da abinci, macaroni sukayi da Irish potatoe jollof me veggies sekuma zobo me sanyi, tace kaci abinci kajiko? gyada kai yayi sannan yaja plate din yasoma ci, yayinda ummi ke kallonsa kamarba muqaddas din taba, yayi baki ya rame duk kwalisar babu, hira take Dan Jan shi dashi yayinda yake amsa mata, kammalawa yayi yayi hamdala ya janye plate din, ummi ina abbu dakuma nuwaira, ummi tace: abbuh yaje kano yau ze dawo insha Allah yana hanya damukayi waya, nuwaera taje makaranta yanzu zaka ga sundawo, gyada kai yayi yace" ummi bari naje dakin ammi( abokiyar zaman hajiarce kasancewar kowa da part dinsa ) tashi yayi yaje dakin ammi, gaysheta yayi ammi tace " muqaddas laifin me mukayi maka haka?" Sunkuyar dakai yayi yace bakomae ammi, muqaddas kai ba yaro bane kuma kaga Kaine babba duk gidan nan, koba abbu Kaine zaka zama jagoran gida, kuma mu iyayenka ne kadinga kula kajiko? Amsawa yayi da toh ami yi hakuri sannan tacigaba da bashi shwarwari da nasihu kan kula da hakkin iyaye, daga nan suka cigaba da hira,don dama shie Dan gidan ammin ne kusan komae dakinta yakeyi, tambayarta yayi" ammi ina khaula da murjana,"aikduk yau suna school kasan exams yakusa gashi abin she ahankali, har ansaka ranar murjana dakuma nuwaira, muqaddas yadago dasauri " yanzu ammi har ansaka ranar sisters dina ba Wanda yafada min?" Ammi tace" muqaddas abbuh yayi fishi sosae da abinda kayi, ko ankiraka baka dauka don haka yahana kowa kara kiranka, jikin muqaddas yayi sanyi matuka donshi babu abinda yafi tsana irin fushin iyayensa, shiru yayi yayinda ammi kedan jansa da hira, sallama akayi dagudu yammatan sukashigo tareda rungume muqaddas din, ammi tace kaji sakarkaru ku baku San kun girma bane wai? Kada Ku karyashi mana, dariya yayi tareda jin farincikin ganin kannensa, nuwaira ta zumburo baki tace" bros shine kamanta damu ko munyi fushi, sisters meyasa ma mukai murna damuka gansa? Murjana ta amsa nidae bana fushi da bros dina namasa uzuri, cigaba sukayi da hira yayinda ammi tashiga cikin daki tabarsu suna shiriri tarsu, cikin farin ciki sosae suke musamman muqaddas don Rabon dayaji ya sake haka yamanta, lallae bature yayi gaskia dayace" home sweet home" bahuashe kuma yace" kowa yabar gida gida yabarshi" karan horn din mota sukaji su nuwaira suka kwasa da gudu suna fadin" ga abbuh ga abbuh" yayinda hakan ya haddasa ma muqaddas faduwar gaba, ammi ce tafito daga bedroom cikin kwalliya ta alfarma takalli muqaddas " lapia ba kaje ka taro babnku ba kana zaune? Oya tashi mun mutafi, abbun ne a tsakar gida yayinda yake magana da yaransa kamar sa'ansu don shi mutum ne mesakewa da iyalansa, ammi CE rike da hannun muqaddas yayinda ummi take kusa da abuh rike da yar jakarsa itama taci kwalliyarta, abbuh yadaga kai yakalli muqadass tareda nunashi, ammi me wannan yaron yazoyi agidana?" Ammi takalli muqaddas daya sunkuyar dakansa kasa yana share hawaye lokaci zuwa lokaci yayinda ummi ta kauda kai kamar batasan me akeyi ba, ammi ta kara rike hannun muqaddas tareda karasowa gaban abbuh," haba abbuh kaida yakamata ace kafi kowa murnar dawowarsa sekuma ace Kaine zaka fadi haka? Ae in zucia ta baci hankali ke nemosa, ka tsaya Dan darajar annabi ka saurari uzurinmu inbeyiba sekamana koma meye" abbuh cikeda Bacin rai yadaka mata tsawa" sauda nikike fadawa abin da yadace inyi? Yaron nan yabarmin gidana ko kuma kibishi!, ammi bata kara cewa komae va tama muqaddas signal yaje yaroki abbunsa, kneeling yayi akasa yace" abbuh Dan darajar annabi kayafemin wlh ba laifina bane kayi hakuri, abuuh yakauda kai gefe guda, yayinda suma su nuwaera suka tsuguna kamar yanda suka yayansu yayi suka tayashi rokon abbuh, shiru abbuh yayi dan weakness dinsa a duniya yaransa ne yana matukar sonsu ssae, kallonsu yayi yaga su matan harsun fara kuka don basu taba ganin fushin abbunsu haka ba yayinda uban gayya ke share hawaye, kutashi nace" khaula tace abbu bazamu tashi ba harsae ka yafema brother dinmu, abbuh yace na yafemasa kutashi, tashi sukayi suna murna yayinda muqaddas ya rungume abbu yafashe da kuka, abbuh yace" ya isa haka kukan namenene? Sannan yajashi suka Shiga parlourn abbun, sallah akayi yayinda aka hallara a parlourn abbu akayi dinner ana ta raha, muqaddas yayi shiru bayacewa komae, abbuh yace " son lapia kake kuwa? Naga duk ka canza min meke faruwa?" Dukar dakai kasa yayi sannan yace abbuh daga Lagos nake gidan alhaji Ahmad Muhammad al'ansar, abbu ne yace" ikon Allah lapia daiko?, nan muqaddas yazayyanowa iyayensa labarin duk abinda yasani gameda matarsa davesan haryau wacece ba, innallilahi wa'inna ilaihi rajiun, ammi tafada yayinda ummi takasa cewa komae, abbuh yace" yanzu muqaddas kace bakasan zeenatu matar kaba? Muqaddas ya amsa Abba haryanzu am so confused wlh bana tunata, kannensa ne suka fara kuka don yanda sukeson matar yayan Nasu suma sunyi mamaki da tsawon wannan shekaru suka kasa tunata se yanzu, ummi tadaka masu tsawa" kutashi kubama mutane waje saboda abin kuka Ku baya muku kadan kuntasa mu agaba kuna mana kuka!" sum sum suka tashi don sun San halin ummi bata wasa da yara don agidan ita kadae suke tsoro, parlourn yarage daga abbuh se muqaddas, ummi da ammi, abbuh yaja numfashi, tabbas muqaddas zee matarka ce Nima wlh Sam namanta Rabon damuyi magana da general, akwae wata kullaliya a Alamarin nan, yakamata mushirya cikin satin nan muje Lagos din batan mutum baa bin wasa bane, ummi CE tace Niko ammi kamar zeenatu tanada ciki aiko, salati ammi Takara sakewa tareda fadin" hasbunallahu waniimal wakeel tabbas ummi anyi haka lokacin dasuka zo karshe nan cikinta yakusa Shiga wata 8, muqaddas neya kuma Shiga tashin hankali, rudani gameda bakingciki, ni meke faruwane dani? Tsugunawa yayi tareda fashewa da kuka, abbuh, ummi Dan Allah kutaymake ni wlh bansan WACECE ITA ba, bana tunata kaina yana min zafi, kuka yakeyi kamar ransa zefita abbuh ne yarikesa muqadass look at me! , dakayar muqaddas ya kalli abbuh, yana me zubar da hawaye gwanin ban tausayi, itako ammi tuni tasoma kuka ganumin Dan gidanta halin dayake ciki, ummi ko dauriya takeyi bata fashe da kuka ba abunka da Fulani kuma gashi muqaddas Dan fari ne , abbuh bansan taba wlh kuwa abbuh! Abby, yacigabada kwantar masa da hankali, Wanda ciwon dayafarayi a gidan general Ahmad yakara tasomasa tuni yafara convulsing idanunsa suka kakkafe, iya tashin hankali wanan family sunshiga, wai meke faruwa da dansu ne? wannan wane irin masifa CE, umni CE ta tashi tabar dakin cikeda tashin hankali, yayinda ammi ke kokarin tofama muqaddas din addua Dan yau convulsing din yadade, abbuh yakalli ammi maza dauko min first aid box dina kamar inada anti seizzure nabashi dayake abbuh tsohon likitane dasauri ammi tadauko masa nan da nan yabashi iv , Wanda bema kai ga cire allurar ba convulsing din ya tsaya Yakama barci.............. Abbuh yakalli ammo dauriya kawae yakeyi yace " yaushe yaron nan yasamu farfadiya, wanna balai had INA?" Ammi cikeda jimami ta tashi ta dauko pillow tadaura kan muqaddas akai Wanda barcinsa kawae yakeyi.....hayhuwar sa ce kawae batayi ba amma yanda takes on muqaddas ko yaranta bata Nuna masu soyayya haka... 💦💦WACECE ITA?💦💦 *PAGE 21* NA UMMU ZAID👌🏽👌🏽 *kuyi hakuri dajina shiru kwana bIyu, wayarce tadan sami problem nagode da kulawarku, love u all ba iyaka* Yaune ranarda zeenatu zata koma wajen malam me dara, don haka da sassafe tashirya takama hanyar giwa, bata wani sha wahala ba ta isa gida, lokacin ta ta radda dashi yana karatun alqurani, iso akamata dakinsa, tsugunawa yayi daf da bakin kofa tagayshesa ya amsa tareda fadin" sannu da zuwa ya hanya?" Lpy lau tabashi amsa sannan malam shuaibu me dara yacigaba" ya jikin naki kina ganin wani canji atare dake kuwa?" Zee ta ansa alhamdulilah sedae haryanzu bana tuna komae" malam shuaibu yace" ae ciwo lokaci daya yake Shiga amma sauki se a hankali yake zuwa insha Allah akwae alamun nasara, dauko magangunan yayi ya mika mata tareda mata bayani, godia tashiga jero masa sannnan ta tashi takama hanyar Kaduna.......... Zeenatu ba wayar ki bace ke kara ko?" Cire hannunta tayi daga cikin wanki sannan tasamu Riga guda daya ta goge hannun, ko kan ta daga wayan har tsinke don hakane ma tasake kira luby CE , dagawa akai luby tace albishir, zee da sauri tace goro, luby tace gamu nan zuwa Kaduna muna hanya yanzu!" Cikeda murna zee tace Allah yakawoku lpy shine baki fada min ba seyanzu?", luby tace surprise visit ne banyi niyyan fada miki ba da sedae kiganmu, abban Abdul ne ya matsa wai don a ajiye mana abinci, hira suka taba sannan sukayi sallama, zee ta fita tafada ma inna, inna ta rike baki lallae zeenatu yau aminiya zatazo baki yaki rufuwa Allah ya kawosu lpy aeseki gama wankin naki kifara hidimar dafa abinci ko'n kinga suna zani Kansu xo, zee ta amsa da toh yanzu kuwa hajia inna, tareda komawa wajen wankin ta, nan da nan tagama cikeda doki ta dora masu abincin rana shinkafa da wake da MaI da yaji tayi ta yanka salad tareda dafa dafaffen kwai ta saka a food flask don tun kan tadaura inna ta tafi gidan suna da bawan allah, wanka tafada tana fitowa tadauko wata Riga da skirt na atmafa small Holland CE maroon da golden yanada ga cikin kayan da lubyn ta aiko mata dasu, farar powder kawae tashafa tareda murza kwalli da Dan wet lip abakinta ba karamin kyau tayi ba tana cikin ninke kayan data cirene taji sallamar su luby Wanda da gudu tafito ta rungume luby Rabon dasu hadu wata 5 kenan sedae waya, daukan Abdul tayi tashiga cikin parlourn inna tana mamakin kara Girman da Abdul yayi gaysheda luby tayi, luby ta amsa da lpy lau, wae maman bawan Allah meye sirrin ne? Kinga yanda kikyi kyau wai, zee tayi daria "banason zaulaya luby kinfara kenan ko? Cigaba sukayi da hira sannan zee ta tashi tadauko mata ruwan sha, itako se kallon zee take yi aranta tana fadin masha Allah Allah yayi halitta, tabara kallahu ahsanal kalliqeen ( adduar da yakamata ace muna yi kenan yayinda mu ka ga mutum yamana kyau saboda kai Baka san bakinka ba, Allah yasa mudace)zee tace wae INA abban Abdul naga be shigo bane, luby tace yana waje yana gaysawa da mutane, nidae bari nasauke farilla naci abinci yunwa nakeji, Abdul kuwa sarkin labari se surutu yakeyi kasancewar bakin shi yayi saurin budewa ba kamar bawan Allah ba shi Sam bashida mgn barshi da yawo dae, zuba masa abinci tayi tana bashi yace, mumy ni dakaina", daria tayi sannan tasaukeshi sdaga jikinta ta tura masa abincin, luby na idarwa sukaji sallamar ishaq don haka zee tajanyo hijab donta tasaka shigowa parloun yayi suka gaysa da zee sannan ta tashi tadauko plate da spoon takawo masu tabasu waje dn suci abinci. Da yamma inna tdawo tace "jamaa kunjini shiru ko wlh biye biye nayi ziyara, luby tagysheta suka cigaba da hira lokacin abban Abdul ma yafita gari,inna tauyi gyaran murya tace" munga tsaraba mungude Allah saka da alhery Baku gaJia da hidima" luby ta amsa bakomae inna Kadan ne bayawa, inna tacigaba"lubabatu kinsan nadaukeki tamkat diyata Dana hayfa cikina ko? Don haka yazama dole namaku fada a matsayin mahaifia yakamata ace kunje kungayda gwaggo, mahayfiarsa ce duk laifin datayi bedace ace yau wata 7 ko leke ishaq be kumayi ba,ke matarsa ce yakamata ki mass nasiha Da lallabashi akan hakkin iyaye kiyi hakuri nasan anbata maku kinjiko?" Luby datake sauraron inna tadago tace" wlh inna tafia nan ma da niyyar zamuje Dan bushiyar mukayi, dakyar na lallabashi ya amince, ba irin maganar dabana ma abban abdul, amma insha Allah gobe can zamu, inna cikeda da jin dadi tace "madallah da mace tagari, ae ishaq yayi dace da mace Rashin fahimtane kawae irin na yaya , haka yafi ae kicigaba da hakuri baa taba cewa wane gaskiarka ta kare sedae ace karyar ka ta Kare " luby tace "hakane inna sannan suka cigaba da hirarsu ita dae zee najinsu, da daddare bayan sun kwanta luby take tambayar zee cigaban da aka samu gameda magani, zeenatu tabata labarin yanda akayi, luby tace insha Allah zaa dace addua itace takobin mumini, cigaba sukayi da tattauna matsalolinsu dan basa boyewa juna sirrinsu, yanda suke da luby zaka rantse yan uwane irin shakikae dinnan Dan ko abban abduk mamakin wannan shakuwa tasu yakeyi.... Dasafe su luby suka shirya suka kama hanyar hayin danbushiya, Har bakin mota tamasu rakiya tanajin kamar kada sutafi Don luba macece me shiga rai kwrae........................... bangane ba malam, wane irin aikine haka kwana nawa mukayi dakai uku ko?, amma saboda ka rainamin wayau Kaine har kwana 5 muqaddas wae yaushe kafara karyane iye!? Cikeda tsoro yadaga ido yakalleta yace" babe am sorry machine din dmuke gyara ne bamu kammal gyarawa ba kuma kohutu bamu samu ba yanzu hka ance ana iya Neman mu a koda yaushe, shiru tayi tanaso ta takaranta gaskia abinda yake fadi shiko muqaddas se zufa yake sharewa yarasa yanda akayi yanzu yake mata karya bayason tasan yaje gidansu SBD sanin halinta kiri kiri take nuns batason iyayensa, kamar wani wawa hka ya matso kusa da ita yanason shafata, dan taba mata fuska yayi Kadan tareda saurin janye hannunsa kamar wanda electric shock Yakama, jin bata masa maseefar data saba bane yasashi janyo ta jikinsa yana dan sunsunar wuyanta tareda lasar gefen wuyan kamar yasamu alewa sosae tafara rikice masa saboda mardiyya bata da wahalar ansar sako kuma gashi kwana 5 basu gamu ba a matse take sosae hakanne yasa tayi saurin rikemasa kai tafara masa wani hot kisses,daukanta yayi yajefa kan gado kamar wani tsohon zaki yacigaba da romancing dinta tako ina uhmmm abin sirrine irin na maaurata nidae dasuri najanyo masu kofa......................... Abbuh ne zaune a office din malam ar'riyad yana masa bayani akan abinda yafaru da muqaddas din, shiru malam yayi sannan yayi gyaran murya "gaskia prof danka yana tareda sihiri sosae akansa amma gaskia sedae nahada ka da wani malami a kano don aikin nan Nada matukar wahala sosae, ajiyar zucia abbuh yayi yakalli malam"to shikenan babu Matsala shiyasa nake Sonka malam inba zaka iya Abu ba kana fada ma mutum gaskia bakamar wasu malaman ba da saeda suyita cin kudinka, kabani number wayar mutumin zan kirasa inma takama naje zanje dakaina insha Allah, malam ar'riyad yabama alhaji Ibrahim number wayan mutumin sannan alhajin yamasa godia yatafi, da dare bayan ya gama cin abinci yakira number malam yahuza, daga dayan bangaren akai sallama "assalamu alaikum" abbuh ya zmsa da "waalaika salam", sannan yayi masa bayanin abinda ke akwae, malam yahuza yace kwarae dazu ar'riyad yamin mgna zaka kirani, amma maganar nan bata waya bace alhaji zefi kyau kuzo tareda Mara lafiyan, Godia abbuh yamasa tareda fadin" yaushe kenan zamu zo?" Malm yahuza yace" eh toh kuzo ranar asabar kaga nan da kwana biyar kenan " godia abbuh yamasa sannan ya katse wayan, kallon ummi yayi datake saurarensa yamata bayanin abinda ake ciki, amsawa tayi da abbuh Allah yabada nasara yakuma yaye wannan musiba, seka kira muqaddas din kafada masa yashirya gameda tafiar, amsawa yayi sannan yadauki wayarsa yayi dialling number din muqaddas, seda takusa tsinkewa aka dauka cikeda masifa mardiyy tace" haba haba!uban waye yake kiran mijina da darenan!!? sarae tasan waye yakira amma tsabar rashin kunya yasa ta fadi haka, shiru alhaji Ibrahim yayi kamar ruwa yacishi saboda tsabar kaduwa, yace uban muqaddas din ne, hararar wayar tayi kamar abbun nagabanta tace" kayi hakuri yayi barci bazae sami damar ansa wayarkaba,kit! takashe wayar, shiru abbuh yayi da waya a hannu cikeda mamakin abinda mardiyya tamasa, Ashe yarinyar nan bata da mutunci haka,? ummi CE takallesa tace abbuh lafia naga kayi wani iri?, bata labarin abinda mardiyya tayi masa yayi, cikeda Bacin rai ummi tace, kagani ko? abbuh niban san meyasa na tsani shegiar yarinyar nan ba, kwata kwata bata da kunya bata da tarbiyya, Allah yasani ita nake zargi da duk abinda kefaruwa abbuh, abbuh ya katseta" haba maryam kidaena fadin hka zato fa zunubi ne koda yakasance gaskia bana sonki da zargi, in halinta ne ae zata tsince abinda ta shuka agaba, muqaddas adduarki kawae yake bukata ummi, gobe nakirasa in na tabbatar yafita aiki. , cigaba yayi da kwantar mata da hankali shida akama wa rashin kunyar ma har ummin tafisa jin haushi , dama ummi macece dabata son raini Sam akwae ta da zucia sosae...

YOU ARE READING
WACECE ITA??
Spiritualta wayi gari ne da hayhuwar yaron daba tasan wanene ubanshi ba, kwatakwata kwatakwata bata iya tuna ryuwar da tayi abaya, tirkashi littafin wacece ita littafine daya kunshi soyayya, rudani, tashin hankali dakuma tausayi, kubiyoni dan jin wannan kaya...