WACECE ITA?💦. Na ummu zayd 👌🏽
Dont forget to vote**Tsugune take ta rafka tagumi tareda kura ma kyakyawan danta idanu Wanda yake jariri shar da ta hayfeshy basu wuce awa 2 ba, tunani ta zurfafa a ciki tare da jerowa kanta tambayoyin dabata San amsarsu ba kuma bata tunanin akwae wani mahaluki daze iya bata amsar wannan tambaya tata rikitacciya wacce ita kanta bazata ce ga takamaiman amsarsuba" waye baban wannan yaron?" Tambayar da take nanatama kanta kenan da har yau Tarasa me iya amsamata su duk tunaninta takasa tuna komae gameda cikin yaron nan itakam taga ta waye garine da cikinsa da hayhuwarsa, turkashi, tashin hankaline fal cikin ranta wacce ta lula cikin tunanin dabatasan tashiga ba,firgigit ta dawo da ga tunanin datakeyi saboda jin kukan jaririnta da tayi wanda ayanzu take ganin batada kowa sama dashy, neman kuka takeyi amma takasa yinsa ashe kuka ma samun wuri ne gameyin sa,takara. kai dubanta ga kyakyawan danta dayake cigaba da canyara kukansa wanda ko wando bayida shy tafashe da kuka BAWAN ALLAH😢, sunan datasami kanta da kiransa kenan wanda atake zuciyar ta lakaba sunan dan, tunjiya take fama da nakuda ita daya ba mataymaki har Allah yasa tasauka lapiya, kuka cikin ta yabada da karfi kululu alamar yunwa nacinta tashy tayi har jikinta na rawa ga jiri tana gani dakyar ta goya danta da dankwalin jikinta tareda dauko hijab dinta wanda tsabar dauda ce tasaka daga fari yakoma brown gawani jirwaye tako ina kamar ruwan kurji tayafa ma kanta tafice dasauri daga cikin kangon, tafiya take wacce ita kanta bata san inda take jefa kafarta ba yayin da wadansu namata kallon mahaukaciya har ana matsawa abata waje, tanaji wasu nafadin ikon Allah! kunga mahaukaciyar can tahayhu ko wane mara imani ne yamata ciki haka Allahu aalam''eh mana dole kowanene yaganta baze iya banbantata da haukar ba, share hawaye tayi tarada cigaba da tafia,har Allah yakawota wani tangamemen gida tahau kwankwasawa kamar zata balla gidan, megadi yazo cikin sauri ya kalleta sama da kasa tareda dakamata tsawa" ke ance miki nan sakatiri(psychiatry) ne? Zaki zo kita bugu kamar gidan naku na masu hnkali? Ko kibace daga nan koyanzu inmiki dukan tsiya anan ehw!" dakyar take numfashy sbd tsavar galabaita datayi ga danyen jego ga yunwa wanda tun bawan Allah na kuka har yayi shiru yayi barcin wahala, dakyar ta iya buda baki tareda cewa "_dan Allah dan darajar manzon Allah. Baba kataymaka min da abinci ko kabarni nashiga naroki arzikin..... Tun kan takarasa maganar tata baba maigadi ya tsaedata yace nalura ke ba mahaukaciya bace daga jin maganganunki yarinya amma dan Allah kiyita kanki tun kamin kisa na rasa nima na abincin nawa dan inmasu gidan nnan suka tarda irinki abakin aikin gidan nan na tabbatar karshen aikina a gidan kenan, hka ta durkusa tana magiya baba megadi yamata korar kare tana kuka ta tashy cikin wani jin jiri tabar kofar gidan, tafara tafiya kenan taji ance ,_yannan! Dasauri tajuyo dantaga me kiran nata taga megadin nan da leda a hannu dasaurinta kuwa tajuyo har tanacin tuntube tazo ta tsuguna a gabansa tace " gani baba " ya kalleta yaji ta matukar basa tausayi ya miko mata leda tare da fadin" kada kisake zuwa kofar gidn nan yarinya ga sadakar abinci da sutura naga duk kinbata kayan naki da jini" batareda yatsaya sauraren abinda zatace ba yajuya da sauri yatafi, gefe tasamu a kofar wani gida me yalwar bishiyoyi ta bude ledar tahango ledar abincin da bava megadi yabata da sauri tabuda tafara kaiwa baka batare da laakari dakoda hannunta dayabaci cikn jini ba, tacinye tas tareda lashe ledar sannan tayi hamdala ta kara buda yar ledarta tahango gorar ruwa takafa kai tasha yakusa rabi sannan ta sauko bawan Allah dayake ta barcin wahala, tafara dan dura masa ragowar ruwan, kasancewa jinjiri cike yake da yunwa tuni yasoma karfe ruwan yasha sannan ta fito da nononta tasoma bashy, wata yar kara ta kwalla kasancewar azabar dataji har cikin kwakwalwarta abinka ga sabon hayhuwa, shiko yanata tsotsar nonon haka tadaure sbd wani irin son dataji tanama bawan Allah dinta.💦💦WACECE ITA?💦💦na ummu zaid👌🏽 *page 2* Anty jaleela ngd Allah bar kauna, u re indeed a very good friend... Love u loads😘
Zeenatu ce tana rakube adan kwangon data saba kwana, kuka take kamar ranta ze fita, saboda ciwon da bawan Allah yakwana biyu yanayi yaron ko kuka yakasa saboda yanacikin wani hali ga rana anata fesawa kasancewar garin na katsina akwae tsanani zafi, nonuwanta sun cika suna mata wani irin zugi saboda yaki shan nonon Sam, tarasa inda zata saka kanta taji dadi, kuka take cikin dashewar murya tana fadin" Bawan Allah mekake so ne? Kada katafi kabarni nidaya aduniyar nan Ya Rabbi ka cetomin rayuwar Dana kabani iko cin wannan jarabawa tawa, wani kara tasaka tareda da amboton ya illah tareda yin xumbur ta dauko danta tafita da shy ko gani sosae batayi sabod wani irin tashin hankali, ba abinda yafado mata a rae se zuwa wajen megadin nan kota samu k sutura a mawa danta, tun randa tafara zuwa yabata abinci tamaida wajen gurun zuwanta tun yana korarta har yakyaleta yana taymaka mata da dan abinci, tana zuwa Bakin gate din gidan ba kakautawa tafara bugawa kamar zatayi hauka, megadi yana bayi yaji wannan bugun gida gabansa yasoma faduwa kada fa yarinyar nan taja!I barin aikina, Allah Allah yake yafito yamata korar kare dan ta mugun bashy haushi yau dae.
Zaid ne yafito daga dakinsa cikin bacin rai yana mamakin halin mutane aransa ya raya wata kila irin masu neman taymakon nan ne matalauta wat d fuck! Waeshin inama megadin nan Dan Shifa yagaji da halin saleh megadi kwanan nan yafara lura d irin wannan bugun gida amma nayau yafi na kullum, mtsww yaja tsaki kasancewar bugun kara tsananta yayi, shifa a rayuwarsa yatsani talaka haka yataso cike d masifa fal ransa yaga Wanda take musu haukar nan yafito yanufi gate din kenan se ga baba megadi yasheko a guje zaid yafara masifa shidae baba salele hakuri kawae yake bashi yana bude kofar tazube a gurin tareda da rusa wani iri kuka, baba dan Allah kataymakeni wlh bawan Allah ne ya rasu bansan yazanyi ba!!" Baba megadi yamatso ya amsa yaron tareda kara kunnanshy a saitin zuciyar bawan Allah, zeenatu (sunanta kenan) aeba mutuwa yayi ba doguwar suma ce mikon butar can kigani dasauri ta tashy duk jikinta rawa yakeyi ta miko masa butar yadan shafa masa ruwa, zaid shiko yana tsaye shida yafito Dan yima matar masifa seya kasa kawae ya zubamata idanu cike da tsanani tausayawa, har ze juya seyaga kamar be kyauta ba yana likita su d sukai rantsuwa akan service to humanity, se yasami kansa dacewa" meke damunsa?" Baba salele ya dago d mamaki dan bezata zaid yanada imani haka ba kasancewar ansan sa da rashin m, beda imani ko digo ba abinda yafi tsana irin talaka, dasauri tacemasa " wlh bansani ba naga baya amsan nono kuma jikinsa zafi" mikoshy mugani yafada, baba salele dasauri yamika masa yaron, zaid yace wannan ae jaundice ke damunsa sedae ayi admitting dinku a asibiti, zeenatu tayi Saurin zaro ido tareda fadin " nashiga uku" wlh ko naira biyar banida shi" tadukar daka tareda wani sheshekar kuka, zaid dae yayi kasake cike d tausayi yace" salele bari nabaka kudin mota kanema mata napep Ku sameni asibitin, baba yace to itako tana ta godia, daga mata hannu yayi alamar tayi shiru nan da na ta tsuke bakinta tayi gum, yaciro dubu daya yaba megad gashy kanema mata abin hawa su biyoni a baya, aransa yanajin baze iya daukar talaka a motarsa va, baba yaje ya samo me napep yamas kwatance inda zasu yabiya yakalleta yace gashy zeenatu kirike canjin a hannunki Allah bashi lapiya tace ameen me napep yaja suka wuce har asibitin turai yar adua suna isa harabar asibitin suka iskesa a tsaye yana jiransu, kallo daya yamata ya dauke kai tareda fadin "kubiyoni abaya" takara saba bawan Allah a bayanta tabi bayansa har reception din asibitin yasami me rubuta kati yace " new patient CE pleas arubuta mata kati tasameni a office matar t amsa da toh yaciro kudin katin yabiya, yayi gaba itadae zeenatu na tsaye rungume da danta, matar tace ya sunan ki ? Tabata amsa d zeenatu, ta kuma tambayar ta kece ba lafia? Aa yarona ne beda lafia, ta tambayeta yasunan sa ta bata amsa da bawan Allah, matar tayi kuri tana kallonta wannan wane irin sunane Abdullah dae ko? Tace A'a sunansa kenan matar ta tave baki ta rattaba sunan batareda tadago ba takuma tambayarta sunan babansa fa,? Hankalin zeena yatashi tayi shiru, jin shorun yayi yawa ne yasa matar dago kanta tareda tambayarta baiwar Allah kinyi shuru kobaki ji menace bane, idon zeenatu yaciko da hawaye tace kibar sunan babanshy dan nima bansani ba, matar takalleta da kyau har zatay magana tayi shiru bata Kuma Cemata komae ba, abinnata bata mamaki taraya ma kanta tokodae shegene? Haka tagama cika komae tabata tareda nuna mata office din doctor,zaid din, kwankwasawa tay tareda sallama da yar dasashiyar muryarta Wanda kamar mecin magani haka zaid ya amsa tanemi kujera tazauna tazuba tagumi, ina file din naki? Yatambbay dasauri ta Miko masa har rawa jikinta yakeyi kawae yakalleta yakauda kai yadauki katin ya karanta Bawan Allah sunan daya gani kenan ajikin katin yadago yakara nazarinta nawasu sakanni kadan tareda tambayar ta sunan danki kenan? Tace eh, yace yasunan babansa, haka kawae tafasa kuka, cike da haushy yadaga mata hannu" kinga ya isa haka malama ba kuka nace kiminba nan ba gidan makoki bane! Nan da nan tay Tsit tareda fadin ni bansan waye babansa ba, har zeyi mgna ya tuna d yaron yana cikin wani hali yafara ruvutu tareda dago kai yace dole zaa kwantar daku tukuna mugani, tace to, sannan yasa aka turasu pediatric ward aka basu gado, nurses sukai musu komae akafara bama abdallah magani, itadae zeenat anhana ta Shiga wajen abdallah tunani ne fal a ranta tareda godewa Allah daya ceto mata rayuwar danta, tayi zurfi cikin tunani kenan taji wata nurse nafadin ina maman bawan Allah?" dasauri tace gani, nurse din tamiko mata wani dan kofi tace gashy kitatso nono zaa bashi dasauri tace to tareda amsar cup din nurse din tajuya haka taciro nonon tafara matsowa wani irin azaba taji har ciki kwakwalwarta kasanewar nonon yamata tsami yacika sosae haka nan takasa wata mata nagefe tana kallonta tace" daurewa zaki fa ki matso" runtse ido tayi tareda matsar nonon tana kwalla haka ta daure dan lafiyar danta yafi mata komae dakyar ta iya bari yakai rabin cup tabarshy, ta ajiye matar takuma cewa tashy zaki kimusu magana kibasu fa, ta amsa da toh tareda mikewa dakyar wata irin yunwa na cinta taje tamika masu, har zata juya wani jiri ya kwasheta tafadi wanda yayi dae2 da zuwan dr zaid dan yadubasu, yace subhanallah tareda kiran wata attendant danta taymaka mata, dataymakon attendant di ta tashy tareda fadin dan Allah kitaymakeni da abinci yunwa nakeji, shidae zaid tsaye kawae yayi yana kallon ikon Allah dasauri yace" laraba kimaidata daki kizo ki amsa a kudi kisiyo mata abinci da ruwa kibata, laraba tace ok sir sannan ta taymaka mata tamaidata dakin taje ta amso kudi ta siyo mata abinci takawo mata ana bata ko wanke hannu batayi ba tasoma kaiwa baki, sudae matan waje nata kallonta cike da tausayi haka taci ta sude matar dake kusa da gadonta tace maman bawan Allah kije ki wanka mana ga pcm kidansha ko kyaji saukin gajiyar, taceto dan Allah inane bayin? Matar tanuna mata tareda bata aron bucket dinta da savulu tayi godia tashiga wanka seda ta dirje jikinta ta wanke kanta wata irin dauda ke fitowa akalla sedatyi amfani da bokiti hudu wajen yin wanka wanda ita kanta taji dadi danta ne yafado mata arae Allah sarki bawan Allah yron da kwana 5 da hayhuwarsa amma saudaya yataba wanka shima dazaa masa dayaji dadi, saurin kauda tunanin tayi tawanke pant din ta dadan kunzugun datayi na tsumma da dankwalinta tawanke ta tasaka sabulu tawanke hkoranta rtas nan da nan taji dadi dadi sosae sannan tafito daga wanka, tana shiga dakin n matan suka fara kallonta dan se tayi kamar ba ita ba tayi fes da ita wannan dae matar takuma magana maman bawa Allah ga mai kidan shafa naga ko kayan sakewa bakida shi ga wannan" har kasa ta tsuguna tayita ma matar godia, matar tace bakomae ae musulmi dan uwan musilmine, haka ta zauna ta gyara jikinta nan da nan ko tayi kyau abinta, matar tacemata n sunana lubabatu kefa? Tabata amsa da zeenatu cikin lokaci kadan suka saba d lubabatu, nurse ce ta kara lekowa ina maman bawa Allah? Tace gani nurse din tace kibada pampas za saka masa da riga da wvda ita tadauko kayan babynta tabada asaka ma bawan Allah zeenatu rasa bakin magana tayi tana mamakin wannan kirki irin nalubabatu godia tasomayi harda hawaye lubabatu tace ba komae maman bawan Allah haka rayuwa tacigaba ita dae tasan kullum zaa kawo mata avinci ace inji doc zaid amma haryau bata kuma ganinsa bama balantana tamasa godia, shakuwar dasukay da lubabatu kuwa kyace yar uwatace, kwanan su 5 a asibiti zeenatu tayi kamar ba ita ba tayi shar da ita ga taymako datake samu daga matan dakinsu, itadae ba abinda zatace se godia, haka rayuwa taciga seda suka kwana goma sannan aka sallame su lubabatu ranan kuwa zeenatu ansha kuka haka suka rabu kowa na kuka lubabatu tace" zeenatu gashi zamu rabu bammusan ko address din juna ba kimin kwatancen gidank insha Allah kuwa zaki ganni, zeenatutayi shiru dan batasan mezatace ma lubbabatu va, data lura setace nikuwa nalyra dake zeenatu akwae abinda kedamnki amma ga address dina duk randa aka sallameku kizo gidana myi magana, zeenatu tace to tareda ansar takardar da luvy ta bata, sukai bankwana tanemi leda ta ajiye address din gidan.

YOU ARE READING
WACECE ITA??
Espiritualta wayi gari ne da hayhuwar yaron daba tasan wanene ubanshi ba, kwatakwata kwatakwata bata iya tuna ryuwar da tayi abaya, tirkashi littafin wacece ita littafine daya kunshi soyayya, rudani, tashin hankali dakuma tausayi, kubiyoni dan jin wannan kaya...