CHAPTER SIX

2.5K 134 4
                                    

*💦WACECE ITA💦💦*       
*page 13*
*na ummu zaid👌🏽                                     .
..Bayan kwana biyu kawu isah ya dira a Lagos, taxid yahau daga airport zuwa GRA olusegun obasanjo street, me taxi yadauki kawu suka isa unguwar, unguwar me kyauce sosae ga yalwar bishiyoyi hakan yasa weather din unguwar takeyin kamar raba raba, tsayawa yayi a kofar gidan tareda kiran  no din hajia sakeena, hello hajia gani na iso kofar gidan, daga daya bangaren aka bada amsa , to bari nakira masu gadin sesu shigo dakai sannu daxuwa, yauwa ya amsa tareda kashe wayar, dokar gidan alhaji Ahmad ce baa budema mutum gida kai tsaye Seya kira mutanen gida saboda babban mutum ne sosae, wani megadine yaleko sanye da uniform din sojoji, yace yashigo tareda daukar masa jakar hannunsa yabi kawu isah abaya, gidane babban gida sosae me cike da yalwar bishiyoyi a Jere har zuwa ainihin main part din gidan, shiga kawu isah yayi da sallama tareda shigewa gidan, oyoyo oyoyo ga kawu ga kawu! Hajia sakeena take fada cikeda murnar zuwan kawun NATA, zama yayi a daya daga cikin kujerun parlour din sanan hajia sakeena tafara gayshesa cikeda murnar ganin kawun NATA, kawu ya hanya ya mutanen safana din? Lpy lau sakeena munsameku lpy daeko? Lpy lau, ta amsa tareda kiran me aikinta takawo mawa kawu abinci da ruwa, kan kace meye ancika gaban kawu da abinci na alfarma, rike baki yayi sakeena manya duk nikadae? Murmushi tayi batareda tace komae ba tafara zuba masa abinci, bayan ya kammala ne ya umurceta data Kaysa dakin masauki yadan huta yayi sallah, haka kuwa akai, da dare bayan Alhaji ahmad yadawo sungaysa da kawu isah akayi dinner sannan kawu isah yayi gyaran murya, to alhamdulilah ke sakeena kinkira ni kwanaki dawata magana me matukar daure kai, yanzu kafin muje ga maganar mu ina yaran suke? Cike da jimami hajia tabashy amsa haseen yana gidan sa shida matarshi itakuma nafeesa tana makaranta a can england, kawu ne yajefo mata tambaya" to itakuma zeenatu fa? Shiru. Sukayi itada alhaji Ahmad sannan alhaji Ahmad yadan nisa yace; kawu mudae bamu da wata diya wae ita zeenatu yaran mu biyu ne kawae, salati kawu yakara ja innalilahi wainna ilaihi rajiun!'"  wannan masifa wace irice take shirin kunno mana? Kusaurare ni da kyau alhaji zeenatu tana daga cikin yayanku asalima itace takebima haseen, kuma kunyi mata aure kwanaki, to nayi dan aiki akan wannan lamari naga kamar cewa sihiri akayi dayasa kowa yamance da ita, Nima nan datake mutuniyata ce nakan kirata lokaci zuwa lokaci amma kusan shekara da rabi kenan senayi kamar nakira se shaf amantar dani, lallae wannan aiki bana wasa bane, sudae su hajia shiru sukayi cikeda tashin hankali dan haryanzu maganar da kawun keyi besa ko alama sun tuna dawata zeenatu ba Sam, kallon kallo suka fara hajia sakeena tace: toh kawu kamar yanda kace zeenatu diyar muce wlh nidae bansanta ba, kawu ne yayi shiru can yace ina zuwa, tareda tashi Dan dauko jakarsa, jakarsa yadauko sanan Yakoma yazauna inda yatashi yazage zip tareda dauko wasu hotuna saboda tabbas yasan zaayi haka, yamika ma haija sakeena, tafara dubawa hannunta ne yafara rawa saboda ganin hoton zeenatu datayi, subiyu ne ita da hajiar suka dauka, kan zeenatu na kirjin hajia suna daria, lokacin data gama makaranta a California ne, se dayan hajiarce da zeenatu da alhaji dasu haseen, hannunsa sakale da juna su biyar din cikeda farinciki, se dayan na bikin zeenatu ne tasha lifaya gata ga mamarta dakuma megidanta muqaddas, gaban hajia ne yatsananta faduwa dan haryanzu datake kallon hoton zeenatu tana hawaye takasa gane ta kwata kwata, gadae kama nan sunayi da ita kamar an tsaga kara kuma tasan Tabas jinintace amma kwata kwata bata iya tuna rayuwarsu tabaya dasukayi da wannan kyakyawr diyarta, alhaji ahmad ne ya amshe hoton daga hannun hajia sakeena yafara kallo shima rudanin yashiga batareda ya gasgata abin da yake gani ba, shima he was just getting confuse, mikama kawu hotunan yayi tareda  zubamasa ido danshifa har ga Allah besan yazeyi describing wanan rudanin dayashiga ba, itako hajia sakeena tunani ta zurfafa ciki Dan sota take ta tuna wannan diya tata, amma takasa tuna komae kanta ne yafara ciwo sanan takoma tazubama kawu isah ido, kawu shiru yayi kana ya nisa to yanzu ku ba lokaci bane yanzu na azauna ana barci tsayuwar dare da sadaka su zamu saka agaba, kuma insha Allah ya kusa kawo karshen wannan Abu yanzu dae zama zamuyi mudage sanan zansa a gida afara aiki akan lamarin nan zaayi saukar alqurani a gida, masallatae ZAmU bi muyita sadaqa da Neman sauki wajen rabbul izzati, zan zauna daku nafara aiki akanku har naga yanda hali zeyi, kara bude jakarsa yayi yadauko wata yellow Jerican yabama hajia ga wannan sakeena keda alhaji ahmad zaku dinga amfani dashi kudan diba kadan Ku kara ruwa awanda kuka diba kushafe jiki sannan kusha, sekuma kurinka yawan ambaton inna ma'al usri yusra, kunji ko? Gyada kai sukayi kamar kana nan yara Dan duk su biyun sunkasa mgna sabida rudewa da ta'ajibi.....                       *****""Yau watanmu uku a asibiti, jikin abdulshakur alhamdulilah yayi kyau yadan ciko ba kamar sanda muka kawoshy ba kasancewar kwash pap ake bashi via nasogastric tube(robar hanci) yanzu kam alhamdulilah dakanshy yake amshewa kuma yanacin abinci sosae, doc zaid ne yashigo dakin da sallamarsa zee ta amsa yayinda take yanke mawa bawan Allah kumba, doc zaid yajawo kujera yazauna yana fuskantar zeenatu wacce tunda tadaga kai takallesa bata kuma kallonsa ba tamayda hankali tacigaba da abinda take yi, kura mata ido yayi kur, tareda daga baki ya yi mgn" yanzu zeenatu fisabillilah Dan nace inasonki shine zaki bata rai haka? Zee ta kallesa tareda kauda kai gefe daya, " gaskia zaid bazan boye maka ba, yanzu baka tunanin inna san yanuwana yakasance kuma inada miji gaskia kuma kaga soyayya bezae yiwu tsakanin mu alhali ina bazawara kai kuma kana saurayi....... Katseta yayi , zee I will not quit wlh harsae kin amshi tayin soyayyayata wlh! Kallonshy tayi tareda mamakin wannan ikon Allah, kamar ana soyayya dole, zee ce tayi murmushi tareda cewa, zaid kada kamanta ayanxu koda agaban iyayena nake amatsayina na bazawara inada damar nazaba ma kaina mijin danakeso balantana kuma yanzu, makauniyar soyayya Sam batamu bace nidakai kallonta yayi tareda kwantar da murya, am so so sorry zee I shouted at u, sonki yanaso ya haukatani kitaymakeni, sake kallonshy tayi taga inta biyewa zaid awajennan haka zatayta zama, " zaid kayi hkr kabari har insan yan'uwa na tukuna semuyi mgna tunda nidakae babu Wanda yasan daedae, dakyar ta lallaba zaid ya hakura, yatafi kwana 2 suka kara a asibiti aka sallamesu........                                                  💦💦WACECE ITA?💦💦        *PAGE 14*                      *NA UMMU ZAID*                                     Boka karkuzu ne yake zaune kogon shi ransa a tsananin bace sanaddiyar zuwan da Emma yayi wajensa duk a kone ko magana bayayi seda kyar(aljanin daakai fama dashy na zeenatu kwanaki) kara karkuzu yasake ahhhhhhhhhh!!! tareda kifar da kayan dake gabansa, danshi duk cikin aljanun dayake aiki dasu bawanda yafi ji dashy yakeso irin emma, zumbur yayita suddabaru sannan Sega wata mummunar halitta nan a gabamshy boka karkuzu yace "kayi, hakuri Emma bansan zaa iyamana wannan shirin ba, Emma dayake cikin ciwo yace narantse da kanka tabbas badan amincin dake tsakanin mu ba tun kakanka dase na halaka wacce tasa akayi mata wannan aikin,   shiru boka karkuzu yayi tareda sassauta murya yace: kafadamin kome kake so indae har zan iya kozanyi yawo tsirara zaka sameshy Emma, Emma yayi shiru kadan sannan yakalli boka karkuzu cikin wata iriyar mummunan yanayi yace: yanzu kaga nidakyar nake iya magana banda lapia  babu abinda nake bukata face jini! Jini! Boka karkuzu ne ya barke da wata arniyar daria sanan yace" jinin wakake so yanzu kasameshy ka gama,?"  Murmushi Emma yayi Meban tsoro yace" jinin dan mardiyya nakeso!" Boka karkuzu yakuma barkewa da mahaukaciar daria sannan yatamke fuska jeka abinka Emma zankiraka kamar kasamu kagama( to masu zuwa wajen bokaye kuyi hattara Dan Wlh duk Wanda zenemi taymako daga aljanu karshe zuriarsu suke komawa su cutar kunga babu riba ga shirka sannan ga cutar da zuria, Allah yasa mudace!), fit Emma yabace tareda sakin wani arnen nishi dayafara amsa kuwwa acikin kogon) washegari boka karkuzu yakira mardiyya, cikeda yatsine ta dauki wayar kasancewar ganin sunan teacher datayi ko baa fada ba tasan wanene, danhaka dauka tayi ta amsa hello, daria boka karkuzu yasaki me muni datasa mardiyya cire wayar daga kunne, lpy daiko ? Amsa yabata da "babu lapia mardiyya, asirinki nagab da tonuwa ja'ira, kwarewa mardiyya tayi tafara tari ba kakkautawa seda tabari yadan lafa mata tace, karkuzu duk cikin wani malami danake aiki dashi aikinka yafi nakowa kyau, kayi duk abinda zakayi kada asiri na ya tuno kona wane zan baka, daria karkuzu yasheke da ita yace" mardiyya bakiso asirin ki ya tuno ko? Dasauri ta amsa da eh hartana wani kada kai kamar lizard,karkuzu yace" ki kwantar da hankalinki jini Muke so bakuma nakowa ba face na danki suhail! What! mardy tafada da karfi" karkuzu yanzu kai harsenabada dana asirina ze rufu? Dan Allah ka rufa min asiri insamo maka kowaye amma banda Dana, karkuzu yakwashe da daria, "mardiyya wanann shikadae ne zesa asirinki yaci gaba da rufuwa Dan haka kinga tafiata, kit yakashe wayarsa, zufa mardiyya tafara sharcewa tareda safa da marwa a dakinta, na shiga uku meke shirin faruwa danine na Boni na lalace! Dasauri tajanyo waya tareda dialling number din aminiyarta sholi,sholi nadauka tace ya akai mardy? Batareda ta tsaya gaysheta ba tafara zayyano mata damuwarta cike da tashin hankali, sholi ce tafashe da daria sannan tadaure fuska, ke haryanzu mardiyya na lura dunia bata baki mukami ba dasauranki yanzu saboda wanann ne kike kuka haikam? Kada kimanta Nima yayana 3 na salwantar saboda rufin asirina meyasameni? Kikwantar da hankalinki ki amince tareda mika masa suhail din, inbanda abinki ai ba wuce lokacin hayhuwar kikayi ba, kisake zazzago su San ranki(kamar su suke bamawa Kansu hayhuwar), ahaka sholi taytama mardiyya famfo har ta amince davada jinin danta suhail( wani sahabi ke cewa " ni nafi tsoron shaydanin mutum akan shaydanin aljani domin shedanin aljani kana iya Neman tsarin Allah dashy ya kauce, shi shedanin mutum baze rabu dakai ba har se ya cimma burinshy akanka" haka yake yanuwa mugujema zama da munanan kawaye don zasu iya kai mutum su baroshy a dokin danasani. )              Zee, yakamata kishirya kitafi Kaduna tunda yanzu dae Abdul din yaji sauki, vaxe yiwu muyita zama ba haryanzu batareda munsan abinyi ba gaskia, luba ce tafada yayinda zee tayi ajiyar zucia gaskia ne, luba nima saboda abdulshakur ne yasa banyi magna ba, luby tace" toh bari baban Abdul yadawo semuyi mgnar Dan inna rannan takira tana ta fada wae mun shashantar da zance" tattaunawa suka cigaba dayI har abban Abdul yadawo bayan sallar ishai, bayan yaci abinci ne luby kecewa" abban Abdul wae ya maganar zuwan maman bawan Allah Kaduna ne?" Bata amsa yayi wlh abin naraeni my dear insha Allah satin nan zata tafi lokaci ba jiran mu zeyi ba, hira suka cigaba dayi tareda tattauna irin na masoya.                              *** Yaune zeenatu zata tafi Kaduna dan haka su luby suka tayata kaita tasha tareda biyan kudin mota, alhery sosae suka mata sannan suka sata a motar ksta zuwa Kaduna garin gwamna, har kuka seda luby tayi Dan gani take kamar zeenatun bazata dawo ba, sabo inji bahuashe yana cewa turken wawa, tafiaar awa uku ce tasadata da Kaduna, kasancewar anmata kwatancen gidan tana sauka ta tare bus zuwa tudunwada, da kwatance zeenatu tagane gidan inna dake unguwar tudunwada layin kosae. Assalamu alaikum! Zeenatu ce tayi sallama yayinda inna ta amsa waalaiki salam, lale marhaban da bawan Allah, zee tafadada faraarta inna shikadae kika sani, murmushi inna tayi atoh shine dae megidan, sannunku da zuwa, yauwa inna INA yini? Lpy lau zeenatu ya gajian hanya, zee ta amsa da lapiaya lau sannan ta tashy don takawo mata abinci da ruwa, zeenatu tafara cin abincin Dan cike take da yunwa tana dan bama bawan Allah Dan ya isa fara cin abinci, bayanta gama taje takai kwanuka wajen wanke wanke tayi alwala tafara ramuwar sallah.....                      💦💦  WACECE ITA💦 *Page15*             Na ummu zaid👌🏽👌🏽                      Washegari malam sani yaxo tareda magungunansa, zeenatu CE zaune dan nesa da  malam yayin da inna kedaga dokin kofar daki zaune tanata fifita kasancewar lokacine na zafi, malam sani yafara mgna" to maman Abdul ga wannan tareda mikomata kunshin Leda wannan hayaki zaki dinga yi dashi, yakara miko wani, wannan kuma kidinga diban kadan kidinga sawa cikin ruwan wanka kiyi safe da rana, wannan kuma rubutu nekidinga sha kadan har sati daya, zeenatu tayi godia, mlm sani yakara nisawa: sannan Dan Allah kidage da ibada banda kalle kalle any how kojin wakoki, amsawa tayi da toh tareda kara yin godia, inna ce tace: mungode mlm sani nawa ne kudin magungunan? Murmushi yayi yace: ae inna ni bana amsan kudi ko kwabo harse an warke, fatana dae Allah yasa adace, ameen duk muka amsa masa sannan yayi MNA sallama yatafi...               ***** mardiyya CE zaune tana tunani itafa Allah yasani tadae amsawa karkuzu ne amma badan hankalinta ya kwanta da abinnnan ba, don son danta aranta karuwa ma taji yanayi, kara taji suhail ya kwalla tareda kiranta mamiiii, dagudu mardiyya ta tashi tayi cikin daki hartana faduwa sabda tsabar rudanin datashiga, suhail ne akwance idanu a kakkafe jini na zuba ta baki ta hanci duk wani orifices na jikinshy fitar da jini yakeyi gwanin ban tausayi,kara ta kwalla tareda faduwa.                         ***Muqaddas ne zaune a office kwata2 yayi loosing wani concentration nashi tunda ya fito aiki gabanshy keta faduwa, daukar key din motar shi yayi tareda kulle office dinshi zuwa gida, tunda yayi parking gabanshy keta tsananta faduwa ahaka kamar kazar da kwae yafashe mawa yashiga cikin gidan nashy, dirrect dakin mardiyyar yashiga kasancewar dokarta ce inbe gantaba dole yashiga uwar dakanta yagaysheta, to yauma hakance takasance, abinda yaci karo dashi ne yasashi juyawar kwakwalwa, ganin dansa kwance male male cikin jini Dan har kwararowa yake daga wajenshi zuwa karkashin gadon mardiyya, jikinsa ne yafara rawa yafashe da wani kuka tareda fadin innalilahi wainna ilaihi rajiun! Dialling no dn abokinsa sanusi yayi tareda karawa a kunne cikeda tashin hankali, kuka yakeyi wiwi, kamar yaron goye danshi duk tunaninsa wanine yakashema sa  iyali,sanusi neyadauka tareda fadin yau madam tabarka kadauki waya kana Sada zu......bekarasa mgna ba kasancewar lura dayayi da muqaddas na kuka, lpy kuwa?,muqaddas ne yabashi amsa cikin kuka "sanusi kaimaza kazo kataymakeni suhail.... Meyasameshy? Kashe waya yayi batareda ya tsaya bama sunusin amsa ba, kuka yacigaba dayi, tareda jijjiga mardiyya da suhail, dan komae ya tsaya masa cak danshy har ga Allah yamanta gaggawar kai asibiti akeyi in ana cikin irin wannan hali, sanusi ne yashigo gidan akagauce, hasbunallahu wani'imal wakeel abinda sanusi ya iya fadi kenan tareda dafa muqaddas tashi maza mukaisu asibiti ba kuka yakamata muyiba, akagauce muqaddas yatashi, tareda saba mardiyya akafada duk wannan nauyi na mardiyya bedamu ba, shikuma sanusi yadauki suhail, a 360 suka bar harabar gidan zuwa asibitin saidu afolayan clinic, emergency trolley aka dauko aka saka mardiyya da suhail, bayanda muqaddas beyiba Dan abarshi yashiga cikin resuscitation room din aka hana Shi shiga, kuka yakeyi kamar ransa zefita sanusi nadan tapping bayanshi Dan duk jikinsu ya lalace da Jinin suhail, bayan one hour doctor yafito yakira muqaddas jiki a sanyaye yabi bayan doc din, bashy umurni yayi da" zauna sir" zama yayi a kujera tareda kurawa ma doc ido, kayi hakuri sir da abinda yafaru kaddarace "ya isa doc ina matata INA Dana kamin bayani please! Matarka munyi nasarar ceton ranta tana recovery room da alama yashiga shock ne sanadiyyr abinda tagani, amma yaron am sorry to say that we have lost him, innalilahi wainna ilaihi rajiun, kuka muqaddas yafara yana yi kamar karamin yaro, haka yayita kuka doc na lallashinsa. Ahaka aka kai suhail gidan sa nagaskia, mardiyya duk tagama susucewa kamar mahaukaciya irin acute psychosis dinnan............                   Alhamdullah Dan hajia sakeena da alhaji Ahmad na amfani da magani kuma alhamdulilah abubuwa ana samun rrangwame, yauma alhaji Ahmad ne ke zaune a tamfatsetsen office dinshi yana ayyukan dake gabanshy tareda sauraren kiraar qurani daga bakin shaik abdurrahman sudais, wani irin haskene ya gifta tagabanshy kamar wucewar Walkiya, salati yafara yi babu kakkautawa batareda yayi jinkirin daena fadi ba, komae ne ya kwancemasa tareda tariyo abubuwan dasuka faru, salati yakara yi jin kamar ana ambato masa sunan zeenatu, my love! yafada tareda mikewa cikeda tashin hankali yana kurma ma yaronsa kira, Lincolin! Yaron ne ya amsa tareda fadin" yes sir yana Sara masa, lincolin drive me home, OK sire Lincoln yafada tareda daukar brief case din alhaji Ahmad din, gida yakoma yataradda hajia sakeena cikin tashin hankali, hajia lafia daeko? Kuka take iya karfinta kamar yarinyar goye fadi take " abbba diyata zeenatu na tunata wlh, rungumo ta yayi tareda yin wata ajiyar zucia me karfi, nima yanda yakasance akanki hka tafaru dani umma ba kuka yakamata muyi ba tashi yakamata muyi mu gode ma Allah, gyada kai tayi tareda karfin halin tashy ta bi bayan alhaji Ahmad din.....

WACECE ITA?? Where stories live. Discover now