Page 9

746 60 0
                                    

⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊


💝 *SANADIN SOCIAL MEDIA* 💝

             *Written by*
*JAMILA MUSA* _{ meelat }_

*Follow me on wattpad @ meelatmusa*

*Sadaukarwa gareki* 👇🏻
*RABI"ATU AMINU MAMMAN DEE*

10/07/2018

9.

Jikin scokert ta ciro hiter tayi ta kwaɗa masa a kai..... Shi kuma yana durƙushe a gabanta kansa yana kallon ƙasa bai kalli momy ba bare ma yayi yunƙurin tashi dan tsirar da lafiyarsa,

         Momy don Allah kiyi haƙuri fadeel ya faɗi haka tare da miƙewa da sauri ya riƙewa momy hannunta da take dukan wa Ahmad dashi,

             Wani irin firgitaccen mari momy ta kwakwkwaɗawa fadeel tare da cewa idan ka sake riƙeni saina ɓata maka rai sakemin hannu dan uwarku,

          Momy kiyi haƙuri don Allah ki daina dukansa, naje na dake sa saima na haɗa dakai duk naci muku zaka san raina ya ɓaci, ɗan gajeran murmushi fadeel yayi sannan yace momy karfa ki manta yanzun nan kika gama faɗa cewa tsanani da duka baya sawa mutum yayi abinda bai saka kansa ba, sannan kuma baya shiryarwa,

Tou momy dukan yaya bashi ne zaisa ya fito da Rabi"atu ba, kiyi haƙuri shima ki lallaɓa shi, wani irin kallo momy tayi wa fadeel tare da cewa ni zan lallaɓa sa fadeel? Dani dashi waye ya kamata ya lallaɓa wani? Zan lallaɓasa amma sai inya faɗa min nina aifesa ko kuwa shine uwana?

       Murmushi Ahmad yayi da gefen bakinsa ba tare daya kalli kowa a cikinsu ba, yace kai fadeel gafara daga nan, fadeel zaiyi magana Ahmad ya daka masa wata irin tsawa wanda tasa "yan hanji kaɗawa,

           Ga fara a wurin tun kafin in taso, da sauri fadeel ya saki hannun momy ya matsa a gefe, jan guyawunsa Ahmad yayi yaja jikinsa zuwa daf da momy, sannan ya ɗora duka hannayensa a saman ƙafarta cikin ladabi ya fara magana cewa,

Momy kiyi haƙuri insha Allah zan fitar da hannuna akan Rabi"atu idan har hakan zaisa kiyi farin ciki,

         Sannan kuma zan daina hukunci akanta idan har kikace min ba kece kika aifeni ba tou zanyi haƙuri da hakan in daina hukunta miki ɗiyarki zan barta da "yan uwanta ni kuma in kama gabana danni idanuwana basa iya ɗaukar abinda takeyi ba tare dana tsawata mata ba, idan kuma har kece uwa a garemu dukanmu dani da Rabi"atu tou kibarta dani, dan muɗin mune jigo ga rayuwarta bata da kamarmu,

     Tou bani bace uwarka bani na aifeka ba shikenan kake so kaji ko? Tou na faɗa maka sai kuma miye? A hankali Ahmad ya ɗago da kansa ya ɗaga idanuwansa dakel ya kalli momy,

        Kallarni da kyau idan bakaji abinda na faɗa ba, cewa nayi bani bace uwarka bani na aifeka ba,

Kuma maza ka ɗauke idanuwanka a kaina idan baka daina kallona ba saina ƙwaƙwule maka idanuwa munafikin Allah tashi ka ɓacemin a wurin, kuma zuwa anjima idan banga Rabi"atu ba saina maka wulaƙanci daya fi wannan dan banga amfanin ɗan daya raina manya ba,

          Jiki a saɓule Ahmad ya miƙe ya fice a ɗakin, fadeel ganin Ahmad ya fita yasa ya kalli momy, kallo ɗaya yayi mata tare da girgiza kansa cewa nima yau zan wuce, cikin tsananin ɓacin rai tace kaima idan ka tafi ka nemi taka uwar munafikin da wani shegen kanka kamar na sadaka,

        Cikin sauri fadeel ya fice, yana zuwa ɗakinsa wanka yayi babu ɓata lokaci yayi shirinsa duk wani ɗan abunda yasan zai ɓuƙata ya tattara ko ta wurin Ahmad bai biya ba saƙo kawai ya tura masa cewa Yaya ni na wuce sai mun sake haɗuwa,

SANADIN SOCIAL MEDIATempat cerita menjadi hidup. Temukan sekarang