Page 20

757 66 1
                                    

⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊

💝 *SANADIN SOCIAL MEDIA* 💝

*Written by*
*JAMILA MUSA* _{ meelat }_

*Follow me on wattpad @ meelatmusa*

*Sadaukarwa gareki* 👇🏻
*RABI"ATU AMINU MAMAN DEE*

26/07/2018

20.

Wani irin wulaƙantaccen murmushi Rabi"atu tayi tare da ɗaga idonta ta kalli sama, ajiyar zuciya tayi, sannan ta goge ɗan guntun ɗigon hawayen da yake mata ƙaiƙayi a saman fuska,

Kaji wani ƙarfin hali? Kaida baka taɓa gani na ba? Bamu taɓa waya ba, daga chat sai chat, kuma mu a ɗaukar lokaci mai tsawo bamuyi magana dakai ba, amma har kake ikirarin rakani zuwa lahira,

Allah sarki, tou bara naji dalilin da zaisa zaka mutu kaima idan har mutuwata tazo, saida ta ƙara goge hawaye sannan ta fara rubuta masa kamar haka,

_Miyasa kace zaka mutu idan har na mutu?_

_Saboda abota, kinsan ni ina girmama aboki_

_Daga abota kawai idan na mutu sai ka kaima ka fece lahira?_

_Lallai haka ne, kin yadda dani?_

_Eh_

_To idan har kin yadda da jishad kuma kina martaba abota idan har kina yin abota dani idan har kin yadda da ni abokinki ne, to ki faɗamin abinda yasa kika ce mutuwa zakiyi, daga lokacin da kika ambanci mutuwa har zuwa yanzun idanuwana da zuciyata sun kasa samun natsuwa, faɗamin don girman Allah miye yasa kika ce haka? Ko nine bakya so ina matsa miki ne?_

_A, a, ni baka matsa min ba,_

_To faɗamin miye kinji?_

_Motar ta!_

_Murmushi jishad yayi sannan yace me motar tayi ne?_

_Yayana ya kwace min key in motar ta ne_

_Tou sai me ya faru kuma?_

_Shine basu dawo min da makullin ba, kuma nayi wa dady magana har yanzun bai sake min magana ba, kuma idan na kira dady ya daina ɗauka, kuma nayi ma momy magana itama bata ce min komai ba!_

_Iyya swry,_

_Ke yanzu saboda motar kike cewa zaki mutu?_,

_Eh_

_To kiyi haƙuri kada ki mutu don Allah, jishad yana tare dake kinji ko?_

_Bani number da zan sameki zan kiraki yanzu!._

_08034528........,_

_Kada kiyi nisa da waya zan ƙiraki anjima kaɗan_

_Ohk_

Bayan ta gama chat da jishad ta rufe dater ta, tunanin maganar jishad takeyi wai zai mutu idan ta mutu, wai don Allah ki rufa min asiri kada ki mutu,

Murmushi Rabi"atu tayi tare da gyara kwanciyarta tana nazarin maganar jishad lallai indiawa sunsan darajar aboki kuma suna da riƙon amana,

Haka tayi ta tunani barkatai gaba ɗaya ta hana zuciyarta sikuni, tana cikin wannan tunanin ne wayarta ta fara ringing, da sauri ta lalubota, ganin number waje yasa ta tabbatarwa ranta jishad ne,

Ɗauka tayi tare cewa hello? Ajiyar zuciyar jishad yayi lokacin da yaji maganar Rabi"atu ta daki dodon kunnensa, ita kuma gaba ɗaya kalasa taji ta lulluɓeta saka makon jin jishad ya sauke ajiyar zuciya!

Shiru sukayi gaba ɗayansu na wani lokaci, sannan jishad yace ya kike ne? Wani iri taji a jikinta, dan haka itama ta ɗan daure tace lafiya qalau, me kikeyi ne yanzun?

SANADIN SOCIAL MEDIATempat cerita menjadi hidup. Temukan sekarang