Page 10

807 65 0
                                    

⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊


💝 *SANADIN SOCIAL MEDIA* 💝

*Written by*
*JAMILA MUSA* _{ meelat }_

*Follow me on wattpad @ meelatmusa*

*Ganin gida kesa kare ya zagi kura amma ba daji ba, mun ƙoshi da nama warinsa mukeji, ana zaman ƙarya bamaguje yazo gari ya iske babu masussuka dan muguwar miya bata ƙarewa a tukunya, ba"a cewa maci wake yasha ruwa,*

*Fataken dare basa bacci, Allah ya ƙarawa kogi ruwa kududdufi ya samu, kowa yaci ladan sarki ya masa yaƙi, jinjina a gareki FADILA LAMEEDO ja muje Meelat Musa tana biye dake gaisuwa ta ga Ashmar da zakiyya*

*NA'IKKE: Abokin kirki yafi mugun ɗan uwa, duhun damisa maganin mai kwaɗayi, kuwwa da kuwwa bata korar buzu, tsoro na daji kunya na gida, dan ansan da wuyan biri ake ɗaure sa a ƙugu, ni JAMILA MUSA nake tunkuɗo saƙon gaisuwa ta zuwa a gareki, fatan alkairi nake mana da addu"a ubangiji yasa albarka a cikin ABOTAR MU*

*Jama"a ku tayani jaje wai mai Dambu tawa take cewa kowa ya fita yayi katin zaɓe, can kuma sai naji wata tace mata Allah yasa nan gaba karki ce A. P. C, towai tambaya shin siyasa ta fara ko kuwa ya abun yake?*

*Sadaukarwa gareki* 👇🏻
*RABI"ATU AMINU MAMMAN DEE*

11/07/2018

10.

Murmushi Ahmad yayi sanna yace kiyi wankanki anan mana? Faɗamin ruwane babu ko sabulu? Ya ƙarasa maganar yana mata kallon ukku saura kwata,

Kallon kanta tayi daga sama har ƙasa sannan tace koda akwai nan ne bana buƙatar yin wanka sai ɗakina,

Gyara tsayuwarsa yayi sannan yace kenan idan aka miki aure kin gama wanka? Eh kullum gida zanzo in abuna,

Da kyau haka Ahmad ya faɗa tare da shafa sumar kansa sannan yaci gaba da cewa, zan fitar dake kiyi wanka amma bisa sharaɗi 1 ya nuna mata da hannunsa tare da ɗan taɓe bakinsa ya tambayeta da kansa zaki iya?

Kawai sai in ansa sharaɗin da ba,a faɗamin ba? Saurin me kikeyi ne to? Baga ni gaki ba? Ya nuna ta sannan ya nuna kansa, ya ƙarasa maganar yana ɗaga duka girarensa,

Tsoki tayi tare da cuno bakinta sannan ta gyara zamanta cewa inajinka, murmushi yayi sannan ya tura hannunsa ta jikin window n ya shiga ciki, taso kizo nan,

Babu gadma ta taso tazo kusa da window ta tsaya, kallonta Ahmad yayi sannan yace ki ɗora hannunki akan hannuna ki ɗauki alƙawari yanzun zan faɗa miki burina, zaki iya? Idan kuma kinsan bazaki iya ba kada ki ɗauka danni idan mutum ya ƙaryamin alƙawari kinsan azaba nake masa mai tsanani, shin zaki iya ne?

Da sauri ta janye hannunta tare da runtse idanuwanta ta fara dogon tunani, kallo kawai ya bita dashi yana jiran yaji abinda zatace, wata zuciyar tace ki yadda banza yayin da wata take gargaɗinta da ta kikayi kanta Ahmad baya ɗaukar raini,

Ki yadda banza ɗan dukan da za"a miki ai zai huci, ke nan zaki zauna ayi ta dukanki kamar wata jaka? Tou miye ya dakeki kawai ki rama, yanzun zaman "yan ci akayi Rabi"atu zaki bari a wani rufe ki sai kace lokacin mallakar bayi, lallaɓashi ya fitar dake idan kika fita zamu samu mafita, zuciyarta ce ta kasu kashi da dama take ta maganganu kamar anan cin kasuwa a cikinta,

Jin gardamar tayi yawa yasa Rabi"atu ta dakawa zuciyar tsawa a bayyane tace saurara ya isa haka nan, cikin dakiya ta kalli Ahmad sannan tace yaya miye sharaɗin naka?,

Bai bata amsa ba ya zagayo ya buɗe ɗakin ya shiga, sannan yace mata sharaɗi na ɗaya ne, zan fitar dake gaba ɗaya a dakin nan amma wallahi duk ranar dana kamaki kin fita ko kina dawowa ko wani abu wanda baimin daɗin ba wallahi sai maki dukan dasai an ƙara lumfashi kin yadda? Cikin rawar jiki tace Eh, wuce ki fice,

SANADIN SOCIAL MEDIAOnde histórias criam vida. Descubra agora