Page 18

706 58 0
                                    

⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊


💝 *SANADIN SOCIAL MEDIA* 💝

             *Written by*
*JAMILA MUSA* _{ meelat }_

*Follow me on wattpad @ meelatmusa*

*Gaisuwa gareki* 👇🏻
*FADILA LAMIƊO*

*Sadaukarwa gareki* 👇🏻
*RABI"ATU AMINU MAMMAN DEE*

25/07/2018

18.

       Bata daɗe da fara bacci ba wayarta ta fara kururuwa, cikin bacci taji wayarta tana ta ringing amma saboda tsabar gajiya ta kasa motsawa,

          Haka wayarta tayi ta ringing amma Rabi"atu gajiya ta hanata ta tashi taga mai kiranta, data gaji da jin kukan wayar a kusa da ita dan taji yana neman hanata tayi bacci, a kasalance ta lalabuto tare da kashe wayar taci gaba da baccinta,

Da safe kuwa bata farka ba sai 08:31am salati tayi da sauri tare da sauƙa daga saman gadon, dan ita tunda take ko wane irin gajiya ne tanayin ƙoƙari tayi sallah asuba a cikin lokaci,

     Toilet ta shiga da sauri tayo alwallah ta fito dan gabatar da sallah da batayi a cikin lokaci ba!

     Bayan ta gama sallah toilet ta koma tayo wanka, saida ta shirya sannan ta fita palo danyin kalaci,

       Ita ɗaya zaune a dirning area wayarta a hannunta tana shafawa kalaci takeyi amma gaba ɗaya hankalinta yafi tafiya a kan wayarta,

Tsoki tayi mai sauti tare da ɗaukar kofin dake ɗauke da ruwan tea takai bakinta! Saida ta ɗan jashi kaɗan sannan ta ajiye a bayyene tace kaiji mutum zai rainawa mutane hankali!

        Ina wani ruwansa da inda naje jiya bana online? Saida ta ƙara yin tsoki tare da tura dankali a cikin bakinta sannan tace to baka san ni ko gidanmu babu wani wanda yake cewa ina naje ina zanje ba?

        Ƙara kallon wayar tayi tare da ci gaba da karanta saƙon da jishad ya turo mata",,

_Kina gani ina miki magana amma kikayi shiru_

                          _Kai na gani kuma ai kaima kasan na gani, kai nifa ba yarinya bace da zaka wani sakani a gaba kana cewa jiya ina naje baka san ba"amin tambayar "yan yara ba?_

       Murmushi yayi mai aji, sannan ya rubuta mata!

_Allah ya baki haƙuri_

                              _Kaima Allah ya baka, ina dai faɗa maka abinda bana so ne a rayuwata, abota kawai sai kayi ta shiga wani hurami daban,_

_Kiyi haƙuri_

     
                _Idan na faɗa maka inda naje me zakayi ma?_

_Babu abinda zanyi sannan babu abinda zanji,_

_Ina so ne kawai naji dan inji idan kuma kuna irin al'adunmu ne!_

                      Gyara zama Rabi"atu tayi sannan ta ajiye wayar a gefenta taci gaba da kalancinta,

Saida ta gama abinda takeyi tsaf sannan ta koma ɗakinta, saida ta kunna waƙa sannan ta kwanta saman gado,

          Number da akayi ta kiranta da ita a daren jiya taci gaba da nema amma babu a kashe, nazari Rabi"atu ta fara waye ya ƙirata da wannan number ne?

          Haka ta gaji da gwadawa sannan ta haƙura,

A lokacin kuwa saƙon jishad ya taru sosai dan haka ta fara ƙoƙarin karantawa, dan itafa tsoro ma takeji kada ya shanye mata jini tunda yace shi ba'a nigeria yake ba, sannan kuma bata san da gaske yake ba ko kuwa me yake nufi tunda bata shiga zuciyarsa ba!

SANADIN SOCIAL MEDIAWhere stories live. Discover now