Page 35

726 59 0
                                    

⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊


💝 *SANADIN SOCIAL MEDIA* 💝

             *Written by*
*JAMILA MUSA* _{ meelat }_

*Follow me on wattpad @ meelatmusa*

*_Assalamu Alaikum masoyana! Ina baku haƙuri naji na shiru jiya, kuyi haƙuri don Allah wasu "yan hidimomi ne suka riƙeni, ngode sosai ina muku fatan alkairi tare da addu"a Allah yasa muyi juma"a cikin farin ciki._*

*Sadaukarwa gareki* 👇🏻
*RABI"ATU AMINU MAMMAN DEE*

10/08/2018

35

      Wutsilniya ta farayi kamar kifi ya faɗi a ƙasa ana ƙoƙarin kama sa, tsayawa jishad yayi da tafiyar tare da kallonta yace wai miye kikeyin abu don Allah kamar wata ƙaramar yarinya?

Shiru tayi, sauketa yayi tare da cewa sauka tunda baki so ai kin huta! Yana faɗi haka ya juya ya koma baya, toilet ya shige ya watso ruwa, yana fitowa ciki ya koma rai a haɗe ya ɗauko kayan da zai saka ya koma palo ya saka bayan ya gama ya haye saman kujera yayi kwanciyarsa,

   Tunda Rabi"atu taga yanayin jishad yanda ya shigo hankalinta ya tashi, a hankali taja bargo ta lulluɓe addu"a ɗauke a bakinta, ita taga ta kanta shima jishad yanayin fushi,

    Wani irin wahalallen bacci ya ɗauketa, babu abinda kakeji sai ajiyar zuciya, dan ita dai zuwa india bai mata daɗi ba,

Jishad kuwa saida ya tabbatar bacci ya ɗauki Rabi"atu sannan ya koma ciki, kusa da ita ya kwanta kamar dai yanda ya saba tunda tazo, a hankali ya jawota jikinsa dan gudun kada ya tasheta,

      Jin lokaci lokaci tana fitar da ajiyar zuciya yasashi juyota yana kallonta da gaske bacci takeyi, tashin ta jishad yayi, da sauri ta buɗe idonta cikin damuwa, tashi ki cire wannan kayan ki saka kayan bacci,

Dakel ta haɗiya yawun bakinta tare da sauka a hankali daga saman gado, ta ɗauki kayanta zata fita, ""cikin faɗa jishad yace ina zakije ne wai? Cikin in ina tace palo zanje na saka,

    Da tsawa yace mata bansan shirmen banza ki saka kizo ki kwanta nace, komai palo komai toilet mtswww tare da juyawa yace Allah yasa ki fitan kiga yanda zan dakaki a wurin nan,

    A siƙwane ta koma ta saka kayan danshi jishad ya bata baya ba inda take yake kallo ba! A kunyace baiwar Allah taje ta hau saman gado a raɓe ta kwanta kamar wanda akayiwa iyaka da hawa gadon,

    Ba tare daya kalleta ba yace dawo nan kusa dani, jan jikinta tayi ta matsa kusa dashi saboda wata irin munafikar kunya takeji haka nan taji tanajin kunyar jishad a daren nan,

     Bayan ta kwanta kusa dashi yace tayi addu"a, addu"ar bacci tayi bayan ta shafe duka jikinta yace ta matso ta riƙeshi, kuka ta farayi tana ƙoƙarin buɗe baki dan tayi magana jishad ya watsa mata wata irin harara, wanda tasa ta riƙeshi da sauri ta cusa fuskarta a cikin ƙirjinsa ta fara bacci,

     Saida tayi bacci sannan shima yayi bacci tunda suka kwanta basu sake motsawa ba saida asuba!

    Saida yayi alwalla sannan ya tashi Rabi"atu, shi kuma masallaci ya wuce dan ya samu jam"i, bayan jishad ya tafi itama ta nufi toilet danyo alwallah,

     A gidansu jishad tun a daren jiya ake neman jishad babu shi babu labarinsa, resmin kuwa ta wasa wuƙaƙenta sosai idonta idon Rabi"atu saita aika ta lahira, amma duk tashin hankalin da resmin take ciki batakai Abbu ba domin dai yace jishad yana so yasa yaji kunya a idon iyayen resmin,

   Abbu yaji baƙin ciki harya rasa inda zai saka ranshi yaji sauƙi, kuma duk wayoyin jishad a kashe suke wannan abu shine ya ƙara ɗaga hankalin Abbu,

SANADIN SOCIAL MEDIAWhere stories live. Discover now