Page 6

956 67 0
                                    

⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊


💝 *SANADIN SOCIAL MEDIA* 💝

*Written by*
*JAMILA MUSA* _{ meelat }_

*Follow me on*

*Wattpad @ meelatmusa*

*Instagram @ meelat_musa*

*Tafasar tukunya bata rage gefe, sai hali yayi daidai akanyi abota, in Allah yaƙi addu"ar biri sai ya mutu a gonar arne,*

*Gaisuwa a gareku HAƊIN KAI GROUP*

*HABIBA IDRIS* _{ Hubbeey }_

*REAL SMASHER*

*MAIMOUNATH O.G*

*HALIMATU SADIYA MUHAMMED* _{ Leema }_

*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_

*Ubangiji ya ƙara haɗin kai da zaman lafiya Am3n*

*Ina miki sannu da jiki SURAYYAHMS Allah ya baki lafiya, ubangiji yasa kaffara ne!*

*Sadaukarwa gareki* 👇🏻
*RABI"ATU AMINU MAMMAN DEE*

04/07/2018

6.

Jikinta har kyarma yake take kiran sunan fadeel,

Daidai zata fita daga cikin farlon suka haɗu gaba ɗaya har karo suke kaiwa juna saboda babu wanda yasan da zuwan kowa!

Lafiya momy? Abdul ne ya tambayeta, cikin in ina bakin momy har ƙyarma yake tace Ah...Ah..Ahma....Ahmad ne zai kashe min ɗiya, gaba ɗayansu sukayi tsoki a lokaci ɗaya tare da sauke ajiyan zuciya suka ce momy mu mumma ɗauka wani abu ne suka faɗa a tare, juyawa sukayi suka bar wurin...,

Wannan wane irin iskanci ne haka? Ina faɗa muku Ahmad yana dukan doughter amma zaku kama gabanku? Saboda ba ɗiyarku bace ko? Ba tare da sun juyo ba sukace ai momy muma idan muka je ƙara mata zamuyi Allah ma yasa ta mutu kema ki huta da ciwon zuciya,

Ni kuke haɗa ma baki kuna bani amsa a tare ko? Babu wanda ya ƙara magana suka wuce abunsu, ganin basu da niyar zuwa yasa momy gyara ɗaurin zaninta tare da komawa ɗakin Rabi"atu cikin kiɗimammen tunani,

Shiko Ahmad riƙeshi momy takeyi amma sai kara kai zamiya yake ya tirje saitin haƙoran Rabi"atu saida yayi mata lullusar fitar hayaci dan bai samu natsuwa ba saida yaga Rabi"atu ta sulale ƙasa ta daina motsi sannan hankalinsa ya kwanta,

Gyara hannun rigarsa yayi sannan ya nufi toilet, alwalla yayo dan gabatar da sallah asubu tunda lokaci yayi, yana fitowa ko inda momy take bai kalla ba ya fice a ɗakin,

Momy durƙushewa tayi a wurin tana kuka tare da kamo Rabi"atu ta ɗorata saman jikinta ta riƙe daidai kanta ta riƙe tana kuka sosai har jijjiga jikinta takeyi saboda yawan kukan,

Ganin kukan baya fishsheta ta sauke Rabi"atu daga jikinta da sauri ta fita a ɗakin, a falor taga Ahmad zaune akan abin sallah ko kallon momy baiyi ba itama bata kalleshi ba saima haushin sa da takeji kamar tayi mishi duka tunda har yayi dukawa rabi"atu,

Tana shiga ɗakinta da sauri ya tashi ya nufi ɗakin Rabi"atu, ɗaukarta yayi yaje ya kaita can wani ɗaki ya ɓoyeta sannan ya dawo ya zauna a inda yake zaune a farko dan yasan buri momy ta kaita asibiti ne,

Bai daɗe da zama ba momy ta fito daga ɗakinta da alama itama saida tayi sallah ta canja kayan jikinta, da saurin ta, ta wuce shi ta nufi ɗakin Rabi"atu amma ga mamaki babu ita babu dalilinta,

Dubawa momy tayi ko ina babu ita, cikin rashin natsuwa tayo farlo tace Ahmad ina kuma ka kaita? Wake nan? Ya tambaya tace ban sani ba, ɗan taɓe baki Ahmad yayi ba tare daya ce komai ba, momy tace dan ubanka bakaji ina magana ba?

SANADIN SOCIAL MEDIADonde viven las historias. Descúbrelo ahora