Page 12

811 58 0
                                    

⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊


💝 *SANADIN SOCIAL MEDIA* 💝

             *Written by*
*JAMILA MUSA* _{ meelat }_

*Follow me on wattpad @ meelatmusa*

            *Assalamu Alaikum, barkanmu da wannan lokaci ina muku fatan alkairi mabiya littafin SANADIN SOCIAL MEDIA, ƙorafe ƙorafenku ina ganinsu kuma inajinsu, yayin da wasu suke cewa don Allah kar na bari Kamal yayi nasarar raba Rabi"atu da budurcinta, wasu kuma suna cewa ta cika taurin kan tsiya yayin da wasu kuma suke cewa bata da kunya da sauransu kowa dai da abinda yake faɗa, to duk naji kuma na gani na gode sosai da shawararku a gareni, amma kuyi haƙuri kada ku manta tun kafin na fara rubuta littafin nan na faɗa muku cewa labarin nan da zan rubuta da gaske ne ya faru sannan kuma da sanin mijin Rabi"atu da yardarsa nake rubuta wannan labari, dan haka ina baku haƙuri duk wanda yaga ban masa yanda yake so ba to don Allah yayi haƙuri wannan labari ba nawa bane kuma ba ƙirƙirarsa nayi ba haka labarin yake kuma haka nake tafiya dashi, da fatan kun gane abinda nake nufi, daga ƙarshe kuma nake cewa ku huta lafiya na gode taku mai ƙaunar farin cikin ku, JAMILA MUSA ngd da yawa ku sarara abunku tare dayin ƙarko ina muku fatan kuyi shekaru irin na dabino*

*Sadaukarwa gareki* 👇🏻
*RABI"ATU AMINU MAMMAN DEE*

15/07/2018

12.

           Yana miƙo mata hannu...............murmushi tayi tare da miƙa hannunta itama, ganin ta kama iska ya tabbatar mata da tunani takeyi, ajiyar zuciya tayi tare da gyara kwanciyarta ta rufe idanuwanta cincin ƙarfinta dan ba idonta haƙƙinsa,

Ƙarfe 09:09am Ahmad ya fara motsi addu'ar tashi daga bacci ne ɗauke a bakinsa, tare da yin miƙa sosai,

             A hankali ya fara buɗe idonsa wanda yayi masa nauhi kamar an ɗora masa dutsin dala a sama, marmara idanuwan sa ya farayi cikin yanayi na wanda yasha bacci har ya godewa Allah,

        Hasken ranar dake hasko masa kwayar idonsa ya tabbatar masa da lallai yayi ranar bacci, a ɗan firgice ya buɗe idanuwan sa gaba ɗaya tare da sauke su saman agogon dake maƙale a jikin bangon ɗakin sa,

        Innalillahi wa"inna ilaihir raji"un ya faɗa tare da dafe kansa da duka hannayen sa, lumshe idanuwan sa ya sakeyi cikin yanayin tunani, ya daɗe a cikin wannan yanayi, murmushi yayi dan lallai duk abinda ya faru a daren jiya tsakanin sa da Rabi"atu kaf ya tunosa a cikin kwalwar kansa,

        A gajiye ya ziro ƙafafuwan sa daga saman gadon sa ya nufi toilet a wahalce, saida ya watsa ruwa sannan ya ɗoro alwalla dan gabatar da sallah asuba data wuce sa,

       Bayan ya gama abinda yakeyi ya nufi ciki amma a ransa yayi alƙawarin bazai wa Rabi"atu magana ba kuma bazai nuna mata yasan abinda ya faru ba amma sai ta gane shi yafita iskanci,

         Ɗakin momy ya nufa kasancewar yau ba ranar aiki bane ya shiga dan ya su gaisa, kwance ya sameta tana waya da da dady wanda ya ɗaga ranar zuwan sa, gefen gadon ya zauna yana jiran su kammala!

    Ganin wayar ba mai ƙarewa bane yasa ya ɗan kwanta, amma sai yaji yanzun ma suka fara, labaransu kawai sukeyi shima yana bata suna dai yin wayar ne cikin jin daɗi da farin ciki,

Ganin haka yasa ya haƙura ya fito dan yin kalaci, bayan ya gama break yana zaune a wurin yana chat har zuwa 12:00pm yana a wurin zaune,

        A gajiye ta fito daga ɗaki tana miƙa sai hamma takeyi saboda gaji kuma batayi wani wadataccen bacci ba, saida ta ƙara miƙewa sosai sannan tace Yaya harka tashi?

SANADIN SOCIAL MEDIADonde viven las historias. Descúbrelo ahora