Page 31

656 56 0
                                    

⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊


💝 *SANADIN SOCIAL MEDIA* 💝

             *Written by*
*JAMILA MUSA* _{ meelat }_

*Follow me on wattpad @ meelatmusa*

*Sadaukarwa gareki* 👇🏻
*RABI"ATU AMINU MAMMAN DEE*

06/08/2018

31.

Uhum a ɓangaren jishad kuwa yabi rankataf dangi "yan uwa da abonkan arziƙi zuwan babban abokiyar ango a gari mai girma da karamci wato india,

    Jishad ya ƙara da cewa Rabi"atu masoyiya ce ta haƙiƙa wanda taci a yaba mata da irin namijin ƙoƙarin da zatayi dan zuwa wurinsa saboda tayasa murnar aurensa,

    Yace kuma Rabi"atu tana girmama shi sannan kuma tana martaba sa, haka kuma tana girmama ƙasar india ne saboda shi,

Faɗa abbu yayi masa sosai tare da masa gargaɗi cewa lallai wurin yayima yayimansa zai ɗauko kansa masifa, lallai idan ya ɗauko Rabi"atu wallahi saidai ta ƙare kansa badai su ba

   Jishad yace Abbu ita iyayenta basu gujemu ba? Tsoro ko fargaba suka sake ɗiyarsu ta taho india domin mu? Wannan fa abun dubawa ne kuma ya kamata ayi ƙoƙari kowa na gidan nan ya nunawa Rabi"atu karamci domin itama tana ɗaga daga cikin ahalinmu nan da kwanaki kaɗan itama zata zama surukar gidan nan!

Wani irin tarwatsetsen mari Abbu ya saukewa jishad tare da masa gargaɗi lallai idan har ya sake gigin kwatanta baƙar fata da sunan surukar gidansu haƙiƙa saiya gundulewa jishad harshe,

   Jishad dafe inda Abbu ya gagara masa mari yayi, sannan ya kalli Ummunsa sannan yace wallahi sai tazo sai ta zo kuma inga yanda za"ayi a mayar da ita nigeria, sai tazo anyi bikin shikenan ma sai amin auren dole? Nifa ma resmin ɗinnan kowa yasan bana santa ina biyayya ne kawai daga tana yaya dani shikenan dan hauka saita juya soyayya?

Yanda fa resmin takeji baƙin ciki a ranta idan taji ko ta ganni ina magana da mace ita Rabi"atu tafi tajin baƙin ciki mai ƙuna a ranta, sakin inda aka maresa yayi sannan yaci gaba da cewa kallon banza harara ko hantara duk wanda yayi ma Rabi"atu wallahi sai yabita nigeria ya koma can da zama,

    Yana faɗin haka ya juya ya fara tafiya yana cewa ni tunda nake a rayuwa ma ban taɓa ganin namijin da ake ƙoƙarin yima auren dole ba saini, harma nayi biyayyar kuma ni baza"abi abinda nawa zuciyar yake so ba? Hmmm Allah ya kawomin ke ƙasar india da alkairi,

   Kuka resmin ta farayi danjin maganganun jishad Abbau ne yace saurara saurara "yata daina kuka ki barni dashi, cikin kuka resmin tace ina da kyawuna fari dogon hanci ga yalwataccen gashin kai bugu da ƙari a tara mata dubu samun kamar resmin aikine ya samu ya sameni a sauƙaƙe yake wani cika bakin baya so na,

    Bayan yasan yanda maza suke wahala na sauraresu amma banda lokacin kowa ina laifin wanda yace yana sanka? Abbu yace karki damu resmin ki barni dashi ya ƙarasa maganar yana mai gogewa resmin hawayen idonta,

     Jishad kuwa shigarsa ɗakinsa wanka yayi ya zuge cikin shiga mai kyau da tsari wanda take nuni dashi cikakken ɗan gayu ne ajin farko da ƙarshe uwa uba kana kallonsa kasan cikakken ɗan bokona idanuwan sa sun buɗe sosai yana da aji daidai na misali kuma yana da wadatar wayewa bawai irin "yan jagaliyar india ba,

      Haka ya fito yazo ya wucesu zaune a palo suna ta ƙullawa da warwarewa Abbu kuwa sai ƙara nanatawa yake baiyi ma iyayensa gardama ba bai haifi ɗan da zai tsallake maganarsa ba, kuma yake ma maganar auren dole ai nima auren dolen akamin da uwarsa amma gamu nan bulumbuƙui dan haka ya ƙara jaddawa resmin ta saka ranta a inuwa anayin auren zai manta da lamarin wata Rabi"atun banza can,

SANADIN SOCIAL MEDIATempat cerita menjadi hidup. Temukan sekarang