Page 36

791 51 0
                                    

⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊


💝 *SANADIN SOCIAL MEDIA* 💝

             *Written by*
*JAMILA MUSA* _{ meelat }_

*Follow me on wattpad @ meelatmusa*

*_RAMLAT ABDULRAHMAN { real mai dambu }_*

                     *_&_*

*_JAMILA MUSA { meelat }_*

_Meelat Musa_
*_Ke na gani, na gani!_*

_Mai dambu_
*_A ina kika gani, kika gani?_*

_Meelat Musa_
*_Yanzu yanzu zani baki labari, inna kulle idona,_*
_Mai dambu_
*_Uhmn_*
_Meelat Musa_
*_Ko na buɗe ido na!_*
_Real mai dambu_
*_hmm uhmm, na baki zo ki anshi dukan soyayya!_*
_Meelat Musa_
*_Hmmm haɗuwarmu nidake silarta soyayyace, na daɗe ina nema na samo burinki, wanda yaso in a kaso shi yai babbar nasara ce, tunda kin so ni da gaske nima bani barinki,_*

_Meelat Musa_
*_Ngde miki zuciyata kinmin adalci, da kika sani na yadda naso mai inganci, so guda ɗaya wanda babu haɗi kuma ga "yan ci, na tabbata gamon da nai da alkairi!_*

     *_Ina miki fatan alkairi Mai dambu Allah yasa albarka a cikin tarayyarmu, wato kin burgeni ne, kaff social media akace waye ƙawarki wanda kikeji da ita budar bakinki kawai sai kikace Jamila Musa, haka ya tabbatar min da ina da matsayi na daban a zuciyarki, ina ƙaunarki! JAMILA MUSA na godiya_* ❤💋

*Sadaukarwa gareki* 👇🏻
*RABI"ATU AMINU MAMMAN DEE*

11/08/2018

37.

Abbu ya daɗe yana kallon jishad sannan yace jishad mi yasa kake so ka koyi halin da ba naka ba?

    Shiru jishad yayi baice masa komai ba, Abbu yace tou kayi haƙuri da yarinyar nan kaji ko?, ɗan gajeran murmushi jishad yayi tare da ɗagowa ya kalli Abbu amma baice komai ba!

     Murmushi Abbu yayi tare da cewa kayi haƙuri ko jishad? Ya ƙarasa maganar yana mai dafa kan jishad, murmushin ƙarfin hali jishad yayi tare da cewa bakina ya haƙura, amma bara a tambayeta ita idan ta yadda!

Abbu yace wace ce zaka tambaya? Jishad yace ita mana, Abbu yace bata da suna ne? Dariya jishad yayi sosai kamar zararre yace wai zuciyata mana, Abbu yace kai dakata bana san shirmen banza,

      Ɗan lumshe idanuwa jishad yayi tare dakai hannunsa wurin zuciyarsa yace kina ji na?  Bayan wani lokaci yaci gaba da cewa saƙo daga Abbu fatan zaki karɓa? Shiru ya sakeyi na wani lokaci sannan yaci gaba da cewa ai nasan kinji komai amma kiyi haƙuri dan tayani cika umarni mahaifina mana!

      Da sauri ya ɗago kansa idanuwa ya zaro sosai tare da kallon Abbu yace wallahi tace bazata yadda ba! Yaci gaba da cewa Abbu ka rufamin asiri ka barni ka barni don ƙaunar da kake ma ummuna, kayi haƙuri ka bar zuciyata da abinda take so,

    Da sauri Abbu ya miƙe tsaye shi kuma jishad durƙusawa yayi tare da riƙe daidai guyawun Abbu ya kwantar da kansa yana cewa kayi haƙuri wallahi idan ma na tafi bana dawowa shi kenan ranka bazai sake ɓaci ba, Rabi"atu tayi min alƙawarin zamu zauna a gidansu nidai ka barni kafin na mutu na roƙe ka Abbu, ya ƙarasa maganar hawaye yana fita daga idonsa,

       Murmushin takaici Abbu yayi sannan yace wa Ummu wai kinji wai zai mutu, ka mutum mana ance maka zamu fasa rayuwa ne idan baka numfashi, kanayi muma munayi dani dakai zanga fasashshe, yana faɗin haka ya cire jishad daga jikinsa ya wuce,

     Da sauri jishad ya miƙe ya nufi inda ummu take tsaye, rumgumeta yayi yana cewa ummu kema baki san abinda nake so? Itama zaɓewa tayi tabi bayan mijinta,

SANADIN SOCIAL MEDIAOnde histórias criam vida. Descubra agora