Page 11

752 65 0
                                    

⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊


💝 *SANADIN SOCIAL MEDIA* 💝

             *Written by*
*JAMILA MUSA* _{ meelat }_

*Follow me on wattpad @ meelatmusa*

*IYA KUƊIN KA, lallai IYA KUƊIN KA hausawa kuwa suka ƙarawa maganar da cewa IYA KUƊIN KA IYA SHAGALIN KA, ni kuma nace iya karatun ka iya buguwar zuciyarka, nikam dai kin baddalamin tunani gaskiya, amma masu iya magana nacewa, sannu bata hana zuwa, mutane kuwa suka ƙare da saidai a daɗe ba"aje ba, gaskiya na jinjina miki bisa namijin ƙoƙarin da kikeyi a cikin wannan littafin naki mai taken IYA KUƊIN KA, kindai san ƙorafina akanki leema basai na faɗa kowa yaji ba*

*BAKIN GANGA, lallai sai BAKIN GANGA masu karatu karku bari na baku labarin littafin nan, domin fasaha da tsantsar basira marubuciyar tayi amfani da ita, har yanzun baku makara ba domin sabon fitowa ne yana tafiya daidai da zamani dan marubuciyar KUNYANGAR QUNCHI itace dai ta dawo da sabon salon nata mai taken BAKIN GANGA nemi naki dan kallon cakwakiya*

              *SO MAKAMIN CUTA, wayyo Allah ni kuma sai ya kama mani zuciyata, Allah ya ƙara basira da hazaƙa nima ina biye dake*

*NI YA NA"EEM NAKE SO, nima dai nace sai yaya na"eem*

*Sadaukarwa gareki* 👇🏻
*RABI"ATU AMINU MAMMAN DEE*

13/07/2018

11.

Banda dariya babu abinda sukeyi a cikin motar saidai su haɗa hannu a kashe taf,

            Sun Ibi lokaci sosai suna tafiya a motar kafin su isa wurin partyn kamal,

Lokacin da suka isa wuri ya cika ya batse gam da jigajigan "yan duniya, amma wai baza a fara partyn ba sai 1:30am,

        Ga wani irin kiɗa da yake tashi dan har cikin zuciyarka kana jin kiɗan, dan duk inda kakai da iya saka idonka ko bindiddiƙi bazaka ga sifikun ba, dan haka suka cewa kiɗan daga cikin bango yake fitowa,

       Idan kuwa mutum yana kusa dakai ya kama kunnenka yayi maka raɗa tou duk iya lafiyar kunnenka bakajin abinda yake faɗa saboda yanda kiɗan yake fita,

       Maza da mata an zuge kowa ka gani ya ansa sunan sa ka kirasa da sheɗan dan sune magoya bayansa da duk wani abu na halaka sun bawa sheɗan gudamawa,

           Rabi"atu a gafen Aysha tana ta ƙara kallon yanda mutanen duniya suka goge abunsu, lallai ya zama dole itama fa ta ƙara zage ɗamtse dan lallai ji take an barta a baya,

       Haka ta buɗe idanuwanta taci gaba da kallon "yan mata da suka ƙwace, Aysha ce taja hannunta suka fita waje danyin magana,

          Rabi"atu ga kayan da zamuyi amfani nan dasu ta nuna mata, cikin rashin fahimta Rabi"atu tace miyasa baza mu tsaya da namu ba?

     A, a, Rabi"a wannan sune kowa yake sakawa baki lura ba? Dan haka muma mu saka kinaji gashi can an fara magana cewa kamal yana iso wa,

Ansar kayan rabi"atu tayi a lokacin har Aysha ta cire rigar jikinta ta saka riga mai ɗauke da sunan kamal a baya, ɗan bingilin wando ne, wanda ko rabin cinya bai kawo ba,

        Kallon shigar Rabi"atu tayi sosai tare da cewa Aysha gaskiya nidai bazan saka ba, cikin lallashi Aysha tace haba friend ai kamal bazaiji daɗi ba, kawai kiyi haƙuri ki saka dare ne fa babu wani wanda zai ganmu yi sauri ki saka mu shige,

         Saida Rabi"atu tayi jim na wasu lokutta sannan dai ta basar ta saka kayan, woo Aysha ta faɗa, taci gaba da cewa yarinya kinfa ci taro, da kin tsaya da wannan ƙauyawan kayan ai da taro yaci mu ta ƙarasa maganar tana dariya,

        Tafawa sukayi sannan suka rankata zuwa ciki, kamal yayi farin cikin ganin Rabi"atu sosai ga wasu dirarrin "yan tashan mata wanda sunci uwar bilicin harda ubansa ga wani atach irin na ɗiyan arna a saman kansu, sune tsaye a gefen kamal sai wani kwartanci sukeyi, kallo ɗaya zakayi wa kamal kasan ya gama karatun iskanci dan matan sai wani lillinda kamal sukeyi suna liliyashi shi kuma sai wani kashe ido yake yana lashe baki kamar wani tsohon maye,

           Ɗan kashewa Aysha ido ɗaya yayi wanda ita ta gane abinda yake nufi, dan haka taja Rabi"atu suka matsa zuwa inda kamal yake zaune,

        Barka da zuwa sarauniyar zuciyata, haka kamal ya faɗa yayin dasu Rabi"atu suka zo inda yake zaune yana nuna mata wurin zama a saman cinyarsa,

Murmushi Rabi"atu tayi tare da girgiza kanta alamar A, a, murmushi kamal yayi sannan ya miƙe tsaye tare da ɗan rungume rabi"atu a gefensa,

          Ganin Rabi"atu a gefen kamal yasa wuri ya cuɗe da hayani, yayin da kiɗa ya daina tashi MC ya fara bayani cewa wannan ƙayataccen taro anyi sa ne domin taya mai girma kamal murnar zagayowar shekarar aihuwar sa, sannan kuma yana sanar da maza da mata cewa a yauɗin nan ne zai saka zobe a hannun sabuwar rayuwa wato Rabi"atu don Allah jama"a ku taɓawa masoya guda biyu, tafi rafraf gaba ɗaya aka ɗauka a wurin,

      Ihu da sowa ya hana ma kaji abinda MC yake faɗa yayin da wasu kejin kamar su rabawa Rabi"atu kanta da gangar jikinta, ɗan kwabar zobe kamal ya fita a cikin aljihunsa ya kama hannun Rabi"atu ya danƙara mata zoben alƙawari, yayin da ihun yaci gaba da ƙaruwa wanda yafi na farko,

        A wurin yanka cake ma hannun kamal a ƙasa na rabi"atu a sama aka yanka cake Rabi"atu ta iba ta bawa kamal a bakinsa tare dayi masa murnar zagayowar ranar aihuwarsa, sannan ta cusa sauran a bakinta a daidai lokacin da kiɗa ya ci gaba da tashi a wurin babuji ba babu gani,

        Haka a kaci gaba da ranƙwashewa yayin da wasu sukaci gaba da antayawa cikinsu giya dan duk kayan mayen da ka sani kuma kake nema akwaisu a wurin, hakan take ga Aysha itama tasha ta kwale abunta,

       Kana mata magana zatayi kamar ta faɗo maka sannan tayi magana cikin maye cewa sun gode sun gode, Rabi"atu kuwa tunda wuri ya cakume kamal yaja hannunta suka silale a wurin,

              Cikin tashin hankali Rabi"atu takeyi wa kamal magana cewa itafa kayanta data cire bata gansu ba, cikin magana mai kashe jiki kamal yace mata me zakiyi dasu ne? No ba komai ina so kawai in canja ne dan bansan lokacin da zan shiga gida ba, yaya yace idan na fita sai yayi min dukan da za"a ƙaramin lumfashi, idan kuma ya ganni da wannan kayan kila zai kasheni ne,

      Murmushi kamal yayi tare da jawo Rabi"atu a hankali zuwa cikin jikinsa, hannunsa saman gashin kanta kallonta yayi ido cikin ido sannan yace kada ki wani damu, a kullum ki zama mai dakakkiyar zuciya kada ki bari wani ɗan ƙaramin ƙwaro ya firgitaki, karki manta matsoraci baya zama gwani, a haka zamuyi soyayyar?

A, a, wannan bai shafi soyayyarmu ba, ɗan ƙara fizgota yayi sosai cikin yanayin tsoro a jikinsa saida fuskar kowa tazo kusa data kowa sannan kamal yace *TSORO* murmushi rabi"atu tayi tare da sauke ajiyar zuciya ta kwanta jikin kamal sosai dan jikinta ya gama rasuwa,

       Murmushin mugunta kamal yayi tare da ɗagata daga jikinsa dan yaga a sauƙaƙe zai kamo Rabi"atu, saida ya zaunar da ita a mazauninta yace muje in ajiyeki gida an fara kiran sallahn asuba,

        Murmushi kamal yayi sannan ya fara tafiya har suka iso ƙofar gidansu Rabi"atu babu wanda ya sake magana, godiya tayiwa kamal bayan sun tsaya sannan ta fita,

Kamal yana kallonta har tasha kwanar gidansu tunda bata ƙofa take shiga ba, da sauri ta duƙa ta kurɗa ta inda take shiga, da sauri ta shige sannan ta danne wurin da katakon da take rufewa tayi ciki da gudu ba tare da wani ko wata ya ganta ba!.....

          Da saurinta ta isa ɗakinta wanka tayi tare da ɗauro alwallah tazo ta haye saman abun sallah,

Tayi raka"atanil fijir sannan tayi sallah asuba saida tayi karatun Qur"ani sannan ta kwanta,

             Kwanciyarta ke da wuya ta lumfeshe idanuwanta danyin bacci amma bacci yace baisan idanuwan Rabi"atu ba, abubuwan da suka faru a wurin bithday ya fara karakaina a cikin ƙoƙon kanta idanuwanta kuwa data rumtse kamal ne tsaye ɗauke da kyakkyawan murmushi a fuskar sa yana miƙo mata hannu.........,

SANADIN SOCIAL MEDIATempat cerita menjadi hidup. Temukan sekarang