Page 8

879 62 1
                                    

⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊


💝 *SANADIN SOCIAL MEDIA* 💝

             *Written by*
*JAMILA MUSA* _{ meelat }_

*Follow me on*

*Wattpad @ meelatmusa*

*Instagram @ meelat_musa*

*Idan lokaci ya iske man shanu ko an a zashi a wuta baya ƙamshi,* 😊

*Asma"u Zayyana, { Asmee } ina gaisuwa ta musamman a gareki, domin keɗin ta dabance a cikin babban birni zuciyata*

          *Asan mutum asan cinikin sa inya bari a san ya fasa*

*Sadaukarwa gareki* 👇🏻
*RABI"ATU AMINU MAMMAN DEE*

08/07/2018

8.

Da hypo zaka wanke ran naka koda klin? Abdul ya sake tambayar Ahmad, na dai faɗa maka, ka dai daina dukana dan haƙuri na gab yake da ƙarewa, Ahmad ya faɗa, ya mutu ma dan uban haƙuri, inji Abdul,

        A daidai lokacin daya sake kai masa duka a hanci, Ahmad bai gama jin zafi ba Abdul ya sake sokewa da hannunsa a saman bakinsa,

         Lafiyayyen duka ɗaya yai masa bakinsa ya fashe, da sauri Ahmad yakai hannun sa daidai inda yake jin zafi ya shafa,

     Jini ya gani a lokacin daya dawo da hannun nasa dan gani lemar daya taɓo a gefen bakin sa,

Kai kai kaiii, ni ka fasawa baki? Yayi tambayar ne cikin nuna tsananin ɓacin ransa, ganin Abdul baiyi magana ba yasa shi sake cewa, nace ni ka fasawa baki na?

     Dunƙule hannunsa yayi tare da kaiwa Abdul duka cewa nine ka fasawa baki,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,??????,,,, cikin fushi, dukan da Ahmad ya kaiwa Abdul yasa suka cakume faɗa babu ji babu gani, faɗa sukeyi kowa yana cakuwa kuma kowa yana dakuwa daidai irin dukan daya haɗeye,

       Amma idan Ahmad yakai nasa dukan yana tambaya wa Abdul nine ka daka harka fitar wa da jini? Fadeel yayi ya raba faɗa amma abu ya faskara, dan shi faɗan Ahmad baya rabuwa saidai idan bai fara ba,

Haka suka ɗauki lokaci mai tsawo suna caskaɗewa dan tun Abdul yana faɗa yanajin daɗin dukan da yakewa Ahmad har ya fara gajiya dan yaga Ahmad ɗin yaƙi yayi laushi dan gani yakeyi kamar anayi masa wahayin ƙarfi ne a duk bayan daƙiƙa ɗaya,

        Ganin abun nasu bamai ƙarewa bane fadeel ya fara kiran wayan momy, su kuwa sai canja wurin dambe sukeyi kamar "yan dambe,

          Momy lokacin data ga wayan fadeel ƙin ɗauka tayi, ya ƙirata babu adadi amma bata ɗauka ba, ganin taƙi ɗauka yasa shi tura mata saƙo cewa, ana faɗa Yaya Abdul da Yaya Ahmad,

_So kashe kansu_

Shine amsar da momy ta bawa fadeel, kuka fadeel ya farayi tare da nufa inda suke kaiwa juna duka, cikin kuka yace Yaya Abdul don Allah kai kayi haƙuri tunda kaine babba ya ƙarasa maganar yana mai kai hannunsa jikinsa dan ƙoƙarin rabasu,

         Cikin muryar wanda yasha dambe ya gaji yace barsa fadeel bara na koyawa yaron nan hankali, murmushi Ahmad yayi tare da cewa kai fadeel matsa a wurin nan kada in ɓata maka jiki da jini,

      Fadeel ganin Ahmad yayi magana yasa ya matsa kusa dashi yace don Allah yaya kayi haƙuri kaima don Allah ku daina, koni da Rabi"atu yanxun bama wannan abun saiku manya,

    Sai yanzun Ahmad ya tuna ma bai kai mata kalacin safe ba, dan haka ya yarfe Abdul daga jikinsa cewa zaka sake shigo harkata,

        Cikin shashshekar gajiya Abdul yace Allah dai ya rufa maka asiri an bani haƙuri wallahi yau da sai kayi jinya banza sakarai, Ahmad bai sake magana ba ya fice daga cikin farlon,

SANADIN SOCIAL MEDIADonde viven las historias. Descúbrelo ahora