Page 13

779 65 0
                                    

⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊


💝 *SANADIN SOCIAL MEDIA* 💝

             *Written by*
*JAMILA MUSA* _{ meelat }_

*Follow me on Instagram @ meelat_musa*

          *Ba sauran kwarewa bayan ka riga ka zamo maƙura, ita jallabiya Allah wa'alamu ce ƙawar social media dan babu basarake babu talaka sannan kuma babu mai kuɗi dan kowa hawa yake yi, tou itama jallabiya haka take sanyata babu gamai kuɗi babu ga basarake babu ga talaka wannan magana tawa jawabi ne amma sai mai cikakken hankali da zai gane inda zance nawa ya dosa*

*Sadaukarwa gareki* 👇🏻
*RABI"ATU AMINU MAMMAN DEE*

17/07/2018

13.

Lokacin da zai saketa a hukuncin farko, tafiya yakeyi babu ji babu gani,

      Saida yayi tafiya mai nisa sannan ya tsaya ba tare daya fito ba ya ɗauki wayarsa ya fara kiran fahad,

       Babu daɗewa ya ɗauka Ahmad yayi masa sannu, murmushi mara sauti fahad yayi tare da cewa kana ta ina ne yanzun?

Na kusa ƙarasawa tsayawa nayi Ahmad ya faɗa, fahad yace tou ka sauka lafiya sai na taho, yayi babu damuwa Ahmad ya faɗa tare da ajiye wayarsa yaci gaba da tafiya,

      Saida yayi tafiya kamar zaije wulƙihu a ƙofar wani katafaren gida ya tsaya sannan yayi horn, babu wani ɓata lokaci mai gadi ya yaye masa get in shi kuma ya silala da motar sa cikin farin ciki zaici uwar Rabi"a babu shakku,

         Bayan yayi parking ne ya fito daga cikin motar, saitin da Rabi"atu take zaune ya buɗe ya fito da ita bawai fitowa ta ahankali ba fizgota yayi cikin matsanancin ɓacin rai,

Janta yakeyi yana tafiya da ita kamar ɗan jagora yanajin haushin makohon da yake masa jagora,

       Har ya isa inda zai ajiyeta, tashin hankali bayyane a fuskarta har zufa takeyi kwalkwal tayi da idanuwa ta fara kuka dan ji takeyi kawai ta isko lokaci,

         Zama Ahmad yayi saman kujera ya ɗora ƙafa ɗaya saman ɗaya taɓe bakin sa yayi tare da yatsina fuska sannan yace barkanmu da sake saduwa a cikin wannan gwabzawa karo na biyu,

      Ɗan gajiyayyen murmushi Rabi"atu tayi tare da zama saman karfet tace haba dai kaima dai yaya miye abun wani gwabzawa? Kawai dai kace zaka hukuntani, tou kuma miye laifi a ciki dan Yaya ya hukunta ƙanwarsa? Ai wannan ƙauna ce mai girma, bazan maka gardama ba na kaita basai na bawa shari'a wahala ba!

            Kallo Ahmad yabita dashi ba tare daya ce mata komai ba, rashin gaskiya yasa ta taci gaba da cewa uhum Yaya ke nan wai wai wai waiii gwabzawa karo na biyu, murmushi tayi tare da ci gaba da cewa wallahi sai naga abun kamar a film irin ector ya kama boss zaici ubanshi, ɗan yarfa duka hannayenta tayi sannan tace tou shikenan naji kaine ector nine boss kasheni kawai wasan yazo ƙarshe,

           Ai basai kince nacicci ubanki ba, yanzu kuwa zan cika alƙawarin dana ɗauka, miƙewa tsaye yayi tare da riƙo abinda zaiyi hukunci dashi, danuwa Rabi"atu ta zaro sosai kamar taga mutuwa dan ganin abinda Ahmad ya ɗauko zai daketa dashi, da sauri ta miƙe tare da furta,

       """La""ilaha i"llallahu muhammadur rasulillah, S. A. W, kuka ta farayi tare daja da baya tana mai nanata innalillahi wa"inna ilaihir raji"un, shima binta yakeyi, ganin yana biyota yasa ta fara gudu a cikin makeken farlon tare da faɗin momyna kizo ki ceceni, idan kuma sai bayan na mutu kika zo na yafe miki momy idan kin samu wata ɗiyar ki saka mata irin sunan na kuma ki riƙa bata labarina da rashin jin da nakeyi kuma kice nabar wasiyya cewa kada ta sake tayo irin halina dan makasanta suna tare da ita,

Ƙyaleta Ahmad yayi duk sai data gama guje gujenta sannan ta dawo kusa da inda yake tsaye da sauri ta ɗurƙusa ta kama ƙafafuwansa tana neman gafara, cikin kuka tare da shan majina tace kayi haƙuri shashshekar kuka sannan taci gaba da cewa idanma azumin kakeji saida ta ƙara shan majina sannan ta ɗago ta riƙe daidai guyawunsa taci gaba da cewa ai saima inyi maka azumin,

        Waiwaye waiwaye takeyi tana ci gaba da cewa ɗan uwa rabin jiki ɗan uwana nakaina wayyo Allahna ina ƙaunarka ina sanka a daidai lokacin da samu nasarar riƙo wata rober yaji { tashshi } dake bayanta tana mai ci gaba da cewa,

       Ubangiji yasa kayi hannun riga da baƙin ciki ɗan uwana ina sanka a daidai lokacin data miƙe ta sheƙawa Ahmad yajin nan a fuska, banda salati babu abinda Ahmad keyi,

           Wata irin dariya Rabi"atu ta sheƙe da ita tare da tafa duka hannayenta zama tayi saman kujerar ta ɗora ƙafarta ɗaya saman ɗaya sannan ta gyara hannun rigarta duk da cewa hannun bai kawo inda take zato ba, dariya takeyi sosai tare da cewa an faɗa maka ni sa"ar wasan yaro ce? Ya kaji nawa salon a cikin wannan tsohon daren?

          Taɓe baki tayi sannan ta fara kwaikwayon maganar Ahmad, barkanmu da sake saduwa a cikin wannan gwabzawa karo na biyu, ɗan gajeran tsoki tayi sannan taci gaba da cewa to an haɗu ka kasa gwabza uwar komai, yau nice zan rufe a gidan nan yau zaka fara ansar sakamako daidai da irin iskanci da aikatamin a baya, faɗamin irin nau"in abincin da baka so? Hahhhhhhh ta kece da dariya,

        Yau wani yaro zaici gidansu, Ahmad kuwa banda ihu da kuka babu abinda yakeyi lallai yau zaici uwar Rabi"atu harsai ta raina kanta, muryar rabi"atu yaji tana cewa da Allah rufe mana baki sai wani yagewa kakeyi wayyo wayyo tana kwaikwayon yanda yakeyin kukan,

      Ɗifff Ahmad ya ɗauke lumfashin sa dan ya gama tsorata da Rabi"atu idonsa a rufe baisan abinda zata masa ba yanzun, ina mukulin daka rufe mu yake? Ta tambaye sa, zo na raɗa miki inda na ajiye shi,

      Da yake akwai sauran yarinta sai ta nufi inda Ahmad yake tsaye, ram ya riƙeta ya fara ci mata yanda ya kamata dayaji idansa ya masa zafi adadin dukan da zai kawaiwa Rabi"atu saidai ya dunƙule hannunsa ya soke a awazu, { haƙarƙari } saida taci ubanta sosai yayi mata jagaja sannan ya barta,

         Janta yayi ƙasa har wannan lokacin idonsa a rufe yake, saida yakaita wani ɗaki ya wurgata sannan ya rufe ɗakin,

      ***            ***
Saida Rabi"atu tayi wata biyu curr Ahmad yana gagara mata azaba, momy kuwa halin Ahmad bata san irin sa ba addu"a kawai takeyi ubangiji ya shirya Rabi"atu ta huta da horon wahala,

Kamal kuwa ya shiga ya fita rashin Rabi"atu a kusa dashi yana masa ciwo, kuma Aisha ta faɗa masa cewa Rabi"atu bata da waya, kuma ya siye waya sabul dal tecno K A 7, ya bawa Aysha ta bawa Rabi"atu amma ganin Rabi"atu yayi wahala a wurinta bama ganin nata ba labarinta kwata kwata babu dan ta zabga uwar hijabinta da niƙaf taje gidansu babu ita babu dalilinta,

        A ɓangaren Rabi"atu kuwa ta anshi horo daidai da abinda take aikatawa a wurin Ahmad tacicci ubanta yanda ya kamata, tayi baƙiƙƙirin ta rame ta koma wata sokuwa dan azaba mai tsanani Ahmad yakewa Rabi"atu dan a ganinsa ta hanyar wannan horon zata samu natsuwa,

            Yau shida fahat suka shigo tana kwance kamar gawa dan Ahmad yace ƙoshi ne yake sakata iskanci shi yasa baya bata wadataccen abinci, hankalin fahad ya tashi yanda yaga Rabi"atu ta koma saida yayi kuka saboda tausayinta gata ta koma kamar an tsafata sai wani wuƙil wuƙil takeyi da idanuwa kamar mage ta faɗa tarko,

         Cikin kuka fahat yace Ahmad don girman Allah ka cire yarinyar nan daga cikin wannan akubar, a hankali Rabi"atu ta ɗago kanta da idanuwanta da suka ƙara fitowa ta kallesu, Ahmad yace wannan yarinyar fa munafika ce babu abinda taji daga cikin abinda na mata ina saketa anjima zata fice daga gida,

        Fahat yace to ko dai tana da iska ne? Ahmad yace koda iska akwai iskanci, fahat yace A, a, kusa ayi mata ruƙiyya akwai wani malami da na sani mai fitar da aljannu bara zan kawoshi a jaraba sa"a mu gani,

            Bayan kwana biyu Fahat yazo da malamin ruƙiyya, Ahmad ya fito da Rabi"atu aka miƙeta a saman tabarma aka fara karatu..............Gadai yanda Rabi"atu take cewa idan taji an taɓo aya mai zafi,

SANADIN SOCIAL MEDIATahanan ng mga kuwento. Tumuklas ngayon