Page 7

911 63 0
                                    

⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊


💝 *SANADIN SOCIAL MEDIA* 💝

             *Written by*
*JAMILA MUSA* _{ meelat }_

*Follow me on*

*Wattpad @ meelatmusa*

*Instagram @ meelat_musa*

*Idan angulu ta biya buƙata zabuwa ta tafi da zanenta! dan komai wayan Amarya sai ansha manta, wasu kuwa ganin baƙin hadari yasa su wanka da kashi domin shidai karambani tsalle ɗaya kake ya jefaka rijiya amma sai kayi dubu baka fita ba, dan duk wanda Allah ya bawa haƙuri yafi a zageshi shegun gari an iso kare yaga kura, da alkairi kishiya ta hau kura, gudu da waiwaiye shi yake jawo mugun zato........*

         *Gaisuwata a gareku!*

*HASSAN ATK*
*YAYA HAYAT BABA ZUBAIRU* _{ Admin of Admins }_

*Sadaukarwa gareki* 👇🏻
*RABI"ATU AMINU MAMMAN DEE*

06/07/2018

7.

Kuka mai kama da ana fitar da aljannu a jikin bil'adama,......

Wani irin wulaƙantaccen kallo Rabi"atu ta sakeyi ma kokon, ɗan gajeran murmushi tayi tare da yin magana a bayyane cewa wai kamar ni nan za"a bawa tsari? Tsari fa? Abinci dadbobi ta ƙarasa maganar da kakkausar murya,

      Ɗan gajeran tsoki tayi tare dayin short da kofin koko cikin tsananin ɓacin rai, saida kofin kokon yayi sama sosai sannan ya dawo ƙasa feff, rumtse hannayenta tayi tare da ɗaga kanta sama ta cije bakinta sannan ta rumtse duka hannayenta jikinta har kyarma yake kamar an kada ɗan wasan dambe tace kayyyyyyyyyyyyy ta faɗa cikin ƙaraji tare da daka tsalle a saman kofin ya tar watse gaba ɗaya,

      Bana shan koko bana sha, ni za"a bawa koko sai kace Akuya? Shashshekar kuka tayi sannan taci gaba da cewa Akuyar ma wandda bata da "yan ci, kuka sosai sannan taci gaba da cewa shikenan nima na zama Akuya tunda har an fara bani abincin dabbobi wayyo Allahna............

Haka Rabi"atu ta ɗora hannayenta duka biyun a ka taci gaba da kuka a cikin daren nan babu ji babu gani,

      Shi kuwa Ahmad ɗakinsu ya nufa yayi kwanciyar sa hankalinsa kwance kamar ya hau jirgi mai ya ƙare,

      Da safe dukansu suna zaune dirning suna break momy ta fito, da shirinta na tafi aiki, dukansu gaisheta sukayi amma babu wanda tayi ma magana tayi gaban abunta,

   Abdul ne ya tashi da sauri yasha gabanta  lokacin har tana ƙoƙarin fita daga cikin farlon,

Kama kunnuwan sa yayi alamar neman yafiya sannan ya fara cewa,

      Kiyi haƙuri momy ki gafarce mu dukanmu baki ɗayanmu, ya ƙarasa maganar ya nuna inda sauran "yan uwansa suke zaune,

Kiyi mana afuwa fushinki barazana ne a rayuwarmu, ki yafe mana gaba ɗayanmu, nuna kansa yayi tare da ci gaba da cewa ni yau zan wuce insha Allah, ki manta fushin da kikeyi dani a zuciyarki,

       ***

Hajiya Fatima itace mahaifiyar su Rabu"atu kuma mata ɗaya a wurin mahaifin su wato Alhaji Sulaiman Muhammad,

       Aurene na zumunchi aka masu dan ƙara yaɗa zaman lafiya a cikin ahalinsu,

Wanda wannan abu ya zamar musu kamar ibada, dan yarinya tana fara tasowa za"ace an bawa ɗan gidan wane ita,

       Familynsu babban family ne daya tara manyan mutane wanda suka haɗa da "yan kasuwa da manyan ƙusoshi a cikin gwamnati dan kisan boko sunfi yawa a cikin familyn,

SANADIN SOCIAL MEDIADonde viven las historias. Descúbrelo ahora